Wang Yi: Neman Sulhu Da Ja Da Baya Riba Ne Ga Masu Son Cin Zali
Published: 30th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen kasar Brazil Mauro Vieira ne ya jagoranci wannan taro, inda bangarori daban daban suka tattaunawa kan yadda kasashen BRICS za su karfafa zaman lafiya da tsaron duniya. (Mai Fassara: Maryam Yang)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku.
এছাড়াও পড়ুন:
Bashin da ake bin Najeriya zai koma tiriliyan 162
Idan har Majalisar Dokoki ta Kasa ta amince da bukatar Shugaban Kasa Bola Tinubu ta neman sake ciyo sabon bashi, jimillar bashin da ake bin Najeriya a yanzu zai koma Naira tiriliyan 162.
A ranar Talata ce shugaban ya aike wa Majalisar Wakilai takardar neman ta sahale masa ya ciyo bashin, wacce shugaban majalisar, Abbas Tajuddeen ya karanta a zauren majalisar.
Abbas ya ce rancen na 2025–2026, ya kunshi Dala biliyan 21.5 (kimanin Naira tiriliyan 34) da Yuro biliyan 2.2 (kimanin Naira tiriliyan 3.96) da Yen na Japan biliyan 15 (kimanin Naira biliyan 164.7) da kuma Yuro miliyan 65 (kimanin Naira biliyan 116.79) a matsayin tallafi.
Tinubu zai ciyo bashin Naira tiriliyan 39 daga kasashen waje Kotu ta ci su El-Rufa’i tarar miliyan 900Yana kuma neman cin bashin cikin gida ta hanyar bayar da takardun lamuni na Dala biliyan biyu, kimanin Naira tiriliyan 34.285, don biyan basussukan fanshon adashi gata da suka taru.
Tinubu ya nemi amincewa da bayar da takardun lamuni na Naira biliyan N757.98 a cikin gida domin biyan basussukan fansho da suka taru har zuwa ranar 31 ga Disamba, 2023.
Shugaban kasan ya bayyana cewa an tsara neman bashin ne don tallafa wa muhimman ayyukan a fannonin ababen more rayuwa, noma, lafiya, ilimi, da tsaro a dukkan jihohi 36 da Babban Birnin Tarayya.
Ya bayyana cewa bayar da takardun lamuni na Dala biliyan biyu ya yi daidai da Dokar Zartarwa ta Shugaban Kasa da nufin samar kuɗin domin farfado da darajar Naira da gudanar da muhimman ayyukan samar da ababen more rayuwa da samar da ayyukan yi.
Tinubu ya jaddada gaggawar buqatar wadannan kudade, yana mai nuni da tasirin cire tallafin mai da raguwar kudaden shiga na cikin gida.
Ya lura cewa hakan zai magance rashin bin tanade-tanaden Dokar Gyara Fansho a baya saboda matsalolin samun kuɗi, da nufin dawo da ƙwarin gwiwa a tsarin fansho da inganta jin daɗin tsofaffin ma’aikatan gwamnati.
Dukkan buƙatun guda uku an miƙa su ga Kwamitin Kula da Kuɗi na Majalisar don ɗaukar matakan majalisa na gaba.