HausaTv:
2025-07-31@12:38:10 GMT

Syria: Adadin Wadanda Aka Kashe A Rikicin Bangaranci Sun Kai 70

Published: 1st, May 2025 GMT

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Syria ta nuna kin amincewarta da tsoma bakin kasashen waje a rikicin da kasar take fuskanta.

Sanarwar ma’aikatar harkokin wajen kasar ta Syria ta kuma ce; gwamnatin kasar za ta kare dukkanin ‘yan kasar.

Kasar Syria tana fuskantar fada a tsakanin ‘yan Duruz da kuma sojojin gwamnatin kasar a yankin Sahanaya da Ashrafiyyah a yankin Suwaida.

Ya zuwa yanzu dai adadin wadanda su ka rasa rayukansu sun kai 70.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021

Da safiyar yau Litinin ofishin yada labarai na majalisar gudanarwar kasar Sin ya gudanar da taron manema labarai, bisa taken “Cimma burikan da aka tsara domin neman bunkasa tattalin arziki da zaman takewar al’umma a tsakanin shekarar 2021 zuwa shekarar 2025”.

A yayin taron, jami’in babbar hukumar buga haraji ta kasar Sin ya bayyana cewa, tun daga shekarar 2021 ya zuwa yanzu, tattalin arzikin kasar Sin ya bunkasa bisa shirin da aka tsara, kana, bisa hasashen da aka yi. Sakamakon haka, jimillar haraji da kudaden da hukumomin buga haraji sun karba ta zarce kudin Sin Yuan tiriliyan 155, adadin da ya kai kaso 80 bisa dari na yawan kudaden shiga na kasar Sin. Cikin adadin, kudin haraji zai kai sama da Yuan tiriliyan 85, adadin da ya karu da Yuan tiriliyan 13, idan aka kwatanta da adadin kudin haraji da aka samu a tsakanin shekarar 2015 zuwa shekarar 2020. Lamarin da ya ba da tabbaci ga bunkasar tattalin arziki da zaman takewar al’umma.

A sa’i daya kuma, jami’in ya ce, tun daga shekarar 2021, ya zuwa yanzu, jerin manufofin da aka samar a fannin rage haraji, da kudaden da hukumomin buga haraji suka karba, ya nuna goyon baya ga aikin raya tattalin arziki da kyautata zaman takewar al’umma. Hasashen da aka yi ya kuma nuna cewa, tsakanin shekarar 2021 da ta 2025, yawan haraji da kudaden da hukumomin buga haraji suka rage, ya kai kudin Sin Yuan tiriliyan 10.5, kana, yawan harajin da aka mayar kan kayayyakin fitarwa ya kai Yuan tiriliyan 9. (Mai Fassara: Maryam Yang)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Ta Yi Allah Wadai Da Takunkumin Da Amurka Ta Kakaba Mata
  • Ma’aikatar Bunƙasa Harkar Kiwo Za Ta Taimaka Wajen Magance Rikicin Manoma Da Makiyaya — Jega
  • Adadin Falasdinawan da Isra’ila take kashewa a Gaza yanzu ya haura 60,000
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
  • Ma’aikatar Leken Asirin JMI Ta Ce Ta Gano Shirin Kashe Manyan Mutane 35 a kasar
  •  Kasar Holland Ta Hana MInistocin HKI Biyu Shiga Cikin Kasarta
  • Mutanen Sweida Na Kasar Siriya Suna Fama da Rashin Abinci da Ruwa
  • Sin Za Ta Ba Da Tallafin Kula Da Yara A Fadin Kasar
  • Ana Ci Gaba Da Habaka Karfin Kudin Kasar Sin Tun Daga Shekarar 2021