Aminiya:
2025-04-30@19:50:56 GMT

Magidanci ya kashe kansa saboda mutuwar matarsa a Neja 

Published: 26th, April 2025 GMT

Wani matashi mai shekaru 30 ya kashe kansa bisa rahotanni bayan rasuwar ƙaramar matarsa a ƙauyen Ikumi da ke Ƙaramar Hukumar Gurara a Jihar Neja.

Majiyoyi sun bayyana cewa magidancin mai mata biyu ya sha fama da matsalolin tunani da na zuciya tun bayan rasuwar matarsa ta biyu a watan Maris na wannan shekara.

Sun ƙara cewa ya kasance yana yawan bayyana cewa ba zai iya samun kwanciyar hankali ba tare da marigayiyar ba.

Shaidu sun bayyana cewa ya yi amfani da bindigarsa ta toka wacce yake farauta da ita wajen harbe kansa har lahira a gonarsa.

Wata majiya ta ce ya bar matarshi ta farko da manya da kuma yara biyu. Kakakin ’yan sanda a Jihar Nijar, SP Wasiu Abiodun, ya ce lamarin ya faru ne a ranar Alhamis 24 ga Afrilu, 2025.

’Yan kasuwar da suka ɓoye kayan abinci na tafka asara Na shiga fim ne don isar da saƙon Musulunci — Malam Inuwa Ilyasu ’Yar Arewa da ta kafa tarihin samun Digiri Mai Daraja ta ɗaya a fannin Shari’a

A cewarsa, “A ranar 24 ga Afrilu, 2025 da misalin ƙarfe 8 na dare, an samu rahoto cewa wani Stephen Moses mai shekaru 30 daga ƙauyen Ikumi ta yankin Shako na ƙaramar hukumar Gawu-Babangida, ya harbe kansa a kirji da bindiga a gonarsa da rana.

“Jami’an ’yan sanda na Gawu-Babangida sun ziyarci wurin da abin ya faru, sun samu bindiga da kuma gawar a ƙasa, an kai gawar asibiti yayin da bincike na farko ya nuna cewa mamacin yana cikin zaman makokin rasuwar matarsa wacce ta rasu kwanan nan, kuma ya kasance yana barazanar kashe kansa, amma ’yan uwansa ba su sanar da ’yan sanda ba don ɗaukar matakan kariya.”

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Amarya harbi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026

Gwamnatin tarayya ta umarci hukumar shirya jarrabawar WAEC da NECO da su fara amfani da cikakken tsarin amfani da Komfuta (CBT) ga dukkan jarabawar su nan da shekarar 2026. Ministan Ilimi, Dr. Tunji Alausa, ne ya bayar da wannan umarnin a ranar Litinin yayin ziyara da kuma duba yadda ake gudanar da gwaje-gwaje na CBT a cibiyoyin Bwari da kuma duba ɗakin gwajin jarrabawa JAMB a kwamfuta.

Alausa ya bayyana cewa, daga watan Mayu ko Yuni na 2026, duka ɓangarorin tambayoyin da aka saba na WAEC da NECO, na rubutu da na gwaje-gwaje, za su kasance a komfuta gaba ɗaya. Ya ƙara da cewa wannan matakin na daga cikin manufar gwamnatin na magance matsalar satar jarabawa.

Gwamnatin Kano Ta Biyawa Ɗalibai 119,903 Kudin Jarrabawar NECO Da NBAIS WAEC Ta Kwace Lasisin Makarantu 574 Sakamakon Satar Amsa

Ministan ya kuma sanar da cewa an kafa kwamitin bincike ƙarƙashin jagorancin Daraktan JAMB, Prof. Ishaq Oloyede, wanda zai duba tsarin jarabawar Nijeriya gaba ɗaya, inda aka ce sakamakon binciken zai fito nan da ƙarshen watan gobe. Alausa ya yaba da ingancin gudanar da jarabawar UTME ta 2025 da JAMB, wanda ya bayyana a matsayin “matsayi na duniya” kuma yana cika ƙa’idojin ƙasa da ƙasa.

A cikin jawabinsa, Oloyede ya bayyana cewa UTME ta 2025 tana ɗaya daga cikin mafi kyawun jarabawar da aka taɓa gudanarwa, inda ya kuma bayyana cewa duk wani zargin rashin dacewar cibiyoyin jarabawa yana buƙatar hujja mai ƙarfi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ɗaure ’yar shekara 80 a kurkuku saboda dukan jikarta da silifas
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
  • Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
  • Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji kuskure ne — Janar Chibuisi
  • Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114
  • Ƴansanda Sun Damke Ango Da Abokansa Bayan Mutuwar Amarya A Jigawa