Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115
Published: 28th, April 2025 GMT
115-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissiso da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan, ko kum littafin mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi.
///… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-hassan limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), kuma da na farko ga Fatimah(s) diyar manzon All..(s), sannan jikansa na farko.
A cikin shirimmu da ya gabata, mun ji yadda wasu malaman tarihi suka kawo wasu hadisai wadanda basu inganta ba suka jinginawa Imam Alhassan Almujtaba (a) dangane da son da yakewa khalifa na ukku wasu Uthman bin Affan, mun gudanar da bincike cikin daya daga cikin hadisan a sanadi da kuma mataninsa inda muka tabbatar da cewa , Mada’ini wanda aka ruwaito wannan hadisin, nasibi ne, wato wata jama’a wacce ta ke addini da kiyayya ga iyalan gidan manzon All..(s), har’ila yau yana kirkiro hadisan na kariya ya jinganawa manzon All..(s) na muzantasu da kuma kirkiro wasu hadisan daga manzon All..(s) na yabon banu umayya.
Sannan a matanin hadisin mun bayyana kariyar zance mai cewa Imam Hassan yana zargin babansa Imam Ali (a) da hannu a kashe Uthman dan Affan, sannan yana tare da mahaifinsa, manya-manyan yake-yake guda biyu da yayi a lokacin khalifancinsa, da wadanda suke tuhumarsa da zubar da jinin Khalifa Uthman.
Wato yake-yaken Jamal da Siffin. Imam Hassan (a) ya yaki wadannan makiyan mahaifinsa wadanda suke zarginsa da hannu a kissan Uthman. Kuma bamu taba sanin akwai sabani tsakanin Imam Ali (a) da yayansa Alhassan da Alhussain (a).
Daga karshen mun kawo maku yadda manyamanayn sahabban manzon All..(s) da suka rage a Madina suka rubuta wasi ku zuwa sauran sahabbansa a sauran yankuna na daular musulunci suna neman taimakonsu don kauda Khalifa uthman daga khalifanci, saboda ya sabawa littafin All..da sunnar manzon All..da kuma siran khalifofin da suka gabata. Sun koka kan yadda ya mika al-amuran daular musulunci ga danginsa banu Umayya suna satar dukiyar al-umma sannan sun barsu da talauci.
Mun bayyana cewa akwai abubun lura a cikin wannan wasikar kamar haka,
1-Sunan zarginsa na kin amfani da littafin All..
02-Sauya sunnan manzon All..(s) da kuma, yayi watsi da ita,
03-yayi watsi ga hanyar khalifofin biyu da suka gabace shi wato Abubakar da Umar
04- Ya kauda ma’anar khalifancin manzon All..(s) daga yadda yakamata ta kasance,
5-Kwace dukkan duniyar Al-ammu da kuka sarrafata a wasu wurare kebantattu, wato kashe ta kan dangin khalifa wato Banu Umayya.
Malaman tarihi sun bayyana cewa, wadannan al-amura sun girgiza daular musulunci, kuma sun kusan su rusata.
Sannan mun bayyana cewa wadanda suke sukan shugabancin Khalifa Uthman sun rubuta wata wasika ga murabiduna, wato wadanda suke kula da kan iyakokin daular musulunci daga cikin sahabbai, sun bukacesu su dawo madina don tsada khalifancin manzon All..(a), don tabbatar da khaifancin ya dawo kan yadda yakamata ya kasanci.
Ga kuma matanin wasikar kamar haka.
{Lalle ku, kun fita ne don ku yi jihadi a kan tafarkin All..mai girma da daukaka, kuna neman kare addinin Muhammad (s) to lalle khalifanku ya lalata addnin Muhammadu, ku dawo ku tsaida shi,…}.
Banda haka a lokacinda wasikun nan suka isa yankuna da dama na daular musulunci sun yi ta aika tawaga don ganin abinda yake faruwa a Madina, sannan tawagogi da suka isa Madina don ganewa idanunsu abubuwan da suke faruwa, da kuma tattauna matsalolin da kuma yadda za’a magance su, sun hada da.
Tawaga daga kasar Masar, kafin haka akwai mutane 700 da suka tura tun farko bayan da suka kama wani bawan Khalifa Uthman wanda ake kira warsh dauke da wasikar Khalifa zuwa dan uwansa gwamnan Masar Abdullahi ibn Abisharkh, na ya kashe sui dan sun isa da sabon kwamna Muhammad dan Abubakar.
A wannan karon mutanen masar sun aiki mutane 400. Tare da jagorancin Muhammad dan Abubakar wanda dama yana manina, da Abdrrahman dan Udais Al-balawi.
2-sai tawagar Kufa wanda ya hada da Malik dan Ashtar, Zaidu dan Sauhan Al-Abdi, da Ziyad dan Annadhir Al-harithy. Da abdullahi dan Asam Al-Amuri da shugabansu gaba daya, Amru dan Ah-tham .
03-sai tawagar Basra wacce ta hada da Hakin dan Jibilah, tere da wasu mutane 100. Bayan haka wasu khamsin sun bisu. A cikinsu akwai Zarih dan Abidi Al-Abdi, da bishru dan shuraih Alkaisi, da dan Mahrash, da wasunsu daga cikin fitattun mutane kuma sanannu na Basra.
A lokacinda wadannan tawagogi suka isa Madina an yi maraba da su, kuma nag ode masu da karban kiran da aka yi masu, sannan sun tattauna da sauran sahabbai da kuma musulmai dan al-amuran da suka faru, da kuma irin mummunan halin da musulmi suka shiga ciki saboda yadda Khalifa Uthman ya sauya al-amura da dama, daga cikin ya hanasu dukiyoyinsu, wadanda suka saba samu a zamanin khalifofin da suka gabata. Ko kuma ya fita daga tsarin da manzon All..(s) yake raba dukiya a cikin al-umma.
Bayan yan kwanaki sai mutanen kasar masar sun ga cewa kafin ko me da farko a rubutawa khalifa Usman wasika, a yi masa nisiha kan ya dawo kan tafarkin da ya dace ga kuma kadan daga cikin abinda wasikar ta kunsa.
Bayan Basmala da salati ga manzon All..(s) da kuma godiya ga All..sai suka ce
(bayan haka, ka sani kan cewa, {Lalle All..baya sauya halin da mutane suke ciki sai sai sun sauya halinsu, muna hadaka da All..kuma muna sake hadaka da All..Lalle kai kana cikin duniya mai gucewa, … .. kuma kada ka manta da rabon a lahira, kada duniya ta rudeka, kuma ka san cewa mu don All..muke yi, kuma don All…muke fushi. Kuma muna neman yardarm All.. ne, kuma lalle ba zamu dauke takubbammu daga wuyoyimmu ba saika tuba daga abubuwan da ka aikata mana, tuba mai tsanani kuma a fili, wannan shi ne maganarmu da kai, sannan bukatarmu a gareka, All..ne mai karban uzurimmu dangane da kai..wassalam…}.
A lokacinda Khalifa Uthman ya karanta sai ya ji tsoro. Sai Mughira ya nemi izininsa yayi Magana da mutane, sai ya bashi izini, a lokacinda suka ganshi sai suka daga murya suna cewa: Ya makaho koma ya Fajiri koma ya fasiki koma.ya koma ya kasa Magana da su.
Sai Uthman ya kira Amru dan Asi, ya bukaci yayi Magana da su, ya amince, amma a lokacinda suka ganshi, sai yayi masu, sallama ba wanda ya amsa daga cikinsu, suka daga murya suna cewa: Ko koma ya makiyin All.. ka kuma ya dan Nabigha. Kai ba amintecce ne a wajemmu ba kuma mai aminci ba.
A nan sai Khalifa Uthman ya fahinci cewa babu wanda zai taimaka masa sai Amirulminina Aliyu dan Abitalib (a), sai ya nemi taimakonsa, ya fada masa cewa, yayi kira ga mutane zuwa ga Alkur’ani mai girma da sunnar annabinsa.
Sai Imam ya amince, amma da sharudda kan cewa, ya yi masa alkawali tsakaninsa da All..zai yi aiki da abinda ya fada. Sai ya yi alkawali zai zai cika alkawalinsa, za iyi aiki da abinda ya fada.
Sai Imam (a) ya je wajen mutane, shima a lokacinda suka ganshi suka ce, koma , sai yace a’a na zo maku da cewa, za’a yi aiki da littafin All.., kuma za’a sauya duk abinda kuka yi fushi dominsa. Sai ya fada masu abinda khlifa ya bada. Sai suka ce: Ka lamunce mana haka zai faru? Sai yace :ee. Sai suka ce mun yarda.
Sai ya shigar da manya manya daga fitattun mutane wajen Uthman, sai suka yi ta sukansa, sannan suka ce, ya Sanya abinda ya yi alkawali na aiki da littafin All..da kuma sunnar manzon All..(s) da kuma bawa musulmi hakkinsu da ake basu.
Sai ya amince ya rubuta ya basu sannan suka karbi takardan suka kama hanyar masar.
Wannan shi ne nassin abinda ya rubuta ya basu’
{Wannan rubutun daga bawan All..Uthman Amirulmuminina zuwa ga wadanda suke sukansa daga cikin muminai da musulmai, kan cewa hakkinsu ne in yi aiki da littafin All..da sunnar annabinsa a cikinu, za’a bawa talaka hakkinsa, wanda yake cikin tsoro a amintar da shi, wanda aka kora adawo da shi …kuma za’a samar da kudade ga musulmi. Sannan Aliyu dan Abitalib (a) shi ne mai lamuncewa muminai, kuma wajibi ne ga Uthman ya cika alkawalin da ya dauka cikin wannan rubutun}.
Banda haka Zubair dan Awwam, Talha dan Ubaidullahi,Sa’du dan Abi wallas, Abdullahi dan Umar, Zaidu dan Thabit, Sahal dan Hunaif,, Abu ayyuba Khalid dan zaid, kuma anyi wannan rubutun a cikin watan Zulkida shekara ta shekara 35.
Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu. Wassalau alaikum warahamatullahi wa barakathu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: daular musulunci wadanda suke masu sauraro
এছাড়াও পড়ুন:
Ziyarar Putin a Indiya alama ce da ke nuna cewa New Delhi na yin watsi da gargadin Trump?
Pars Today – Vladimir Putin ya yi tafiya zuwa Indiya don ƙarfafa dangantakar ƙasashen biyu.
Vladimir Putin, shugaban Rasha, ya isa New Delhi a ranar Alhamis, 4 ga Disamba, a ziyararsa ta farko zuwa Indiya tun bayan fara yakin Ukraine a 2022. Ziyarar ta kwanaki biyu na da nufin zurfafa haɗin gwiwa tsakanin tsaro da kasuwanci tsakanin ƙasashen biyu. Putin yana tare da wata babbar tawaga wacce ta haɗa da ministan tsaron Rasha. Ana sa ran zai halarci wani cin abincin dare na sirri tare da Firayim Ministan Indiya Narendra Modi, sannan tattaunawa ta hukuma da zaman tattalin arziki, gami da taron kolin shekara-shekara na 23.
A lokacin ziyarar, ana sa ran ɓangarorin biyu za su sanya hannu kan yarjejeniyoyi 10 tsakanin gwamnatoci da yarjejeniyoyi sama da 15 na kasuwanci, tare da sanya fifiko kan tattalin arziki a cikin dabarun tattalin arziki har zuwa 2030, da kuma yiwuwar haɓaka cinikin ƙasashen biyu zuwa dala biliyan 100. Haɗin gwiwar tsaro yana ɗaya daga cikin manyan fannoni na tattaunawa, tare da makamashi da manyan alaƙar kasuwanci.
Tafiyar Putin ta zo ne a lokacin da Indiya ke fuskantar matsin lamba daga gwamnatin Trump kan siyan man fetur na Rasha da aka rage. Tun daga shekarar 2022, Indiya ta zama ɗaya daga cikin manyan abokan cinikin mai a Rasha, inda ta adana biliyoyin daloli ta hanyar rage farashin shigo da mai daga ƙasashen waje. Duk da haka, takunkumin da Amurka ta sanya wa manyan kamfanonin Rasha kamar Rosneft da Lukoil sun riga sun rage yawan man da Indiya ke fitarwa daga Rasha. A watan Agusta na 2025, gwamnatin Trump ta sanya harajin kashi 50% kan yawancin kayayyakin Indiya, tana mai nuni da dogaro da Indiya kan man Rasha da kuma abin da Washington ta kira tallafin kuɗi kai tsaye ga yakin Ukraine. Wannan matakin ya haifar da damuwa sosai a New Delhi, domin duk wani sabon yarjejeniyar makamashi ko tsaro da Moscow zai iya haifar da ƙarin ramuwar gayya daga Amurka.
Duk da waɗannan matsin lamba, Rasha ta bayyana cewa ba ta damu ba kuma ta ci gaba da mai da hankali kan faɗaɗa alaƙa da Indiya. Masu sharhi sun yi jayayya cewa haɗin gwiwar dabarun da ke tsakanin ƙasashen biyu zai dawwama, koda kuwa siyan mai ya ragu, saboda Rasha ta ci gaba da samar da muhimman kayan gyara ga tsoffin kayan aikin soja na Indiya. Ciniki tsakanin ƙasashen biyu ya kai dala biliyan 68.7 a tsakanin 2024-2025 – kusan sau shida kafin barkewar cutar. Duk da haka, fitar da kayayyaki daga Indiya zuwa Rasha ya kasance ƙasa da dala biliyan 5, kuma New Delhi na neman ƙarin damar shiga kasuwar Rasha don magunguna, motoci, da ayyuka.
Bayan tsaro da tattalin arziki, ziyarar tana da matuƙar muhimmanci a fannin siyasa. Ga Indiya, karɓar bakuncin Putin alama ce ta ‘yancin kai na dabaru da kuma sha’awarta ta kiyaye daidaiton manufofin ƙasashen waje. Ga Putin – wanda ba kasafai yake tafiya ƙasashen waje ba – tafiyar ta nuna muhimmancin da Moscow ke bai wa dangantakarta da New Delhi. Wani jami’in ma’aikatar harkokin wajen Indiya ya bayyana dangantaka da Rasha a matsayin “haɗin gwiwa mafi karko a wannan zamani,” yana mai jaddada cewa ya kamata a duba ziyarar ta hanyar amfani da hanyoyin haɗin gwiwa na ƙasashen biyu.
Ba za a iya fassara tafiyar Putin kawai a matsayin New Delhi da ke yin watsi da barazanar gwamnatin Trump ba. Maimakon haka, tana nuna dabarun Indiya na dogon lokaci na kiyaye ‘yancin kai da daidaito a dangantakarta ta duniya. A cikin ‘yan shekarun nan, Indiya ta yi aiki don ci gaba da haɗin gwiwa mai inganci da dukkan manyan ƙasashe yayin da take guje wa dogaro da kowace abokin tarayya guda ɗaya. Rasha ta kasance ginshiƙi ga wannan hanyar, idan aka yi la’akari da rawar da ta taka a matsayin babban mai samar da makamai na Indiya kuma mai ci gaba da samar da fasahar tsaro da kayayyakin gyara.
Gargaɗin gwamnatin Trump—ciki har da hauhawar farashin kaya a kan kayayyakin Indiya da matsin lamba na rage shigo da mai daga Rasha—halaye ne da Indiya ba za ta iya mantawa da su ba. Washington ta ci gaba da rashin jin daɗin dangantakar makamashi da tsaro da Indiya ke da ita da Moscow, tana kallon su a matsayin goyon baya kai tsaye ga ƙoƙarin Rasha a Ukraine. Duk da haka, Indiya ba ta cikin ikon nisanta kanta daga Rasha gaba ɗaya. Ta dogara ne da kayan aikin soja na Rasha, waɗanda ba su da sauri ko araha. Haka kuma ta amfana da kuɗi daga man fetur na Rasha da aka rage a cikin ‘yan shekarun nan.
Ziyarar Putin ta nuna muhimmancin da dangantakar ke da shi ga ɓangarorin biyu. Ga Rasha, tana aika da sigina cewa duk da takunkumin da ƙasashen yamma suka sanya mata, har yanzu za ta iya ci gaba da haɗin gwiwa da manyan ƙasashen yankin. Ga Indiya, tafiyar ta nuna cewa ba za ta yanke shawara kan manufofin ƙasashen waje ba kawai a ƙarƙashin matsin lambar Amurka. Ta hanyar maraba da Putin, New Delhi tana neman nuna cewa alaƙa da Moscow wani ɓangare ne na manufofin ƙasashen waje masu daidaito, masu haɗin gwiwa da yawa—ba wai kawai wani ɓangare na hamayyar Amurka da Rasha ba.
Wannan ba yana nufin Indiya ta yi watsi da gwamnatin Trump gaba ɗaya ba. A aikace, Indiya ta riga ta rage shigo da man fetur na Rasha kuma tana ci gaba da tattaunawa a hankali da Amurka don guje wa tashin hankali mai tsanani. Saboda haka ziyarar Putin ta nuna ƙoƙarin Indiya na daidaita matsin lambar Amurka da buƙatunta na dabaru idan aka kwatanta da Rasha. New Delhi ta san cewa ba tare da kyakkyawar alaƙa da Moscow ba, shirye-shiryenta na tsaro da tsaron makamashi za su sha wahala.
Gabaɗaya, tafiyar Putin zuwa Indiya ta nuna ƙudurin ƙasashen biyu na ci gaba da ƙarfafa haɗin gwiwarsu na dabarun yaƙi duk da matsin lamba daga ƙasashen duniya. Haɗin gwiwar tsaro, cinikin makamashi, da la’akari da yanayin ƙasa sun kasance a cikin ginshiƙin dangantakar, kuma ɓangarorin biyu suna ci gaba da ɗaukar juna a matsayin muhimman abokan hulɗa na dabarun yaƙi. Ziyarar ta sake tabbatar da juriyar haɗin gwiwar Indiya da Rasha na dogon lokaci.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Mayar Da Martani Kan Sanarwar Bayan Taron Majalisar Kasashen Yankin Tekun Fasha December 5, 2025 Afirka ta Kudu Za Ta Dauki Hutu Daga Halartar Tarukan G20 A Karkashin Shugabancin Trump December 5, 2025 Microsoft Za Ta Fuskanci Hukunci Kan Taimaka Wa Laifukan Isra’ila A Kan Falasdinawa December 5, 2025 Amurka Tana Sake Yin Bitar Alakar Da Ke Tsakaninta Da Tanzania December 5, 2025 Fadlallah Na Hizbullah Ya Yi Kiran Hadin Kai A Tsakanin Musulmi Da Larabawa Domin Fuskantar Kalubale December 4, 2025 Jiragen Haramtacciyar Kasar Isra’ila Sun Kai Hare-hare A Kudancin Lebanon December 4, 2025 An Kira Yi Gwamnatin Canada Da Ta Kama Olmert Da Livini Na “Isra’ila December 4, 2025 An Kashe Shugaban ‘Yan Dabar Gaza “Abu Shabab” Da Isra’ila Ke Goyon Baya December 4, 2025 Iran : Jagora Ya Bayyana Ra’ayin Musulunci Kan Hakkokin Mata December 4, 2025 Taron IMO : Tehran Ta Yi Watsi Da Zarge-zargen Isra’ila Marasa Tushe December 4, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci