Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
Published: 29th, April 2025 GMT
Wasu abubuwan fashewa da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram ne suka dasa, sun kashe kimanin mutane 26, ciki har da mata da ƙananan yara a kusa da garin Rann da ke Ƙaramar Hukumar Kala Balge ta Jihar Borno.
Majiyoyin tsaro da na cikin gari sun bayyana cewa mutane da dama sun jikkata bayan da motar da ke ɗauke da wadanda abin ya shafa zuwa Gambarou Ngala ta taka abin fashewar.
Wata majiya ta ce, “Ba a tantance adadin mutanen da suka mutu ba, amma rahotanni na farko sun nuna cewa mata huɗu da yara shida da maza 16 ne suka mutu a wannan fashewar.”
Ta ci gaba da cewa lamarin ya faru ne a kan hanyar Furunduma, kimanin kilomita 11 daga garin Rann, da misalin karfe 11 na safe a ranar Litinin.
Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin NajeriyaTa ƙara da cewa an kai wasu da suka jikkata asibitin Rann domin kula da su.
Babu wata sanarwa a hukumance daga bangaren sojoji ko ’yan sanda game da faruwar lamarin.
Sai dai kuma, kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Borno, Kenneth Daso, bai yiwu ba saboda layin wayarsa ba ya shiga.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Abubuwan Fashewa Boko Haram mata da ƙananan yara Rann Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
’Yan bindiga sun kashe mutum 3 sun sace 64 a Zamfara
’Yan bindiga sun kashe mutum 3 tare da yin garkuwa da wasu 64 a ranar Asabar a Karamar Hukumar Tsafe ya Jihar Zamfara.
Cikin waɗanda ’yan ta’addan suka kashe har da wani jigon jam’iyyar APC, Hon. Umaru Moriki wanda aka bindige a kan hanyar Gusau zuwa Tsafe, waɗanda aka yi garkuwa da su kuma har da mata da ƙananan yara a kauyen Fegin Baza.
Harin ta faru ne washegarin da Ministan Tsaro, Bello Matawalle ya ziyarci jihar, inda ya sanar cewa Hedikwata Tsaro ta girke ƙarin jami’an tsaro a jihar.
A yayin ziyarar ministan ya bayyana cewa zai gana da jami’an tsaro inda zai ba su umarni kar su raha wa ’yan ta’adda.
NAJERIYA A YAU: Matsayar Doka Kan Taron Da Jam’iyyar PDP Ta Gudanar Da amincewar hukumomi nake tattaunawa da ’yan bindiga — Sheikh GumiMinistan ya kuma zargi gwamnatin jihar kan abin da yake yi da kuɗaɗen da take samu daga Gwamnatin Tarayya.
Jihar, wadda ita ce mahaifar Matawalle, tana fama da matsalar hare-haren ’yan bindiga da suka hana ayyukan noma da sauran harkokin tattalin arziki.
Hare-haren bayan nan, kari ne a kan wasu da dama da suka addabi jihar, duk da ayyukan soji da dama domin daƙile matsalar.
Yadda abin ya faruRahotanni sun ce ’yan bindiga kusan 30 ne suka buɗe wuta kan motar Hon. Moriki yayin da yake kan hanyarsa zuwa Kaduna, inda suka kashe shi nan take.
Bayan haka, sun yi garkuwa da mazauna kauyen 64, suka tafi da su zuwa wani wurin da ba a sani ba.
Hon. Moriki, wanda ya taɓa tsayawa takarar kujerar Majalisar wakilai a Mazaɓar Zurmi/Shinkafi, shi ne Sarkin Fada na Moriki a halin yanzu.
Ɗan marigayin, Abubakar Umar Moriki, ɗalibi a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK) ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya ce: “Baba ya yi ƙoƙarin yin u-turn bayan ya lura da ’yan bindiga, amma suka buɗe masa wuta. An harbe shi, ya rasu nan take. An yi masa jana’iza bisa tsarin Musulunci. Allah Ya gafarta masa, ya kuma sanya shi da Aljanna Firdaus.”
An gudanar da sallar jana’izar marigayi a Masallacin Juma’a na Federal Low-cost, Tudun Wada da ke Gusau, ƙarƙashin jagorancin Imam Alƙali Abdullahi Yakubu.
Ministan Tsaron Ƙasa, Alhaji Bello Mohammed Matawalle, ya halarci jana’izar tare da yin ta’aziyya ga iyalan marigayin.
Matawalle ya bayyana rasuwar Hon. Moriki a matsayin babban rashi ga jihar da ƙasa baki ɗaya, la’akari da ayyukan alheri da ya yi wa jama’a, musamman maƙwabta da ’yan uwa.
A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun APC na jihar, Yusuf Idris, ya fitar, Matawalle ya yi addu’ar Allah Ya saka masa da Aljanna Firdaus, ya kuma ba iyalansa ƙarfin zuciya wajen jure wannan rashi.
Ministan ya bayar da gudummawar Naira miliyan 10, buhunan shinkafa 50, buhunan masara 25 da buhunan gero 25 ga iyalan marigayin, tare da tabbatar musu da kulawa daga gwamnati.
A madadin iyalan marigayin, Ambassador Abubakar Hussaini Moriki ya gode wa ministan bisa kulawa da tausayi da ya nuna.
Ya ce sun san cewa ministan ya soke dukkan ayyukansa na yau domin halartar jana’izar, ya kuma yi tafiya daga garin Maradun zuwa Gusau don yin ta’aziyya da su a wannan lokaci na jarrabawa.