Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@02:19:33 GMT

Ba zan shiga ruɗani ba saboda matsalolin Man United – Amorim

Published: 26th, January 2025 GMT

Ba zan shiga ruɗani ba saboda matsalolin Man United – Amorim

Ruben Amorim ya yi amai ya lashe kan kalaman da ya yi cewar ƙungiyarsa ta Manchester United ta kakar nan ita ce mafi muni a tarihi.

Sai dai ya ce ba zai yi yaudara ba da cewar ba su da manyan matsaloli ba a kasa.

Amorim ya ce ya yi kuskure da ya samar da baraka lokacin da ya fuskanci ƴan wasa nan take, bayan tashi karawar da Brighton ta yi nasara 3-1 a Premier League.

Hakan ya sa ya gana da ƴan jarida cikin fushi da ta kai ya faɗi wasu kalaman.

An tambaye shi ko ya san cece-kucen da batunsa ya haifar kafin fuskantar Rangers a Europa League, Amorin sai ya ce yana magana da kansa ba da ƴan wasa ba.

Sai dai ya amince da dukkan sakamakon da ya faru a United tun bayan da ya kama aiki a cikin Nuwamba – Ya samu maki 11 da rashin nasara shida daga wasa 11 a Premier League – wannan ba abin a yaba bane.

”Ina magana da kaina fiye da ƴan wasa, kamar yadda Amorim ya ce ”Amma wasu lokutan yana da wuya na ɓoye fushi na.”

United tana gurbin da za ta iya kai wa zagayen ƴan 16 a Europa League kai tsaye, an fitar da ita a League Cup, kuma tana ta 13 a teburin Premier League.

Har yanzu akwai batun da ake tambaya kan dakikin da United ba ta kokari a gida, wadda aka doke wasa huɗu daga biyar da ta yi baya.

An doke United wasa shida daga 12 da ta yi a Old Trafford a Premier League – ƙwazo mafi muni tun bayan 1893-94.

Watakila United ta fuskanci wasannin gaba da kwarin gwiwa, saboda mai tsaron baya, Victor Lindelof ya koma atisaye bayan jinya, haka shima Marcus Rashford ya fara karɓar horo, wanda ake alakanta shi da wasu ƙungiyoyin.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe

Dakarun Operation Haɗin Kai sun kama mut biyar da ake zargin suna taimaka wa ’yan ta’adda da kayan aiki.

Daga cikinsu har da wani ɗan ƙasar China da ya ce shi mai harkar ma’adinai ne.

Damina: NiMet ta gargaɗi jihohi 13 kan barazanar ambaliyar ruwa Ya kamata Isra’ila da Iran su kawo ƙarshen rikicin da ke tsakaninsu — Gwamnatin Tarayya

An kama su ne a lokacin kai wani samame da aka gudanar daga 5 zuwa 7 ga watan Yuni a ƙananan hukumomin Kukawa da Ngala na Jihar Borno, da kuma Geidam a Jihar Yobe.

A lokacin wannan aiki, dakarun sun ƙwato wasu kayayyaki da suka haɗa da mota, babur, wayoyin salula, fasfo na ƙasar China, da kuma kuɗi Naira 10,000.

Shugaban sashen yaɗa labaran tsaro, Manjo Janar Edward Markus Kangye, ya bayyana hakan a wata ganawa da manema labarai a Abuja.

Ya ce sojojin sun kuma kai farmaki wasu yankuna bisa bayanan sirri da suka samu, ciki har da Gwoza da Abadam a Borno da kuma Nangere a Yobe, daga 6 zuwa 9 ga watan Yuni.

Ya ƙara da cewa daga 6 zuwa 11 ga watan Yuni, wasu maza da mata da yara da dama sun miƙa wuya ga dakarun Najeriya.

Kangye ya bayyana cewa rundunar ta kuma kai wasu hare-hare tare da haɗin gwiwar jami’an tsaro a Ngala, Marte, Gwoza a Jjihar Borno da Bade da Gujba a Jihar Yobe daga 6 zuwa 10 ga watan Yuni.

A wannan lokaci, sun lalata sansanonin ’yan ta’adda, sun ƙwato makamai da alburusai.

Manjo Janar Kangye ya ce sojojin Najeriya za su ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin ’yan ƙasa tare da tabbatar da doka da oda.

“Mun ƙudiri aniyar kare martabar Najeriya da tabbatar da zaman lafiya a kowane yanki na ƙasar nan. Wannan aiki namu na ci gaba da yin tasiri,” in ji shi.

Ya buƙaci haɗin kan jama’a wajen taimaka wa sojoji su ci gaba da yaƙi da ’yan ta’adda.

Ya ce idan jama’a da hukumomi suka haɗa kai, Najeriya za ta samu zama lafiya da wadata.

“Zamu ci gaba da sanar da al’umma duk wani ci gaba da muka samu wajen yaƙar ta’addanci,” in ji Kangye.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sojoji Sun kama ɗan China da wasu 4 kan zargin safarar makamai a Borno da Yobe
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawar mutum bayan kwanaki 8
  • Ambaliyar Mokwa: An sake gano gawa guda bayan kwanaki 8
  • Majalisar Tarayya Na Ƙoƙarin Zama Ƴar Amshin Shata – Saraki
  • Cikin Shekaru 2, Tinubu Ya Karɓo Bashi Fiye da Shugabannin Nijeriya 3 – Obi
  • De Bruyne Ya Kammala Komawa Napoli Bayan Barin Man City
  • An kashe jaririn wata 9 da wasu 3 a Filato
  • Zan Ci Gaba Da Ɓata Wa Masu Sukar Tinubu Rai Da Ayyuka – Wike