Aminiya:
2025-12-14@16:32:51 GMT

Za a rataye wani soja saboda laifin kashe budurwarsa

Published: 29th, April 2025 GMT

Wata koutun soja ta yanke wa wani jami’inta hukuncin kisa ta hanyar rataya bayan samun sa da laifn kashe buduwarsa.

Kotun da ta zauna a Hedikwatar Runduna ta 82 da ke Enugu, ta yanke wa Private Adamu Mohammed hukuncin kisa kan laifin budurwar taas mai suna Hauwa Ali.

Da yake sanar da hukuncin, Shugaban kotun, Birgediya Sadisu Buhari, ya ce, “Kotun Soja ta Kasa ta yanke hukuncin cewa sojan da ake tuhuma, mai lamba 21NA/80/6365 Private Adamu Mohammed, an yanke masa hukuncin kisa ta hanyar rataya bisa tuhumar kisan kai.

Mukaddashin kakakin Rundunar, Jonah Unuakhalu, ya ce kwamitin kotun  ya cimma matsaya ɗaya bayan nazari mai zurfi na shaidu, tarihin aikin wanda ake tuhuma, da kuma roƙon sassauci daga lauyansa.

Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok Kano: Galadima biyu a masarauta ɗaya Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno

Ya shaida wa manema labarai a Abuja cewa kotun sojan, ta kuma yanke wa wani Soja mai suna Private Abubakar Yusuf hukuncin ɗaurin shekaru 10 a kurkuku saboda samun sa da laifin fashi da makami a wani shahararren kantin sayayya a Enugu.

Ya kara da cewa an yanke wa waɗannan mutane biyu hukuncin ne bayan kammala shari’o’insu kan laifukan kisan kai da fashi da makami.

Babban Kwamandan Runduna ta 82, Manjo-Janar Oluyemi Olatoye, ne ya kaddamar da kotun sojin a ranar 18 ga Fabrairu, 2025, domin yanke hukunci kan shari’o’in da suka shafi ma’aikatan da suka yi kuskure a cikin Rundunar.

A cewarsa, waɗannan hukunce-hukuncen sai sun samu tabbatarwa daga hukumomin soji da suka dace, wanda ya nuna ƙarshen shari’o’in sojojin.

Ya sake jaddada ƙudurin Sojojin Najeriya na tabbatar da ɗa’a da kuma kiyaye mafi girman ƙa’idoji na ɗabi’u da ƙwarewa.

“Kuskuren ayyukan wasu kaɗan ba su nuna ƙimar ƙungiyar ba. A koyaushe ana ɗaukar matakai masu sauri da kuma ƙarfi don tabbatar da riƙon amana da adalci,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: budurwa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno

Dakarun Sojin Rundunar Operation Haɗin Kai, sun kashe ’yan ta’adda biyu a wani samame da suka kai yankin Shettimari da ke Ƙaramar Hukumar Konduga, a Jihar Borno.

Majiyoyi sun shaida cewa rundunar ta kai harin ne ƙarƙashin Operation Desert Sanity V da safiyar ranar Alhamis.

Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na Turkiyya Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai

Wata majiyar soji ta ce, “Sojojin sun tare mayaƙan a kusa da inda suka ke shirin kai hari a yankin da misalin ƙarfe 1:20 na dare.”

Ya ƙara da cewa, “Sojojin sun yi nasarar daƙile ’yan ta’addan nan take, inda suka kashe biyu daga cikinsu yayin da wasu suka tsere.”

Bugu da ƙari, majiyar ta ce daga baya an gano wasu bama-bamai guda biyu da kuma wani gidan harsashi guda ɗaya mai ɗauke da harsasai 23 masu ɗangon 7.62mm x 39mm da ’yan ta’addan suka watsar yayin tserewa.

Majiyar ta ƙara da cewa, “Babu wanda ya mutu a cikin sojojin, sai dai daga baya tawagar sojojin sun ci gaba da aikinsu.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kashe mutum 11 da jikkata wasu 29 a bikin Yahudawa a Ostireliya 
  • Isra’ilaTa Kashe Wani Bafalasdine Matashi A Wani Hari Da Takai A Arewacin Kogin Jodan.
  • Buɗe cibiyar horas da sabbin sojoji a Kudu zai taimaka — Janar Shaibu
  • Dan bindiga ya kashe sojojin Amurka biyu da wani farar hula a Siriya
  • Kotu ta sa ranar yanke hukunci a Shari’ar Abba Kyari da NDLEA
  • Birtaniya Ta yi  Barazanar Yanke Gudunmawar Da Take Bawa Kotun Duniya
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Hukuncin Kisa Kan Maryam Sanda
  • Kotun Koli ta soke afuwar da Tinubu ya yi wa Maryam Sanda
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano