Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa
Published: 29th, April 2025 GMT
Wata koutun soja ta yanke wa wani jami’inta hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samun sa da laifn kashe buduwarsa.
Kotun da ta zauna a Hedikwatar Runduna ta 82 da ke Enugu, ta yanke wa Private Adamu Mohammed hukuncin kisa kan laifin budurwar taas mai suna Hauwa Ali.
Da yake sanar da hukuncin, Shugaban kotun, Birgediya Sadisu Buhari, ya ce, “Kotun Soja ta Kasa ta yanke hukuncin cewa sojan da ake tuhuma, mai lamba 21NA/80/6365 Private Adamu Mohammed, an yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa tuhumar kisan kai.
Mukaddashin kakakin Rundunar, Jonah Unuakhalu, ya ce kwamitin kotun ya cimma matsaya ɗaya bayan nazari mai zurfi na shaidu, tarihin aikin wanda ake tuhuma, da kuma roƙon sassauci daga lauyansa.
Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a BornoYa shaida wa manema labarai a Abuja cewa kotun sojan, ta kuma yanke wa wani Soja mai suna Private Abubakar Yusuf hukuncin ɗaurin shekaru 10 a kurkuku saboda samun sa da laifin fashi da makami a wani shahararren kantin sayayya a Enugu.
Ya kara da cewa an yanke wa waɗannan mutane biyu hukuncin ne bayan kammala shari’o’insu kan laifukan kisan kai da fashi da makami.
Babban Kwamandan Runduna ta 82, Manjo-Janar Oluyemi Olatoye, ne ya kaddamar da kotun sojin a ranar 18 ga Fabrairu, 2025, domin yanke hukunci kan shari’o’in da suka shafi ma’aikatan da suka yi kuskure a cikin Rundunar.
A cewarsa, waɗannan hukunce-hukuncen sai sun samu tabbatarwa daga hukumomin soji da suka dace, wanda ya nuna ƙarshen shari’o’in sojojin.
Ya sake jaddada ƙudurin Sojojin Najeriya na tabbatar da ɗa’a da kuma kiyaye mafi girman ƙa’idoji na ɗabi’u da ƙwarewa.
“Kuskuren ayyukan wasu kaɗan ba su nuna ƙimar ƙungiyar ba. A koyaushe ana ɗaukar matakai masu sauri da kuma ƙarfi don tabbatar da riƙon amana da adalci,” in ji shi.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: budurwa
এছাড়াও পড়ুন:
Amurka ta matsa lamba a kan kotun ICC don janye bincike kan yakin Gaza da Afghanistan: Reuters
Gwamnatin shugaban Amurka Donald Trump ta bukaci kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa (ICC) ta yi gyara ga yarjejeniyar da aka kafa domin kare Trump da manyan jami’an Amurka daga duk wani bincike na yanzu ko nan gaba, in ji wani jami’in gwamnatin Trump a ranar Laraba. Barazanar dai na kunshe ne da gargadin kara sanya takunkumi idan kotun ta ki bin umarnin.
Kamfanin dillancin labaran reuters ya bayar da rahoton cewa, wa’adin na Washington ya hada da karin wasu bukatu guda biyu: cewa kotun ta ICC ta janye bincikenta kan laifukan yaki da shugabannin Isra’ila suka aikata a lokacin yakin Gaza, da kuma cewa ta rufe binciken da ta yi tun farko kan halin sojan Amurka a Afghanistan. Idan kotu ta ki yin aiki, gwamnatin Amurka na iya sanya sabbin takunkumi kan daidaikun jami’an ICC.
Matsayin gwamnatin Trump na baya-bayan nan ya ginu ne kan takun saka a baya da hukumomin kasa da kasa. Kotun hukunta manyan laifuka ta ICC da ke birnin Hague, ta fuskanci matsin lamba daga Washington tun bayan da ta bude bincike kan ayyukan sojan Amurka a lokacin yakin Afghanistan da kuma a baya-bayan nan, kan matakin da “Isra’ila” ta dauka a zirin Gaza.
Jami’an Trump sun bayyana irin wannan binciken a matsayin na siyasa da kuma cin zarafi ga ikon kasa, kamar dai yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ghana ta yi Allah wadai da cin mutuncin ‘yan kasarta da ke balaguro a Isra’ila December 11, 2025 Sakamkon Jin Ra’ayi: Yawancin Amurkawa na adawa da kai hari kan Venezuela December 11, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Kasashen Nijeriya Da Saudiyya Sun Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Tsaro Ta Shekaru 5 December 10, 2025 Shugaban Kasar Iran Yace Mata Su ne Ginshin Gina Makomakar Kowacce Kasa December 10, 2025 Iran Ta yi Tir Da Kisan Karen Dangin Isra’ila A Gaza A Ranar Yaki Da Kisan Kiyashi Ta MDD December 10, 2025 Borkina Faso Ta Saki Sojojin Sama Na Najeriya 11 Da ta Kama Bayan Jirginsu Yayi Saukar Gaggawa. December 10, 2025 Hamas Ta yi Tir Da Sabbin Matsugunan Yahudawa Da Isra’ila Ke yi A Yankunan Da Ta Mamaye December 10, 2025 Iran Tana Daukar Bakwancin Taron BRICS Na Binciken Kimiya Da Kuma Ci Gaban Ilmi December 10, 2025 Nasarar Da Iran Ta Samu A Yakin Kwanaki 12 Kan HKI Yana Jawo Hankalin Kasashen Duniya December 10, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci