Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno
Published: 29th, April 2025 GMT
Wasu abubuwan fashewa da ake zargin ’yan ta’addan Boko Haram ne suka dasa, sun kashe kimanin mutane 26, ciki har da mata da ƙananan yara a kusa da garin Rann da ke Ƙaramar Hukumar Kala Balge ta Jihar Borno.
Majiyoyin tsaro da na cikin gari sun bayyana cewa mutane da dama sun jikkata bayan da motar da ke ɗauke da wadanda abin ya shafa zuwa Gambarou Ngala ta taka abin fashewar.
Wata majiya ta ce, “Ba a tantance adadin mutanen da suka mutu ba, amma rahotanni na farko sun nuna cewa mata huɗu da yara shida da maza 16 ne suka mutu a wannan fashewar.”
Ta ci gaba da cewa lamarin ya faru ne a kan hanyar Furunduma, kimanin kilomita 11 daga garin Rann, da misalin karfe 11 na safe a ranar Litinin.
Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin NajeriyaTa ƙara da cewa an kai wasu da suka jikkata asibitin Rann domin kula da su.
Babu wata sanarwa a hukumance daga bangaren sojoji ko ’yan sanda game da faruwar lamarin.
Sai dai kuma, kokarin jin ta bakin kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Borno, Kenneth Daso, bai yiwu ba saboda layin wayarsa ba ya shiga.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Abubuwan Fashewa Boko Haram mata da ƙananan yara Rann Tsaro
এছাড়াও পড়ুন:
Yadda Iran ta yi jana’izar kwamandojinta Isra’ila ta kashe
Iran ta gudanar da gagarumin jana’izar tare da karramawq ga kwamandojinta da masana kimiyyar nukiliya da wasu ’yan kasar da Isra’ila ta kashe a yankin kwana 12 da aka gwabza a tsakanin ƙasashen.
Iran ta shirya gagarumin jana’izar a ƙwaryar birnin Tehran kwana huɗu bayan Isra’ila ta amince da yarjejeniyar tsagaita wuta a yaƙin da ɓangarorin biyu ke iƙirarin nasara a yaƙin da aka fara ranar 13 ga Yuni, 2025.
A safiyar Asabar daruruwan dubban mutane ne suka fito ɗauke da tutocin ƙasar suna wake-waken jinjina domin karrama kwamandojin da suka kwanta dama a wurin jana’izar.
Mutanen sun kuma riƙa daga hotunan mamatan a matsayin waɗanda suka yi mutuwar shahada, a yayin da suke la’antar Isra’ila da Amurka.
Daga cikin kwamandojin da Isra’ila ta kashen har da jagoran Rundunar Juyin Juya Halin Musulunci na Iran Janar Hossein Salami da Janar Amir Ali Hajizadeh da wani ƙwararren masanin kimiyyar makamashin nukiliya, Mohammad Mehdi Tehranchi.
Za a iya tuna cewa Amurka ta kai wa cibiyoyin nukiliyar Iran hare-hare a ƙarshen makon da ya gabata, kafin daga bisani a tsagaita wuta.
Amurka da Isra’ila sun yi iƙirarin cewa hare-haren sun yi gagarumar nasarar ruguza shirin kera makaman nukiliya na Iran.
Amma daga bisani Iran ta ƙaryata su, da cewa babu wata illa da hare-haren suka yi wa shirinta da makamashin nukiliya.
A ranar Talata Shugaban addini na Iran, Ayatollah Ali Khamenei ya karyata abin da ya kira kambama harin da shugaban kasar Amurka, Donald Trump ya yi na cewa harin hare-haren sun mayar da shirin nukiliyar Iran baya da shekaru.
An kashe manyan sojojin da masa kimiyyar nukiliyar Iran ne a harin da Isra’ila ta fara kaiwa bisa hujjar neman daƙile shirin Iran na mallakar makamin nukiliya.