Falasdinu: Mahmud Abbas Ya Nada Magaji Da Kuma Mataimakasa
Published: 28th, April 2025 GMT
Shugaban Palasdinu da kuma kungiyar kwatar yencin falasdinawa PLO Mahmud Abbas ya nada magajinsa da kuma wasu mataimaka.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran, ta bayyana cewa Abbas dan shekara 89 ya nada mataimakinsa ne bayan taron majalisar gudanarwa ta gwamnatinsa a makon da ya gabata.
Labarin ya kara da cewa kasashen yamma da yankin sun dade suna takurawa Abbas kan ya nada mataimaki da kuma wasu mataimaka sabuda rawar da gwamnatinsa zata taka bayan yakin gaza.
A yau ne majalisar zartarwa ta amince da nada Hussein Al Sheikh a matsayin mataimakin shugaban majalisar da kuma mataimakin shugaban kasa a lokaci guda.
Kamfanin dillancin labarai na gwamnatin Falasdinawan WAFA, ya bayyana cewa gwamnatin Abbas ce da hakkin sa hannu a kan yarjeniyoyi da suka shafi Falasdinu, a madadin dukkan kungiyoyin Falasdinawa, banda wadanda su ka dauke da makamai suna yakar HKI, wato Hamas da kuma Jihadul Islami a Gaza.
Mr Al Sheikh, dan shekara 64 a duniya na hannun daman Abbas ne a kungiyarsa ta fatah.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Salami: Babu Inda Ba Za Mu Iya Kai Wa Hari Ba A Fadin HKI
Kwamandan dakarun kare juyin juya halin musulunci na Iran Manjo Janar Hussain Salami ya fada a yau Alhamis cewa; Abokan gaba suna yi mana barazana da yaki, sannan ya tabbatar da cewa a shirye suke su fuskanci duk abinda zai faru.
Manjo janar Salami wanda ya gabatar da jawabi ga taron dakarun sa-kai na “Basiji a nan Tehran ya kuma kara da cewa; Babu wani wuri komai zurfi da nisansa a HKI da ba mu tsinkayowa, idan kuwa aka ba mu umarni to za su yi nasara, mu Sanya abokin gaba ya yi nadama.
A gefe daya ministan tsaron Iran ya bayyana cewa; Duk wani hari da ake tunanin kawo wa Iran, to kuwa zai fuskanci mayar da martani mai tsanani.
Ministan tsaron na Iran Laftanar janar Azizi Nasri Zadeh ya kara da cewa; Idan har yaki ya barke, to za a tilasta wa Amruka ficewa daga wannan yankin, kuma asarar da za ta yi sai ta rubanya wacce za ta yi wa Iran.”
Ministan tsaron na Iran ya kuma ce; Abin takaici ne yadda wasu jami’an Amurka su ka yi barazanar yiyuwar barkewar yaki, idan ba a cimma matsaya ba a tattaunawar Nukiliya, sannan ya kara da cewa: Tehran ba ta maraba da yaki, amma kuma a lokaci daya ta shirya masa.”