“Baya ga tsarin Daidaiton Jinsi, muna kuma ƙaddamar da Dokar Kare Al’umma a jihar Zamfara. Waɗannan matakai suna da muhimmanci don tabbatar da cewa tsarin zamantakewarmu yana da ƙarfi kuma ya dace da buƙatun mutanenmu, musamman ma masu rauni.

“Dokar kare haƙƙin yara da dabarun aiwatar da ita sun ƙarfafa ƙudurinmu na kare haƙƙin yara da walwalarsu.

A matsayinsu na ginshiƙin makomarmu, dole ne mu tabbatar da cewa yara suna cikin aminci da kulawa don cimma burinsu.

“Dokar nakasassu ta jihar Zamfara ta nuna ƙudurinmu na kare haƙƙin nakasassu. Wannan na neman kawar da wariya da haɓaka damar shigarsu cikin al’umma. Mun haɗa da manyan masu ruwa da tsaki, ciki har da nakasassu, don tabbatar da jin muryoyinsu.

“Saboda haka, za a sake duba dokar don ƙara haɗa kai, kuma za a kafa kwamitin da zai magance takamaiman buƙatun nakasassu.”

Gwamna Lawal ya ƙara jaddada cewa gwamnatinsa ta tsinci fannin kiwon lafiya a cikin wani mawuyancin hali a jihar.

“Don cimma burinmu na samar ingantacciyar kiwon lafiya kuma mai araha daidai da tsarin duniya, mun ayyana dokar ta-baci a bangaren kiwon lafiya.

“Misali, ta hanyar Hukumar Raya Al’umma da Ci Gaban Jama’a (CSDA), gwamnatin jihar ta gyara cibiyoyin kiwon lafiya 61, ciki har da manyan asibitoci 10, sannan ta shiga tsakani a wasu cibiyoyin kiwon lafiya na matakin farko guda 51.

“Tare da tallafin gwamnatin jiha kai tsaye, mun gyara tare da inganta asibitin ƙwararru na Yariman Bakura da manyan asibitocin Talata Mafara da Shinkafi, inda muka mayar da su Manyan Asibitocin Ƙwararru na yankin.

“Mun kuma fara gina cibiyar VVF don kula da matsalolin mata masu juna biyu tare da amincewa da gina cibiyar gwaje-gwaje a matsayin wani bangare na ƙudurinmu na samar da ingantaccen kiwon lafiya.

“Ƙoƙarin da muke yi, tare da goyon bayan dukkan abokan hulɗarmu, ya riga ya fara samar da sakamako mai kyau a dukkan tubalan gina tsarin kiwon lafiya.

“Mun yi nasarar dakatar da yaɗuwar cutar shan inna a jihar Zamfara, kuma mun samu raguwar bullar cututtukan da za a iya magance su ta hanyar rigakafi, kamar su kyanda, sankarau, da zazzabin rawaya. A shekarar 2024, jiharmu ta samu bullar cutar Diphtheria guda biyu kacal duk da barkewar annobar a jihohin makwabta.

“Mun kuma ba da gudunmawa sosai wajen gyara Kwalejin Koyon Aikin Jinya da Ungozoma da ke Gusau da kuma gyara Kwalejin Kimiyya da Fasaha ta Lafiya da ke Tsafe.

Gwamnan ya yaba da haɗin gwiwar UNICEF da jihar, kuma ayyukan sun yi matuƙar tasiri.

“A kan tasirin da GAVI ya yi a jiharmu, muna godiya musamman da yadda ku ka haɗa cibiyoyin kiwon lafiya 50 na mu da na’urorin wutar lantarki masu amfani da hasken rana, wanda ke ba su damar samar da ayyuka na sa’o’i 24 cikin inganci.”

“Wannan aikin yana haɓaka ƙarfinmu don adanawa da rarraba alluran rigakafin zuwa wurare daban-daban. Zuba jarin ku a rijiyoyin burtsatse masu amfani da hasken rana da ban-ɗakuna a cibiyoyin kiwon lafiya 29 yana inganta jin daɗin ma’aikata da marasa lafiya, yana kuma ƙarfafa alaƙar al’umma ga wuraren kiwon lafiya.

“Muna godiya da goyon bayanku na shigar da mata da yara marasa galihu 33,000 cikin tsarin inshorar lafiya na jihar. Wannan aikin yana ɗaya daga cikin ayyuka mafi tasiri da aka taba yi, kuma mun sadaukar da kai don ci gaba da samun nasarori.”

A farko, Cristian Munduate, wakilin UNICEF a Nijeriya, ya ce wannan ne karo na farko a duniya da GAVI ta yanke shawarar tallafa wa tsarin kiwon lafiya na ƙasa da ƙasa. “Mun yi farin ciki saboda an ga sakamako mai kyau a Zamfara, kuma wannan zai sa GAVI ta ci gaba da tallafa wa ayyukan kiwon lafiya a irin wannan matakin ba kawai a cikin ayyukan ƙasa ba.”

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC

Gwamnan Jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya ƙaryata jita-jitar da ke yawo a kafafen sada zumunta cewa zai bar jam’iyyar APC zuwa ADC tare da wasu gwamnoni biyar.

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Dauda Iliya, ya fitar, Zulum ya ce wannan labari ƙarya ne, kuma wasu ne kawai ke ƙirƙirarsa domin cimma wata manufa ta ƙashin kansu.

Gwamna ya gargaɗi sarakuna kan mamaye filayen kiwo a Gombe Majalisar Dattawa ta gindaya sharaɗin dawo da Sanata Natasha

Ya ce yana nan daram a jam’iyyar APC kuma yana biyayya ga jam’iyyar a matakin jiha da ƙasa baki ɗaya.

Sanarwar ta ce, “Mun ji wani labari da ake yaɗawa cewa zan koma jam’iyyar ADC tare da wasu gwamnoni biyar.

“Wannan labari ba gaskiya ba ne. Waɗanda suka ƙirƙira shi ba sa kishin ƙasa kuma ba sa taimaka wa Jihar Borno ko Nijeriya.”

Zulum ya ƙara da cewa yana nan daram a APC, domin ya damu da ci gaban Jihar Borno.

“Ina roƙon jama’ar Borno da su yi watsi da wannan jita-jita. Mu ba mu da lokacin siyasar da ba ta da amfani. Muna da aiki a gabanmu na ci gaban jiharmu,” in ji shi.

Ya kuma roƙi kafafen yaɗa labarai da su tabbatar da sahihancin labarai kafin su yaɗa su.

Hakazalika, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da aiki tuƙuru a ƙarƙashin jam’iyyar APC domin ciyar da jihar gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Yobe
  • An ƙaddamar da tsarin inshorar lafiya na mutum 38,000 a Gombe
  • Gwamna Peter Mbah Ya Ƙaddamar Da Jiragen Kasuwanci 3 Na ‘Enugu Air’ Mallakin Jihar
  • Kira ga Haƙuri: A Dakatar da Ƙirƙirar Sabbin Masarautu a Jihar Bauchi
  • Fursunoni 58 Na Rubuta Jarabawar NECO A Kano
  • Sojoji Da Masu Gadin Gandun Daji Zasu Murkushe Masu Aikata Laifuka A Kwara
  • China Ta Maida Martani da Haka Kayakin Kiwon Lafiya Na Tarayyar Turai Shigowa Kasar
  • Zulum ya musanta shirin ficewa daga APC
  •  Na’im Kassim: Kare Kasa Ba Ya Da Bukatuwa Da Izinin Kowa
  • Shirin Tinubu Kan Kiwon Dabbobi Zai Samar Da Ayyukan Yi Miliyan 5 Ga Matasa – Jega