An gano tsohuwar da ake nema a cikin maciji
Published: 26th, April 2025 GMT
Iyalan wata dattijuwa da suka nema suka rasa sun shiga fargaba bayan gano gawarta a cikin wani maciji.
Lamarin na zuwa ne bayan kumburin ciki ya bayyana sosai a kasurgumin maciji — kafin dangin tsohuwar su gano cewa maciji ya haɗiye kakarsu a cikinsa.
Sojoji sun kashe ’yan ta’dda 1,770 sun kama 3,070 a Arewa —Janar Musa Magidanci ya kashe kansa saboda mutuwar matarsa a NejaIyalan matar da ta ɓace sun bi sawun macijin zuwa wani mai yawan ciyayi a kudancin Sulawesi na kasar Indonesia.
’Yan yankin sun tsorata matuka lokacin da suka ga maciji mai tsawon kafa 26 ya yi nauyi da wani babban kumburi a cikinsa.
A lokacin da suka farka cikin macijin, sun gano gawar matar mai suna Hasia mai shekara 66, wadda ta bata a lokacin da take komawa gida daga wurin aikinta a wata gonar roba.
Ana kyautata zaton macijin ya fito ne daga dogayen ciyayin ya sari kafarta, wanda hakan ya sa ta faɗi.
Ɗan matar mai suna Nurdin, ya ce danginsa da ke cikin damuwa, sun kaddamar da bincike lokacin da dare ya yi, bayan da suka lura tsohuwar ba ta dawo gida ba.
Sun yi cigiya kafin su far wa macijin da misalin ƙarfe 9 na dare.
Sai suka sari macijin, suka buɗe cikinsa, inda suka tarar da gawar Hasia a cikinsa.
Nurdin ya razana, inda ya ce: ‘Wannan abu ne mai ban tsoro.
“Na san mutuwa ce mai raɗaɗi ga mahaifiyata, kodayake macijin ya mutu.
“Ba zai taɓa dawo da ita ba. Yanzu muna addu’ar Allah Ya jikan ta da rahama.
Ipda Zakaria, Shugaban ‘yan sandan PituRiase, ya ce: ‘Yanzu haka, ana shirin yi wa matar jana’iza.’
“Saboda haka, muna kira ga mazauna yankin da su yi taka-tsan-tsan wajen tafiya, domin an san cewa akwai manyan macizai a dajin.”
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — Dalung
Tsohon Ministan Matasa da Wasanni, Solomon Dalung, ya ce shekara biyu da Bola Ahmed Tinubu ya yi a matsayin shugaban ƙasa sun fi kowane lokaci muni tun bayan dawowar mulkin dimokuraɗiyya a ƙasar.
Yayin da yake magana da BBC a ranar Dimokuraɗiyya da Najeriya ke cika shekaru 26 tana mulkin farar hula, Dalung ya ce ba wani abin arziƙi da talaka ya amfana da shi daga wannan gwamnati.
An kama ’yar Najeriya da laifin safarar ɗalibai 15 a Australia Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — FayemiYa ce: “Kawai abin da talaka ya samu daga gwamnatin Tinubu shi ne tsadar rayuwa, yunwa, wahala da matsalar tsaro.”
Ya zargi gwamnatin da cewa cire tallafin man fetur ba tare da shiri ba, kuma hakan ya jefa mutane cikin ƙuncin rayuwa.
“Talakawa na mutuwa saboda yunwa, amma idan an tambayi Shugaba Tinubu, sai ya ce bai yi nadamar cire tallafin ba,” in ji Dalung.
Gwamnatin Tinubu dai ta ce ta cire tallafin ne domin hana wasu tsiraru ci gaba da cin gajiyarsa da kuma bunƙasa tattalin arziƙin ƙasa.
Amma Dalung ya ce gwamnatin ba ta talaka ta ke ba: “Idan ba canza motoci da jirage da gina sabon gida ga mataimaki ba, to babu wani abu da talaka ya gani.”
Dalung ya ce dimokuraɗiyya na cikin mawuyacin hali tun zuwan Tinubu, ya zargi gwamnati da kama waɗanda ke sukar ta da kuma sayen abokan hamayya wajen komawa APC.
“Mun ga yadda ake kama ‘yan gwagwarmaya saboda kawai sun faɗi ra’ayinsu. Kuma wasu na komawa jam’iyyar APC bayan an saye su,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa gwamnati na barazana ga ci gaban ƙasa idan ba a gyara lamarin ba.
Dalung, ya ce duk da rahoton Bankin Duniya da ke cewa tattalin arziƙin Najeriya na bunƙasa, bai yarda ba.
“Ta yaya za ku ce tattalin arziƙin da ke cikin matsin lamba yanzu yana bunƙasa? Wannan fa ba gaskiya ba ce.”