Sojojin Yemen Sun Kai Hari Kan Sansanin Nevatim Na Harahtacciyar Kasar Isra’ila Da Makami Mai Linzami
Published: 26th, April 2025 GMT
Sojojin Yemen sun kai hari kan sansanin Nevatim na haramtacciyar kasar Isra’ila da ke Negev da makami mai linzami
Dakarun Yemen sun sanar da aiwatar da wani farmakin soji kan sansanin sojojin saman Nevatim na haramtacciyar kasar Isra’ila da ke yankin Negev a kudancin Falasdinu da aka mamaye.
Rundunar sojin kasar Yemen ta bayyana a cikin wata sanarwa da ta fitar a yau Asabar cewa: Rundunarta ta kai wani harin soji kan sansanin sojin saman Nevatim da ke yankin Negev da makami mai linzami na kirar “Falestine 2”.
Majiyar ta kara da cewa: Makami mai linzamin ya kai ga inda aka saita, kuma na’urorin kariya na haramtacciyar kasar Isra’ila sun kasa kakkaboshi. Ta yi nuni da cewa: Wannan farmakin wata nasara ce ga al’ummar Falastinu da ake zalunta da mayakansu, da kuma yin watsi da kisan kiyashin da makiya yahudawan sahayoniyya suke yi kan ‘yan uwan al’ummar Yemen a Zirin Gaza.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Isra ila
এছাড়াও পড়ুন:
Sojojin HKI Sun Ci Gaba Da Kashe Kawunansu
A cikin kwanakin bayan nan ana samun karuwar sojojin HKI da suke kashe kawunansu saboda tabuwar kwakwalensu sanadiyyar yakin Gaza.
Kafafen watsa labarun HKI sun kunshi rahotanni da suke bayani akan yadda sojojin mamayar da su ka yi yaki a Gaza, suke samun tabuwar hankali, da hakan yake sa su kashe kawukansu bayan sun baro Gaza.
Wasu rahotannin sun ambaci cewa, sojojin na HKI suna rayuwa ne a cikin tsaro da ranaza saboda munanan ayyukan da su ka aikata marasa kyau.