Aminiya:
2025-11-28@19:18:28 GMT

Yadda matsalar ƙwacen waya da faɗan daba ke addabar Kano

Published: 27th, April 2025 GMT

Matsalar faɗace-faɗacen daba da kuma ƙwacen waya na ci gaba da ci wa al’umma Jihar Kano tuwo a ƙwarya, domin kuwa babu ranar da za ta zo ta wuce ba tare da an samu rahoton faɗan daba ba ko na ƙwacen waya a sassan jihar ba, abin da ke sanya fargaba a zukatan al’umma.

Munin lamarin ya kai matakin da akwai wuraren da mutane ba sa iya zuwa da daddare saboda tsoron mummunan abin da ke iya samun su.

An kashe sojoji 12 a barikin Nijar An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba

Wasu na ganin yadda ake gudanar da siyasar jihar da kuma yadda rashin aikin yi su ne ummulahaba’isin wannan matsalar musammam a tsakanin matasa.

Wani ma’aikacin kiwon a lafiya a sashen bayar da agajin gaggawa a daya cikin asibitiocin jihar ya ce, kusan kullum sai an kawo wadanda suka sami raunuka, sakamakon fadan daba ko a hannun masu kwacen waya.

Ya ce “Wannan ce shekarata ta biyu a wannan bangaren kuma magana ta gaskiya kullum sai an kawo masu rauni a wannan bangaren domin a kula da su.

“Na fi shekarau 19 ina wannan aiki, amma ban taba ganin abin tashin hankalin irin wannan ba, kuma idan ba a dauki mataki cikin gaggawa ba, to tabbas akwai babbar barazana ga zaman lafiya.”

Yadda suke ta’asar

Matasan da ke aikata wannan ta’asa suna amfani da fadan daba su afka wa mutane su kwace musu wayoyin hannu da kuma kudade.

Haka ne ma ya sa mutane da yawa ba sa iya fito da wayoyinsu domin amsa kira a wasu wuraren.

Wasu kuma sun kaurace wa wuraren da ayyukan bata-gari ya yi kamari.

Wani magindanci mai suna Aminu Baffa, ya ce an kwace masa wayar da bai fi sati da saya ba.

Ya ce abun ya faru ne a Kofar Mata da misalin karfe 10 na dare inda bayan ya kira mahaifiyarsa a waya, wasu matasa uku dauke da muggan makamai suka nufo shi, suka ce, ‘Gama wayar ka ba mu.’

Ya bayyana cewa mahaifiyar tasa “ta ji maganarsu, don haka ta ce kada ka ja da su, ka mika musu wayar baki alaikum.”

Daga baya wani a cikinsu ya jefa masa layin wayarsa.

Shi ko wani saurayi mazaunin unguwar Shagari Kuarters, yankan da aka yi a goshinsa yayin masu kwacen wayar suka same shi a kofar gidansu da misalin karfe 9 da dare, suka kuma kwace masa waya. Sai da aka yi masa dinki a raunin da suka ji masa.

To sai dai wani mazaunin unguwar Dorayi mai suna Awwalu Maiwada ya ce ana samun saukin ayyukan bata-gari da masu kwacen waya, saboda irin sabbin matakan da gwamnati take dauka domin tabbatar da tsaro.

A yi wa tufkar hanci tun da wuri

A farkon watan Afrilu da muke ciki ne aka tsinci gawar wata matar aure ’yar shekara 23, Ruma Shu’aibu, a kwance cikin jini, a unguwar Farawa cikin Karamar Hukumar Kumbotso, lamarin da ya sa mazauna unguwar cikin dimuwa saboda sun san matar mai son maman lafiya ce.

Mijinta, Ibrahim Muhammad, wanda ya ce ya bar ta a gida, ya bayyana cewa hankalinsa ya tashi lokacin da ya kira wayarta ba ta dauka ba, don haka ya nemi makwabcinsa ya duba amma shi ma ba wanda ya amsa liransa, ko da mijin ya dawo gida, sai ya tarar da ita a kwance cikin jini kuma an dauke wayarta.

Haka nan, an guntule wa wani malamim makaranta, Aminu Umar, yatsa, yayin karbar wayarsa a kan titin zuwa Jami’ar Bayero ta Kano, abin da ke alamta irin kalubalen da ke gaban gwamnoni.

Mutane na nuna damuwa bisa yadda dadan daba a unguwaani irin su Yakasai da Sabuwar Kofa da Kofar Mata da Dorayi da Sharada da Kofar Na’isa, kan kai ga zubar da jini ko ma rasa rayuka a tsakanin matasa.

Da yawa kuma ana wucewa da su zuwa asibiti domin samun kulawa da lafiyarsu.

Dalilin ƙaruwar faɗan daba da satar waya a Kano

Wani tsohon jami’in dan sanda, Sami Mohammed, ya ce, “Abin da ke kawo hakan bai da wahalar.

“Matsin tattalin arziki da talauci da kuma tashin farashi sun jefa matasa cikin kunci, shi ya sa suke daukar kwace waya da harkar daba domin kaiwa tudun mun tsira.

“Abu ne a fili, mutane kusan kashi 70% ba sa yarda su fito da wayarsu bainar jama’a su buga, saboda tsoron masu kwacen waya,” in ji shi.

Ya kara da cewa “abin da yake sa lamarin ke ci gaba shi ne kasuwannin da ake sayar da wayoyin hannu na sata na ci, ta yadda barayin sun san inda za su sami mai sayen wayar cikin ’yan awanni.”

Matakan da Gwamnatin Kano ta ɗauka

A shekarar 2023, Gwamnatin Kano da rundunar ’yan sandan jihar sun dauki aniyar kawo karshen wannan matsalar, inda gwamnatin ta yafe wa wasu batagarin matasa 222 da suka tuba kuma aka dauki 50 daga cikinsu a matsayin ’yan sandan sarauniya (special constabulary).

Kazalika gwamnatin ta kafa kwamitin tsaro na musamman karkashin Kwamishina, Dokta Yusuf Kofar Mata, domin kawo karshen matsalar.

Kazalika, Mataimakiya ta Musamman ga Gwamna kan Tsaron Al’umma, Ambasada Dakta Maimuna Umar Sharif, ta ce suna wayar da kan jama’a kan harkokin tsaro tare da sama wa ’yan sanda motocin aiki, da kuma samar da fitilu masu amfani da hasken rana a kan tituna a birni a karkara.

Ta ce nan ba da daɗewa ba za a ƙaddamar da gidauniyar tsaro kamar yadda Jihar Legas ta yi domin samar da issassun kudaden gudanar da ayyukan tsaro.

Kazalika kwamishina ’yan sanda na jihar, Ibrahim Adamu Dikko, ya shirya taro da dukkan masu unguwanni da turawan ’yan sanda daban-daban domin cimma matsaya kan yadda za a fuskaci matsalar, kuma mataimakin gwanar jihar, Aminu Abdulsalam Gwarzo, ma ya samu hallartar zaman.

Yadda za magance dabanci da ƙwacen waya a Kano

Wani masanin harkokin tsaro, Awwalu Durumin Iya, ya zayyana hanyoyin da za a kawo karshen matsalar.

Da farko, in ji masanin, “Tilas gwamnati ta samar da hanyoyin ayyukan yi ga dimbin matasa masu zaman kashe wando a sassa da lunguna.”

A cewarsa, “samun aikin yi dai dauke hankalinsu daga yawan fadace-fadacen daba da satar waya ko kwace.”

Durumin Iya ya ba da misali da garin Kura wanda mafi yawan mazauna yankin ’yan tauri ne, amma ba a fiye samun matsalolin tsaro da fadace-fadacen daba ba, saboda mafi yawa suna aikin gona da kuma noman shinkafa.”

Masanin ya kara da cewa, “Tilas a kawo karshen jagaliyar siyasa,” wadda yake ganin ita ce matsalar da ke kara taimaka wa matasan suke yin rawar gaban hantsi a zamantakewa da kuma sha’anin siyasa.

Ya yaba wa hukumar ’yan sanda saboda aiki tare da sarakunan gargajiya wajen tattara bayanai da kuma jan kunne ga masu aikata wadancan miyagun ayyuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faɗan Daba Jihar Kano masu kwacen waya kawo karshen ƙwacen waya

এছাড়াও পড়ুন:

Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon  Dake Takawa Makiya Birki

Kwamandan rundunar soja ta “Sayyidush-shuhada” dake Tehran Janar Qurbani Muhammad Wali Zadeh ya bayyana cewa; makamai masu linzami da Iran take da su ne, da kuma jiragen sama marasa matuki suke takawa makiya birki.”

Janar Qurbani Muhammad Wali Zadeh ya kuma ce; Albarkacin sadaukar da jinanai da shahidai su ka yi ne da kuma kwazon kwararrun masana, su ka sa Iran samun wannan karfin da take da shi.

Wali Zadeh wanda ya halarci taron girmama rundunar sa-kai ta Basiji da kudancin birnin Tehran, ya kara da cewa, Iran ta samu matsayin da take da shi ne a wannan lokacin daga jihadin shahidai da tsayin dakar al’ummar Iran, sannan kuma ya kara da cewa; A halin yanzu karfin Iran a fagen makamai masu linzami ya kai kolin da makiya suka kwana da sanin cewa duk wata barazana ta kawo wa jamhuriyar musulunci hari, zai fuskanci martani mai tsanani.

Haka nan kuma ya ce; Al’ummar Iran ba ta taba zama mai tsokana da fara kai hari ba a cikin kowane fada, amma kuma ba ta ja da baya a gaban barazanar makiya.

Janar din sojan na Iran ya yi Ishara da martanin da Iran din ta mayar bayan shahadar Janar Shahid Kassim Sulaimani da ya tabbatar da karfinta na  kare kai. Wannan karfin ne yake hana abokan gaba tarbar aradu da ka, su kawo wa Iran din hari.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Najeriya: Allah Ya Yi Wa Babban Malamin Addini Shehu Dahiru Bauchi Rasuwa November 27, 2025 An Zabi JMI A Cikin Majalisar Zartarwan Ta Hukumar Yaki Da Makaman Guba Ta Duniya CWC November 27, 2025 HKI Tana Amfani Da Tsagaita Wuta A Gaza Don Sake Shata Kan Iyakokin Yankin November 27, 2025 Yawan Falasdinawa Da Suka Yi Shahada Na Karuwa Saboka Keta Yarjeniyar Tsagaita Wuta November 27, 2025 An Rutsa Da Tsohon shugaban Kasar Najeriya A Guine Bissau Bayan Juyin Mulki November 27, 2025 Iraki: An Dakatar Da Tura Iskar Gas Zuwa Injunan Bada Wutan Lantarki A Yankin Kurdistan November 27, 2025 Ma’aikatar Harkokin Wajen Falasdinu Ta Sanar Cewa Akalla Yan Mata 33000 Ne Isra’ila Ta Kashe A Gaza November 26, 2025 Mataimakin Shugaban Nijeriya Ya Dawo Gida Bayan Kammala Taron G20 A Afrika Ta Kudu. November 26, 2025 Aljeriya Tayi Kira Da A Dakatar Da Israila Game Da Hare-haren Da Take Kaiwa November 26, 2025 Sojoji Sun Sanar Da Kwace Mulki A Kasar  Guinea Bissau November 26, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamnatin Kano ta nemi a binciki Ganduje kan zargin kalaman ta da hankali
  • Yadda mutane suka yi cikar ƙwari don halartar jana’izar Sheikh Dahiru Bauchi
  • Gwamnati Za Ta Biya Wasu Kudaden Ariyas Ga Masu Fensho Wannan Wata
  • Makaman Iran Masu Linzami Ne Kandagarkon  Dake Takawa Makiya Birki
  • NAJERIYA A YAU: Amafani Da Karfin Soji Ko Tattaunawa Ne Zai Kawo Matsalar Tsaro A Najeriya?
  • Tinubu ya ayyana dokar ta-ɓaci kan matsalar tsaro
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi 34 a Kaduna
  • ’Yan sanda sun kama masu laifi da 34 a Kaduna
  • Tukur Mamu ya karbi N50m daga kuɗin fansar harin jirgin kasan Kaduna – DSS
  • Kano Pillars ta kawo ƙarshen wasanni 8 ba tare da nasara ba