Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
Published: 29th, April 2025 GMT
Hukumar Jin Daɗin Alhazai ta Jihar Jigawa ta ƙaddamar da shirin rigakafin mahajjata na shekarar 2025 a yankin Hadejia da ke shiyyar arewa maso gabas ta jihar.
Shugaban hukumar, Alhaji Ahmed Umar Labbo, ne ya bayyana hakan ga manema labarai a Hadejia.
Alhaji Ahmed Umar Labbo ya jaddada kudirin hukumar na ba da fifiko ga lafiya da kuma tsaron mahajjatan jihar.
Ya ce, kare lafiyar mahajjatan jihar nauyi ne da ya rataya a wuyan hukumar.
“Shirin rigakafin da muka fara yana nuna shirinmu na tabbatar da nasarar aikin Hajjin shekarar 2025. Ina ƙarfafa mahajjata su ba da haɗin kai tare da bin ƙa’idojin lafiya yayin wannan tafiya mai albarka.”
“Ina kuma ƙarfafa ku da ku zama masu bin doka da haƙuri yayin aikin Hajji. Da fatan za ku halarci dukkan tarukan bita da kai da aka shirya, domin muhimmanci su Alhazai” In ji shi.
Labbo, wanda ya sa ido a kan shirin rigakafin tare da bai wa wani mahajjaci daga Hadejia allurar farko, ya bayyana cewa aikin rigakafin zai ci gaba har zuwa lokacin tafiyar su zuwa ƙasa mai tsarki.
Haka kuma, Shugaban cibiyar lafiya a matakin farko, Dr. Bala Ismaila, ya bayyana muhimmancin allurar rigakafin da ake bayarwa, wanda ya haɗa da rigakafin cutar sankarau, cutar shan inna, da kuma cutar zazzabin cizon sauro (yellow fever).
Ya kuma yi bayani kan yiwuwar fuskantar rashin lafiya bayan rigakafin, inda ya shawarci mahajjata da su nemi kulawar likita cikin gaggawa idan suka fuskanci hakan ko wata matsala da ta wuce kima.
Wakilinmu ya ruwaito cewa, ana gudanar da aikin rigakafin a dukkan kananan hukumomi 27 na jihar.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa
এছাড়াও পড়ুন:
Isra’ila da Iran su daidaita rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya
Gwamnatin Tarayya ta roƙi ƙasashen Isra’ila da Iran da su daina rikici, su zauna lafiya su sasanta tsakaninsu.
A wata sanarwa da Ma’aikatar Harkokin Waje ta fitar, ta bayyana damuwa kan yadda rikicin ke ƙara ta’azzara, inda ta nemi ɓangarorin biyu da su kai zuciya nesa don samar da zaman lafiya a duniya baki ɗaya.
Mahara sun kashe mutum 26 a sabon hari a Binuwai Mulkin Tinubu ya fi kowane muni tun bayan dawowar mulkin farar hula — DalungSanarwar ta ce faɗa da ramuwar gayya na jefa rayukan fararen hula cikin hatsari, kuma yana iya haddasa rikici mai muni a yankin Gabas ta Tsakiya, wanda hakan zai iya barazana ga tsaron duniya da kuma ci gaban tattalin arziƙi dunuya.
“Mu a matsayimmu na ƙasa mai son zaman lafiya, muna roƙon ƙasashen da ke rikici da su zauna su tattauna maimakon su ci gaba da faɗa.”
Gwamnatin Tarayya ta kuma yi kira ga ƙasashen duniya, musamman Kwamitin Tsaro na Majalisar Ɗinkin Duniya, da su ɗauki matakai don hana yaɗuwar rikicin da kuma samo hanyar warware matsalar.
Sanarwar ta ƙara da cewa amfani da ƙarfin soji ba shi da amfani matuƙa, domin faɗa ba zai kawo sauƙi ba.
Najeriya ta ce a shirye ta ke ta bayar da taimako domin hana yaɗuwar rikicin da kuma tabbatar da zaman lafiya a yankin.