Aminiya:
2025-12-15@04:17:20 GMT

Yadda matsalar ƙwacen waya da faɗan daba ke addabar Kano

Published: 27th, April 2025 GMT

Matsalar faɗace-faɗacen daba da kuma ƙwacen waya na ci gaba da ci wa al’umma Jihar Kano tuwo a ƙwarya, domin kuwa babu ranar da za ta zo ta wuce ba tare da an samu rahoton faɗan daba ba ko na ƙwacen waya a sassan jihar ba, abin da ke sanya fargaba a zukatan al’umma.

Munin lamarin ya kai matakin da akwai wuraren da mutane ba sa iya zuwa da daddare saboda tsoron mummunan abin da ke iya samun su.

An kashe sojoji 12 a barikin Nijar An kama mutum 9 kan zargin satar mutane a Taraba

Wasu na ganin yadda ake gudanar da siyasar jihar da kuma yadda rashin aikin yi su ne ummulahaba’isin wannan matsalar musammam a tsakanin matasa.

Wani ma’aikacin kiwon a lafiya a sashen bayar da agajin gaggawa a daya cikin asibitiocin jihar ya ce, kusan kullum sai an kawo wadanda suka sami raunuka, sakamakon fadan daba ko a hannun masu kwacen waya.

Ya ce “Wannan ce shekarata ta biyu a wannan bangaren kuma magana ta gaskiya kullum sai an kawo masu rauni a wannan bangaren domin a kula da su.

“Na fi shekarau 19 ina wannan aiki, amma ban taba ganin abin tashin hankalin irin wannan ba, kuma idan ba a dauki mataki cikin gaggawa ba, to tabbas akwai babbar barazana ga zaman lafiya.”

Yadda suke ta’asar

Matasan da ke aikata wannan ta’asa suna amfani da fadan daba su afka wa mutane su kwace musu wayoyin hannu da kuma kudade.

Haka ne ma ya sa mutane da yawa ba sa iya fito da wayoyinsu domin amsa kira a wasu wuraren.

Wasu kuma sun kaurace wa wuraren da ayyukan bata-gari ya yi kamari.

Wani magindanci mai suna Aminu Baffa, ya ce an kwace masa wayar da bai fi sati da saya ba.

Ya ce abun ya faru ne a Kofar Mata da misalin karfe 10 na dare inda bayan ya kira mahaifiyarsa a waya, wasu matasa uku dauke da muggan makamai suka nufo shi, suka ce, ‘Gama wayar ka ba mu.’

Ya bayyana cewa mahaifiyar tasa “ta ji maganarsu, don haka ta ce kada ka ja da su, ka mika musu wayar baki alaikum.”

Daga baya wani a cikinsu ya jefa masa layin wayarsa.

Shi ko wani saurayi mazaunin unguwar Shagari Kuarters, yankan da aka yi a goshinsa yayin masu kwacen wayar suka same shi a kofar gidansu da misalin karfe 9 da dare, suka kuma kwace masa waya. Sai da aka yi masa dinki a raunin da suka ji masa.

To sai dai wani mazaunin unguwar Dorayi mai suna Awwalu Maiwada ya ce ana samun saukin ayyukan bata-gari da masu kwacen waya, saboda irin sabbin matakan da gwamnati take dauka domin tabbatar da tsaro.

A yi wa tufkar hanci tun da wuri

A farkon watan Afrilu da muke ciki ne aka tsinci gawar wata matar aure ’yar shekara 23, Ruma Shu’aibu, a kwance cikin jini, a unguwar Farawa cikin Karamar Hukumar Kumbotso, lamarin da ya sa mazauna unguwar cikin dimuwa saboda sun san matar mai son maman lafiya ce.

Mijinta, Ibrahim Muhammad, wanda ya ce ya bar ta a gida, ya bayyana cewa hankalinsa ya tashi lokacin da ya kira wayarta ba ta dauka ba, don haka ya nemi makwabcinsa ya duba amma shi ma ba wanda ya amsa liransa, ko da mijin ya dawo gida, sai ya tarar da ita a kwance cikin jini kuma an dauke wayarta.

Haka nan, an guntule wa wani malamim makaranta, Aminu Umar, yatsa, yayin karbar wayarsa a kan titin zuwa Jami’ar Bayero ta Kano, abin da ke alamta irin kalubalen da ke gaban gwamnoni.

Mutane na nuna damuwa bisa yadda dadan daba a unguwaani irin su Yakasai da Sabuwar Kofa da Kofar Mata da Dorayi da Sharada da Kofar Na’isa, kan kai ga zubar da jini ko ma rasa rayuka a tsakanin matasa.

Da yawa kuma ana wucewa da su zuwa asibiti domin samun kulawa da lafiyarsu.

Dalilin ƙaruwar faɗan daba da satar waya a Kano

Wani tsohon jami’in dan sanda, Sami Mohammed, ya ce, “Abin da ke kawo hakan bai da wahalar.

“Matsin tattalin arziki da talauci da kuma tashin farashi sun jefa matasa cikin kunci, shi ya sa suke daukar kwace waya da harkar daba domin kaiwa tudun mun tsira.

“Abu ne a fili, mutane kusan kashi 70% ba sa yarda su fito da wayarsu bainar jama’a su buga, saboda tsoron masu kwacen waya,” in ji shi.

Ya kara da cewa “abin da yake sa lamarin ke ci gaba shi ne kasuwannin da ake sayar da wayoyin hannu na sata na ci, ta yadda barayin sun san inda za su sami mai sayen wayar cikin ’yan awanni.”

Matakan da Gwamnatin Kano ta ɗauka

A shekarar 2023, Gwamnatin Kano da rundunar ’yan sandan jihar sun dauki aniyar kawo karshen wannan matsalar, inda gwamnatin ta yafe wa wasu batagarin matasa 222 da suka tuba kuma aka dauki 50 daga cikinsu a matsayin ’yan sandan sarauniya (special constabulary).

Kazalika gwamnatin ta kafa kwamitin tsaro na musamman karkashin Kwamishina, Dokta Yusuf Kofar Mata, domin kawo karshen matsalar.

Kazalika, Mataimakiya ta Musamman ga Gwamna kan Tsaron Al’umma, Ambasada Dakta Maimuna Umar Sharif, ta ce suna wayar da kan jama’a kan harkokin tsaro tare da sama wa ’yan sanda motocin aiki, da kuma samar da fitilu masu amfani da hasken rana a kan tituna a birni a karkara.

Ta ce nan ba da daɗewa ba za a ƙaddamar da gidauniyar tsaro kamar yadda Jihar Legas ta yi domin samar da issassun kudaden gudanar da ayyukan tsaro.

Kazalika kwamishina ’yan sanda na jihar, Ibrahim Adamu Dikko, ya shirya taro da dukkan masu unguwanni da turawan ’yan sanda daban-daban domin cimma matsaya kan yadda za a fuskaci matsalar, kuma mataimakin gwanar jihar, Aminu Abdulsalam Gwarzo, ma ya samu hallartar zaman.

Yadda za magance dabanci da ƙwacen waya a Kano

Wani masanin harkokin tsaro, Awwalu Durumin Iya, ya zayyana hanyoyin da za a kawo karshen matsalar.

Da farko, in ji masanin, “Tilas gwamnati ta samar da hanyoyin ayyukan yi ga dimbin matasa masu zaman kashe wando a sassa da lunguna.”

A cewarsa, “samun aikin yi dai dauke hankalinsu daga yawan fadace-fadacen daba da satar waya ko kwace.”

Durumin Iya ya ba da misali da garin Kura wanda mafi yawan mazauna yankin ’yan tauri ne, amma ba a fiye samun matsalolin tsaro da fadace-fadacen daba ba, saboda mafi yawa suna aikin gona da kuma noman shinkafa.”

Masanin ya kara da cewa, “Tilas a kawo karshen jagaliyar siyasa,” wadda yake ganin ita ce matsalar da ke kara taimaka wa matasan suke yin rawar gaban hantsi a zamantakewa da kuma sha’anin siyasa.

Ya yaba wa hukumar ’yan sanda saboda aiki tare da sarakunan gargajiya wajen tattara bayanai da kuma jan kunne ga masu aikata wadancan miyagun ayyuka.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Faɗan Daba Jihar Kano masu kwacen waya kawo karshen ƙwacen waya

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON

Hukumar Aikin Hajji ta Ƙasa (NAHCON) ta fara ɗaukar likitoci da sauran ma’aikatan lafiya domin aikin Hajji da ke tafe a ƙasar Saudiyya.

Hukumar NAHCON ta bayyana cewa shafin neman aikin ya fara aiki daga ƙarfe 11 na dare ranar Juma’a 12 ga Nuwamba, 2025. Za a rufe shafin da ƙarfe 11.59 ranar Litinin, 15 ga watan Disamba, 2025

Latsa nan domin shiga shafin ɗaukar ma’aikatan lafiyan kai-tsaye.

NAHCON ta bayyana cewa jami’an lafiyan da za a ɗauka Su ƙunshi likitoci, masu haɗa magunguna, malaman jinya, da jami’an kula da lafiyar lafiya da ta muhalli (CHO/EHO). Su ne za su yi aikin kula da lafiyar alhazai a yayin aikin Hajjin na shekarar 2026.

NAHCON ta bayyana cewa jami’an da suka yi aiki da ita a matsayin kula da lafiyar alhazai a  shekaru uku da suka gabata (2023 zuwa 2025) ba ne kaɗai za a ɗauka domin wannan aiki na 2026.

Yadda za ku nemi aikin

Masu nema za su shiga shafinta kai-tsaye domin ganin ka’idodin da kuma cike bayanansu. Latsa nan domin lafiyan kai-tsaye.

Ko kuma su gaida babban shafinta daga nan su latsa wasu layuka huɗu da ke hannun dama daga sama.

Daga daga nan su latsa RESOURCES, sai su latsa su shiga NMT Application Portal.

A ciki za su ga ka’idodin neman aikin, su cike bayansu, da kuma sauke duk dakardun da su cike.

Hukumar NAHCON ta bayyana cewa daga bisani za a tuntuɓi duk waɗanda suka yi nasara.

Allah Ya ba da sa’a.

Ka’idodin neman aikin

NAHCON ta jaddada cewa:

– Ma’aikatan lafiya da suka cancanta ne kawai za su iya nema aikin ba Tawagar Lafiya ta Ƙasa (NMT) domin aikin Hajjin 2026

– Aikin NMT na 2026 zai gudana ne bisa tsarin sa-kai, bisa ƙa’idojin duniya da NAHCON ta amince da su.

– Bayanai da aka bayar za su taimaka wajen tantance cancanta da shirin shiga matakin gaba na tantancewa ko jarabawa.

– Duk bayanan da aka gabatar za a duba su. Duk wani kuskure. Ɓoye gaskiya, ko ƙirƙirar bayanan ƙarya zai iya jawo ƙin amincewa da aikace-aikacen ko cirewa daga jerin waɗanda cancanta.

– Wannan aikace-aikacen kyauta ne gaba ɗaya. NAHCON ba ta karɓar kuɗi kai tsaye ko a kaikaice, ko ta hannun wakilai ko hukumomi. Ku yi hattara!

– Cika fom ɗin ba ya nufin an amince da cancanta ko zaɓen ku.

 

Ƙa’idar shekaru:

– Likitoci: 27 zuwa 60 shekara

– Masu haɗa Magunguna: shekara 26 zuwa 60

– Nas da sauran rukuni: 22–60 shekara .

Sharuɗɗa

Dole masu neman shiga NMT su kasance:

1. Suna aiki a lokacin neman shiga.

2. Ba su halarci ayyukan NMT a shekara uku da suka gabata ba (2023, 2024, da 2025).

3. Su kasance a shirye su yi aiki na tsawon kwanaki 28 da kuma zama a Saudiyya har zuwa kwanaki 45 kafin dawowa Najeriya.

4. Ba za a sallame su a wurin aikinsu ba kafin su kammala aikin NMT.

5. Su nuna kyawawan halaye tare da bin ƙa’idojin aikin lafiya da na NAHCON.

6. Su gabatar da tabbacin mai tsaya musu (guarantor).

 

Sharuɗɗan Guarantor:

– Dole ya kasance mutum mai daraja: Ma’aikacin gwamnati (ba ƙasa da GL 15), basaraken gargajiya, Alƙali (Magistrate), ko Shugaban Ƙaramar Hukuma.

– Dole ya san mai neman aikin NMT tsawon aƙalla shekaru biyar kuma ya tabbatar da gaskiya, ƙwarewa, da iya aikinsa.

– Dole ya gabatar da kwafin katin shaida ko wata takardar shaida da ake amfani da ita a ofisoshin gwamnati na Najeriya.

 

Takardun da dole a haɗa da su:

– Fom ɗin Guarantor da aka cika

– Takardar shaidar ƙwarewar aiki (Basic Professional Certificate)

– Takardar NYSC (idan ta shafi mai nema)

– Lasisin aikin lafiya na wannan shekara

– Hoton fasfo (mai farin baya)

– Sanarwar mai nema (applicant’s declaration)

– Takardar izini daga wurin aiki (employer’s clearance letter) .

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tsaro: Abba ya kafa runduna ta musamman da za ta ke tsaron tashoshin mota a Kano
  • Shirin kafa ‘Hisbar Ganduje’ ya tayar da ƙura a Kano
  • Haɗin Kan Musulmai Da Kirista A Nijeriya Zai Kawo Saukin Matsalar Tsaro — Shehu Sani
  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • Yadda za ku cike neman aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Yadda za ku nemi aikin jami’an lafiya a Hajjin 2026 da NAHCON
  • Kungiyar NLC A Najeriya Ta Shirya Zanga-Zanga Kan Matsalar Rashin Tsaro A Fadin Kasa
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Gwamnonin Arewa Sun Yi Rawar Gani A Kafa Gidauniyar Fuskantar Matsalar Tsaro
  • Yadda Bunkasar Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samar Da Karin Damammaki Ga Kasashe Masu Tasowa