Har Yanzun Ana Zaman Dar-Dar A Burkina Faso Bayan Kokarin Juyin Mulkin Da Bai SamiNasara Ba
Published: 29th, April 2025 GMT
Ana ci ga ba da zaman dar-dar a kasar Burkina faso, bayan da shugaban kasa mai ci Ibrahim traure ya sake tsallaka rijiya da baya, a wani kokarin juyin mulki wanda bai sami nasara ba a makon da ya gabata.
Shafin yanar gizo na labarai ‘Africa News’ya nakalto radiyo Faransa RFI yana fadar cewa an bankado juyin mulkin ne bayan da dukkan bakin da aka gayyata a ranar 22 ga watan Afrilu zuwa wani taro sun kasa halattan taron.
Labarin ya kara da cewa a cikin yan kwanaki masu zuwa mutanen kasar zasu fito zanga-zanga don nuna goyon bayansu ga shugaban Traore.
Har’ila yau ana gudanar da bincike a cikin barikokin sojojin kasar a birnin Wagadugu a kokarin gano wadanda suke adawa da gwamnatin Traore, sannan suke aiki wa kasashen yamma musamman kasar Faransa wajen ganin bayan shugaba Ibrahim Traore.
Kafin haka dai an nakalto ministan tsaron kasar ta Burkina faso Muhammada Sana ya na wani bayani a tashar talabijin na kasar, kan cewa kafin su gano shirin juyin mulki sun satar maganar wayar tarho tsakanin wani babban sojan kasar da shugaban wata kungiyar ta’addaci wanda aka shirya za su kashe shugaba Traore.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rundinar IRGC, ta sanar da shahadar babban kwamandanta Manjo Janar Hossein Salami a harin ta’addancin Isra’ila
Dakarun kare juyin juya halin Musulunci na Iran sun sanar a cikin wani sako mai cike da alhini da shahadar Manjo Janar Hossein Salami, babban kwamandan dakarun IRGC wanda ya yi shahada da asubahin ranar Juma’ar nan yayin wani hari na ta’addanci” da gwamnatin sahyoniyawan ta kai kan hedkwatar rundunar.
Hukumar soji tana jinjinawa wannan babban kwamandan da aka gabatar a matsayin babban jigo wajen kare manufofin juyin juya halin Musulunci na Iran, tare da yin alkawarin mayar da martani mai tsauri ga makiya.
Ga yadda sanarwar IRGC ta kasance :
Da sunan Allah, Mai rahama, Mai jin kai
A cikin bakin ciki da radadi muna sanar da shahadar Manjo Janar Hossein Salami, babban kwamandan dakarun kare juyin juya halin Musulunci, da da wasu mukarabansa, a lokacin harin ta’addancin da gwamnatin sahayoniya ta kai a safiyar wannan ranar ta Juma’a akan hedkwatar IRGC yayin da suke gudanar da muhimmin aiki na tsaron kasa.
Muna mika ta’aziyyarmu ga Jagoran juyin juya halin Musulunci kuma babban kwamandan sojojin kasar, Imam Khamenei, da iyalan duk wadanda abun ya shafa.
Duk da wannan harin na dabbanci, muna tabbatar wa al’ummar Iran masu daraja cewa, har yanzu rundunar sojojin Iran a shirye suke don maida martani ga gwamnatin sahyoniyawan.
Nan ba da jimawa ba za a isar da cikakken bayani kan halin da ake ciki biyo bayan harin na makiya da kuma matakin da za a dauka na hukunta su.
Haka zalika kafofin yada labarai na Iran sun rawaito shahadar babban hafsan hafsoshin sojojin kasar Iran Manjo Janar Mohammad Hossein Baqeri.
Shi ma Manjo Janar Baqeri ya yi shahada a wani harin ta’addanci da gwamnatin sahyoniya ta kai birnin Tehran a safiyar yau Juma’a.