Kissoshin Rayuwa: Imam Hassan (a) 115
Published: 28th, April 2025 GMT
115-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissiso da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan, ko kum littafin mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi.
///… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-hassan limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), kuma da na farko ga Fatimah(s) diyar manzon All..(s), sannan jikansa na farko.
A cikin shirimmu da ya gabata, mun ji yadda wasu malaman tarihi suka kawo wasu hadisai wadanda basu inganta ba suka jinginawa Imam Alhassan Almujtaba (a) dangane da son da yakewa khalifa na ukku wasu Uthman bin Affan, mun gudanar da bincike cikin daya daga cikin hadisan a sanadi da kuma mataninsa inda muka tabbatar da cewa , Mada’ini wanda aka ruwaito wannan hadisin, nasibi ne, wato wata jama’a wacce ta ke addini da kiyayya ga iyalan gidan manzon All..(s), har’ila yau yana kirkiro hadisan na kariya ya jinganawa manzon All..(s) na muzantasu da kuma kirkiro wasu hadisan daga manzon All..(s) na yabon banu umayya.
Sannan a matanin hadisin mun bayyana kariyar zance mai cewa Imam Hassan yana zargin babansa Imam Ali (a) da hannu a kashe Uthman dan Affan, sannan yana tare da mahaifinsa, manya-manyan yake-yake guda biyu da yayi a lokacin khalifancinsa, da wadanda suke tuhumarsa da zubar da jinin Khalifa Uthman.
Wato yake-yaken Jamal da Siffin. Imam Hassan (a) ya yaki wadannan makiyan mahaifinsa wadanda suke zarginsa da hannu a kissan Uthman. Kuma bamu taba sanin akwai sabani tsakanin Imam Ali (a) da yayansa Alhassan da Alhussain (a).
Daga karshen mun kawo maku yadda manyamanayn sahabban manzon All..(s) da suka rage a Madina suka rubuta wasi ku zuwa sauran sahabbansa a sauran yankuna na daular musulunci suna neman taimakonsu don kauda Khalifa uthman daga khalifanci, saboda ya sabawa littafin All..da sunnar manzon All..da kuma siran khalifofin da suka gabata. Sun koka kan yadda ya mika al-amuran daular musulunci ga danginsa banu Umayya suna satar dukiyar al-umma sannan sun barsu da talauci.
Mun bayyana cewa akwai abubun lura a cikin wannan wasikar kamar haka,
1-Sunan zarginsa na kin amfani da littafin All..
02-Sauya sunnan manzon All..(s) da kuma, yayi watsi da ita,
03-yayi watsi ga hanyar khalifofin biyu da suka gabace shi wato Abubakar da Umar
04- Ya kauda ma’anar khalifancin manzon All..(s) daga yadda yakamata ta kasance,
5-Kwace dukkan duniyar Al-ammu da kuka sarrafata a wasu wurare kebantattu, wato kashe ta kan dangin khalifa wato Banu Umayya.
Malaman tarihi sun bayyana cewa, wadannan al-amura sun girgiza daular musulunci, kuma sun kusan su rusata.
Sannan mun bayyana cewa wadanda suke sukan shugabancin Khalifa Uthman sun rubuta wata wasika ga murabiduna, wato wadanda suke kula da kan iyakokin daular musulunci daga cikin sahabbai, sun bukacesu su dawo madina don tsada khalifancin manzon All..(a), don tabbatar da khaifancin ya dawo kan yadda yakamata ya kasanci.
Ga kuma matanin wasikar kamar haka.
{Lalle ku, kun fita ne don ku yi jihadi a kan tafarkin All..mai girma da daukaka, kuna neman kare addinin Muhammad (s) to lalle khalifanku ya lalata addnin Muhammadu, ku dawo ku tsaida shi,…}.
Banda haka a lokacinda wasikun nan suka isa yankuna da dama na daular musulunci sun yi ta aika tawaga don ganin abinda yake faruwa a Madina, sannan tawagogi da suka isa Madina don ganewa idanunsu abubuwan da suke faruwa, da kuma tattauna matsalolin da kuma yadda za’a magance su, sun hada da.
Tawaga daga kasar Masar, kafin haka akwai mutane 700 da suka tura tun farko bayan da suka kama wani bawan Khalifa Uthman wanda ake kira warsh dauke da wasikar Khalifa zuwa dan uwansa gwamnan Masar Abdullahi ibn Abisharkh, na ya kashe sui dan sun isa da sabon kwamna Muhammad dan Abubakar.
A wannan karon mutanen masar sun aiki mutane 400. Tare da jagorancin Muhammad dan Abubakar wanda dama yana manina, da Abdrrahman dan Udais Al-balawi.
2-sai tawagar Kufa wanda ya hada da Malik dan Ashtar, Zaidu dan Sauhan Al-Abdi, da Ziyad dan Annadhir Al-harithy. Da abdullahi dan Asam Al-Amuri da shugabansu gaba daya, Amru dan Ah-tham .
03-sai tawagar Basra wacce ta hada da Hakin dan Jibilah, tere da wasu mutane 100. Bayan haka wasu khamsin sun bisu. A cikinsu akwai Zarih dan Abidi Al-Abdi, da bishru dan shuraih Alkaisi, da dan Mahrash, da wasunsu daga cikin fitattun mutane kuma sanannu na Basra.
A lokacinda wadannan tawagogi suka isa Madina an yi maraba da su, kuma nag ode masu da karban kiran da aka yi masu, sannan sun tattauna da sauran sahabbai da kuma musulmai dan al-amuran da suka faru, da kuma irin mummunan halin da musulmi suka shiga ciki saboda yadda Khalifa Uthman ya sauya al-amura da dama, daga cikin ya hanasu dukiyoyinsu, wadanda suka saba samu a zamanin khalifofin da suka gabata. Ko kuma ya fita daga tsarin da manzon All..(s) yake raba dukiya a cikin al-umma.
Bayan yan kwanaki sai mutanen kasar masar sun ga cewa kafin ko me da farko a rubutawa khalifa Usman wasika, a yi masa nisiha kan ya dawo kan tafarkin da ya dace ga kuma kadan daga cikin abinda wasikar ta kunsa.
Bayan Basmala da salati ga manzon All..(s) da kuma godiya ga All..sai suka ce
(bayan haka, ka sani kan cewa, {Lalle All..baya sauya halin da mutane suke ciki sai sai sun sauya halinsu, muna hadaka da All..kuma muna sake hadaka da All..Lalle kai kana cikin duniya mai gucewa, … .. kuma kada ka manta da rabon a lahira, kada duniya ta rudeka, kuma ka san cewa mu don All..muke yi, kuma don All…muke fushi. Kuma muna neman yardarm All.. ne, kuma lalle ba zamu dauke takubbammu daga wuyoyimmu ba saika tuba daga abubuwan da ka aikata mana, tuba mai tsanani kuma a fili, wannan shi ne maganarmu da kai, sannan bukatarmu a gareka, All..ne mai karban uzurimmu dangane da kai..wassalam…}.
A lokacinda Khalifa Uthman ya karanta sai ya ji tsoro. Sai Mughira ya nemi izininsa yayi Magana da mutane, sai ya bashi izini, a lokacinda suka ganshi sai suka daga murya suna cewa: Ya makaho koma ya Fajiri koma ya fasiki koma.ya koma ya kasa Magana da su.
Sai Uthman ya kira Amru dan Asi, ya bukaci yayi Magana da su, ya amince, amma a lokacinda suka ganshi, sai yayi masu, sallama ba wanda ya amsa daga cikinsu, suka daga murya suna cewa: Ko koma ya makiyin All.. ka kuma ya dan Nabigha. Kai ba amintecce ne a wajemmu ba kuma mai aminci ba.
A nan sai Khalifa Uthman ya fahinci cewa babu wanda zai taimaka masa sai Amirulminina Aliyu dan Abitalib (a), sai ya nemi taimakonsa, ya fada masa cewa, yayi kira ga mutane zuwa ga Alkur’ani mai girma da sunnar annabinsa.
Sai Imam ya amince, amma da sharudda kan cewa, ya yi masa alkawali tsakaninsa da All..zai yi aiki da abinda ya fada. Sai ya yi alkawali zai zai cika alkawalinsa, za iyi aiki da abinda ya fada.
Sai Imam (a) ya je wajen mutane, shima a lokacinda suka ganshi suka ce, koma , sai yace a’a na zo maku da cewa, za’a yi aiki da littafin All.., kuma za’a sauya duk abinda kuka yi fushi dominsa. Sai ya fada masu abinda khlifa ya bada. Sai suka ce: Ka lamunce mana haka zai faru? Sai yace :ee. Sai suka ce mun yarda.
Sai ya shigar da manya manya daga fitattun mutane wajen Uthman, sai suka yi ta sukansa, sannan suka ce, ya Sanya abinda ya yi alkawali na aiki da littafin All..da kuma sunnar manzon All..(s) da kuma bawa musulmi hakkinsu da ake basu.
Sai ya amince ya rubuta ya basu sannan suka karbi takardan suka kama hanyar masar.
Wannan shi ne nassin abinda ya rubuta ya basu’
{Wannan rubutun daga bawan All..Uthman Amirulmuminina zuwa ga wadanda suke sukansa daga cikin muminai da musulmai, kan cewa hakkinsu ne in yi aiki da littafin All..da sunnar annabinsa a cikinu, za’a bawa talaka hakkinsa, wanda yake cikin tsoro a amintar da shi, wanda aka kora adawo da shi …kuma za’a samar da kudade ga musulmi. Sannan Aliyu dan Abitalib (a) shi ne mai lamuncewa muminai, kuma wajibi ne ga Uthman ya cika alkawalin da ya dauka cikin wannan rubutun}.
Banda haka Zubair dan Awwam, Talha dan Ubaidullahi,Sa’du dan Abi wallas, Abdullahi dan Umar, Zaidu dan Thabit, Sahal dan Hunaif,, Abu ayyuba Khalid dan zaid, kuma anyi wannan rubutun a cikin watan Zulkida shekara ta shekara 35.
Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wata fitowa idan All..ya kaimu. Wassalau alaikum warahamatullahi wa barakathu.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: daular musulunci wadanda suke masu sauraro
এছাড়াও পড়ুন:
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Bayyana Dalilan Hana Jami’anta Auren ‘Yan Kasashen Waje
Babi na 25 na sabuwar doka ya shafi batun aure ga jami’ai da sojojin rundunar tsaro.
Musamman, Sashe na 5 na wannan takarda ya bayyana cewa “ba a yarda wani jami’i ya auri bakuwa ko kuma dan Nijeriya da aka ba takardar zama ba.”
Za A Sake Duba Daftarin HTACOS Bayan Shekara Biyar
Sabon Daftarin HTACOS na shekarar 2024, wanda Majalisar Rundunar Sojoji ta amince da shi, ya fara aiki ne a ranar 6 ga Disamba, 2024, lokacin da Shugaban Kasa ya sanya wa takardar hannu.
A cewar Babi na 25, Sashe na 1, dan karamin jami’i mai mukamin Second Lieutenant, Midshipman ko Pilot Officer (2Lt/Mid/Plt Offr) yana cikin lokacin gwaji ne, kuma ana tsammanin zai zauna a gidan jami’ai (Officers’ Mess) ba tare da matar aure ba.
Haka kuma, ba a yarda ya yi aure ba, kuma idan ya riga ya yi aure kafin ya shiga makarantar horo, duk da cewa hakan yana cikin bayanansa, ba za a dauke shi a matsayin jami’in da ya yi aure ba dangane da batun masauki, albashi, da sauran alawus-alawus da ake bai wa jami’an da suka yi aure.
Sai dai, Sashe na 2 na wannan babi ya bayyana cewa, “idan wani soja, jami’in ruwa ko jami’in sama ya samu matsayi na jami’i a cikin kowace runduna ko reshe a matsayin Second Lieutenant, Midshipman ko Pilot Officer (2Lt/Mid/Plt Officer), kuma yana da aure kafin a daga darajarsa, zai zauna a gidan jami’ai (Officers’ Mess) na tsawon akalla watanni uku. Bayan haka, ana iya ba shi gida na jami’an da suka yi aure idan akwai, ko kuma a ba shi kudin haya a madadin haka.”
A cewar doka, kafin aure, jami’ai dole ne su nemi amincewar manyan hukumomi tare da gabatar da abokan aurensu domin binciken cancanta.
Babi na 25, Sashe na 3–4 ya bayyana cewa: “Duk wani jami’i da bai yi aure ba dole ne ya fara neman izinin hukumar da ta dace kafin ya yi niyyar aure. Jami’in RCC ba zai cancanci neman aure ba sai bayan shekaru biyar da samun mukamin jami’i.”
Amincewar za ta kasance ne kawai bayan an kammala bincike da tantancewar matar da jami’in yake son aura ta hannun hukumarta ta sama da ta dace.
“Idan wani jami’i ya auri soja, jami’in ruwa, ko jami’in sama (namiji ko mace) a karkashin kowace dokar da ke akwai, za a ba jami’in ko wannan soja/jami’in damar yin ritaya daga Rundunar daga ranar wannan aure. Idan ma’aikatan da suka yi aure ga juna aka daga darajarsu, matar aure ko mijin jami’in da aka daga darajarsa za a sallame shi daga Rundunar.”
Laifi ne ga wani jami’i ya boye aurensa da soja, jami’in ruwa, ko jami’in sama (namiji ko mace) domin hana jami’in ko wannan soja/jami’in yin ritaya daga Rundunar.
Dalilin Da Ya Sa Aka Bayyana Haka – Tsohon Janar
A halin yanzu, wani tsohon janar mai ritaya, da aya nemi a sakaya sunansa, ya ce dokar an kafa ta ne don hana sojoji bayyana bayanai ga kasashen waje ta hannun matansu ko mazansu.
Ya ce babu yadda wani jami’i zai guji tattaunawa da matarsa ko mijinta kan al’amuran aiki lokaci-lokaci, inda ya kara da cewa yin hakan tare da abokin aure bako na kasashen waje na iya kawo barazana ga dan kasar jami’in.
Ya ce, “Tabbas, dokar an kafa ta ne don kare bayanai da sauran al’amuran tsaro. Ka yi tunanin soja dan Nijeriya da ya auri bako dan wata kasa kamar daga Kamaru ko Laberiya, kuma Nijeriya ta shiga yaki da dayan wadannan kasashen, abin da ake tsammani shi ne cewa aminci na iya rabuwa ko wani abu makamancin haka. Idan aka yarda da hakan gaba daya, hakan ba zai amfani kasa ba daga bangaren tsaro.”
Tsohon Kwamandan Runduna Ya Ce A Sake Duba Dokar
Kwamandan Runduna Shehu Sadeek (mai ritaya) ya ce, duk da cewa wannan Daftari ya samo asali ne daga tsaron kasa, ya kamata a sake duba irin wannan doka bisa ga kyawawan hanyoyi da kasashe masu ci gaba ke bi, inda ake yin bincike kan abokin aure da aka nufa. Ya ce yawancin rundunonin soja a duniya suna da irin wadannan dokoki amma ba sa hana aure gaba daya.
Ya bayyana cewa HTCOS (Ka’idoji da Sharudan Aiki na Rundunar Sojoji) Daftari ne da rundunar kanta ta tsara don tsara yadda al’amuran cikin rundunar za su gudana, kuma ta bambanta da Dokar Rundunar Sojoji (Armed Forces Act).
A cewar sa, haramcin aure da baki gaba daya an kafa shi ne don hana yiwuwar barazanar tsaro saboda jami’ai na da damar samun bayanai masu muhimmanci. Ya kara da cewa wannan tanadi ya samo asali ne daga la’akari da tsaron kasa, ba daga son ra’ayi ko al’adu ba.
Ya ce aure da bako na iya samar da hanyar bayyana sirrin kasa ba da gangan ba.
Na biyu, ya ce haramcin yana da alaka da dan kasa da biyayya, inda ya kara da cewa “dan kasar bakon abokin aure na iya haifar da tambayoyi game da biyayya biyu, kamar hakkin gado da hakkin zama, a hanyoyi da ka iya saba wa dokokin tsaron Nijeriya.”
Na uku, a cewarsa, shi ne hadarin tura jami’ai aiki da kuma matsalolin da ke tattare da wuraren aiki. Ya ce jami’ai da suka yi aure da baki na iya fuskantar takurawa lokacin da aka tura su kasashen waje, musamman idan suna rike da mukamai masu mahimmanci, watakila a fannin leken asiri, wanda ke kawo cikas ga gudanar da ma’aikata. Dalili na karshe da ya bayar shi ne alaka ta mayar da martani da dalilan diflomasiyya.
A cewar Shehu, yawancin rundunonin soja a duniya suna da irin wadannan dokoki. Sai dai ya bayyana cewa ba doka ce ta duniya ba, amma kuma ba ta musamman ga Nijeriya ba.
“Alal misali, a Amurka, babu wani haramci gaba daya, amma jami’ai a wasu hukumomi suna bukatar samun izinin tsaro kafin su auri bako. Duk da cewa ba a haramta gaba daya ba, ana bukatar bincike kan abokin aure da aka nufa.”
“A Birtaniya, ba sa haramta aure da bakon wata kasa, amma damar jami’in samun bayanai masu muhimmanci ana takaita ta har sai an kammala bincike kan abokin aure. Sin, Rasha, da wasu kasashe a Gabas ta Tsakiya da Afirka suna haramta shi a fili. Indiya da Pakistan kuma suna bukatar amincewa kafin aure,” in ji shi.
“Watakila, idan aka duba abin da ke faruwa a sauran sassan duniya, ina ganin za mu iya sake duba wannan doka don gabatar da hanyoyin bincike kafin a yi irin wannan aure maimakon haramtawa gaba daya.
An kafa wannan doka ne a lokacin mulkin soja; sabbin jami’ai na iya ganin irin wadannan sharuda a matsayin tauye hakkokinsu. Ina ganin wannan wani fanni ne da rundunar za ta iya dubawa, ganin abin da ke faruwa a sauran kasashe,” in ji shi.
Binciken da aka gudanar ta Inatanet ya nuna cewa a rundunar sojin Amurka, jami’ai suna da ikon yin aure da ‘yan kasashen waje, amma dole ne su sami takardar izinin tsaro.
Ana bukatar su sanar da hukumarsu game da dangantakar auren, kuma ana la’akari da wannan aure a yayin yanke shawara kan batun izinin tsaro.
Da yake mayar da martani kan dokar da ke hana sojojin Nijeriya yin aure da ‘yan kasashen waje, Daraktan Cibiyar Albarkatun Dan’Adam da Ilimin Jama’a (CHRICED), Dokta Zikirullahi Ibrahim, ya soki wannan doka.
Ya ce irin wannan ka’ida ya kamata ta shafi mutanen da ke da manyan mukamai kawai, kamar Shugabannin Rundunoni wadanda ke da damar shiga bayanai masu mahimmanci, ba duk wanda ke cikin rundunar soja ba.
A cewarsa, “Idan aka ce ‘yan rundunar soja ba za su yi aure da ‘yan kasashen waje ba, me ya sa za a ware su daga sauran jami’an gwamnati? Ina tambaya, yaya game da ‘yan Nijeriya a cikin rundunar soja da suka mayar da iyalansu kasashen waje?
“Iyalansu da yawa daga bisani suna samun zama ‘yan kasa a wadannan kasashe. Mun ga misalai da dama. Mafi yawan manyan hafsoshin mu na soja, iyalansu suna da fasfot biyu, na Nijeriya da na wata kasa. To me muke yi game da wannan lamari?”
Ya kara tambayar dalilin da ya sa irin wannan doka ba ta shafi ‘yan siyasa ba.
Ya ce, “Yaya game da ‘yan siyasa? Da dama daga cikinsu suna da fasfot biyu (dual citizenship). To me ya sa sai sojoji ne kawai ake warewa? Ashe ba ‘yan kasa ba ne su ma?
“Idan har muna son tsaftace tsarin gwamnati, babu wani reshe na gwamnati da ya kamata a ware shi. Ba za ka yi doka ga rukuni daya, sannan ka yi wata doka daban ga wani rukuni ba.
“Ya kamata a samu daidaito wajen kirkirar manufofi, domin a karshe ba za ka kirkiri doka da ba za a iya aiwatar da ita ba, wacce kuma ba za ta yi tasiri ba.”
Ya jaddada cewa irin wannan takurawa ya kamata ta shafi mutanen da ke neman mukamai na jagoranci kawai.
A cewarsa, wadanda ake tunanin za a nada su a matsayin shugabannin runduna ne kadai ya dace a hana su yin aure da ‘yan kasashen waje.
Ya kara da cewa, “Soyayya da kauna ba su kamata su kasance karkashin dokokin dan’Adam ba.”
Ya ce, “Dangantakar soyayya aiki ne na Allah. Za mu iya samun doka gaba daya wadda za ta ce wasu mukamai ba za a bari su rika mutane masu fasfot biyu, ko ‘ya’ya, ko mata ko miji masu fasfot biyu ba. Wannan zai sa mutane su zama masu hankali, su kuma fahimci al’amuran kasa, domin za su san cewa ‘idan na kasance da wannan, akwai iyaka a ci gaban aikina.’”
Sai dai Daraktan CISLAC (Cibil Society Legislatibe Adbocacy Centre), Auwal Rafsanjani, ya nuna goyon bayansa ga takaita aure ga jami’an soja masu aiki.
A cewarsa, mutanen da ke irin wadannan mukamai suna da bayanai masu mahimmanci na kasa, don haka ya kamata su yi la’akari da muradun kasa wajen zabar abokan aure.
Ya ce, “A ganina, idan kana rike da mukamin tsaro mai matukar muhimmanci, lallai zai zama hadari ka yi aure ko ka rike dangantaka da mutum daga wata kasa daban, wanda watakila zai iya fallasa irin wadannan bayanai.”
Ya ce, “Don haka idan ka yanke shawarar zama jami’in tsaro, to ka riga ka san sakamakon hakan. Ban yi imani cewa irin wadannan mutane ya kamata su rike dangantaka wadda za ta iya fallasa bayananmu masu mahimmanci ba.
“Idan ka yanke shawarar zama jami’in tsaro, tun kafin ka shiga aikin, ka riga ka san irin sadaukarwa da gata da ke tattare da ita.
Saboda haka, a ganina, tun daga farko, ya kamata mutane su san wadannan abubuwa. Sun riga sun san akwai wasu bayanai da dole su kasance a boye saboda tsaron kasa.”
ShareTweetSendShare MASU ALAKA