Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Sansanin Nevatim Na Harahtacciyar Kasar Isra’ila Da Makami Mai Linzami
Published: 26th, April 2025 GMT
Sojojin Yemen sun kai hari kan sansanin Nevatim na haramtacciyar kasar Isra’ila da ke Negev da makami mai linzami
Dakarun Yemen sun sanar da aiwatar da wani farmakin soji kan sansanin sojojin saman Nevatim na haramtacciyar kasar Isra’ila da ke yankin Negev a kudancin Falasdinu da aka mamaye.
Rundunar sojin kasar Yemen ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Asabar cewa: Rundunarta ta kai wani harin soji kan sansanin sojin saman Nevatim da ke yankin Negev da makami mai linzami na kirar “Falestine 2”.
Majiyar ta kara da cewa: Makami mai linzamin ya kai ga inda aka saita, kuma na’urorin kariya na haramtacciyar kasar Isra’ila sun kasa kakkaboshi. Ta yi nuni da cewa: Wannan farmakin wata nasara ce ga al’ummar Falastinu da ake zalunta da mayakansu, da kuma yin watsi da kisan kiyashin da makiya yahudawan sahayoniyya suke yi kan ‘yan uwan al’ummar Yemen a Zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
A ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da HKI ke yi a kasar labanon a jiya ma ta kai hari a kudancin kasar kuma ta yi sanadiyar mutuwar mauta 4 tare da jikkata wasu guda 3,
Isra’ila ta kai hari da jirgin sama mara matuki kan wata mota a kauyen kafr rumman , kana kuma ta sake kai wani harin a garin kafr sir kamar yadda rahotanni suka bayyana, kuma wadannan hare haren suna zuwa ne kwanaki 3 bayan da sojojin israila suka kai samame ta kasa a kudancin labanon a yankin Nabatiya inda suka kai hari a jiya,
A ranar jumaa da ta gabata ne shugaban kasar ta labanon joseph Aun ya nuna damuwarsa game da ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da Isra’ila ke yi, inda yayi tir da tel aviv game da irin mataken da take dauka na karya yarjejeniyar.
A yan kwanankin nan sakatare janar din kungiyar hizbullah na kasar labanon shaikh Naim Qassem ya jaddada cewa tsayin daka ne karfin labanon, don haka Amurka na matsin lamba ne don ganin an danneta an tauye mata yanci da raunata ta don biyan muradun gwamnati.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Kamaru: Jagroan ‘Yan Hamayya Ya Yi Kira Da A Tsayar Da Harkoki A Fadin kasar November 1, 2025 MDD Tana Sa Ido Akan Kashe-kashen Da Ake Yi A Zaben Kasar Tanzania November 1, 2025 Gaza: Daga Tsagaita Wuta Zuwa Yanzu Fiye Da Mutane 200 Ne Su Ka Yi Shahada November 1, 2025 Shugaban Najeriya Ya Mayar Da Martani Ga Takwaransa Na Amurka Akan Rikicin Addini November 1, 2025 Iran ta damu da halin da ake ciki a yankin El Fasher na Sudan November 1, 2025 Kwamitin Tsaron MDD ya goyi bayan shirin Morocco game da yankin Yammacin Sahara November 1, 2025 Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya November 1, 2025 Najeriya ta musanta ikirarin Trump, na cewa Kristoci na fuskantar babbar barazana a kasar November 1, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci