Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-03-20@12:01:03 GMT

Ba zan shiga ruɗani ba saboda matsalolin Man United – Amorim

Published: 26th, January 2025 GMT

Ba zan shiga ruɗani ba saboda matsalolin Man United – Amorim

Ruben Amorim ya yi amai ya lashe kan kalaman da ya yi cewar ƙungiyarsa ta Manchester United ta kakar nan ita ce mafi muni a tarihi.

Sai dai ya ce ba zai yi yaudara ba da cewar ba su da manyan matsaloli ba a kasa.

Amorim ya ce ya yi kuskure da ya samar da baraka lokacin da ya fuskanci ƴan wasa nan take, bayan tashi karawar da Brighton ta yi nasara 3-1 a Premier League.

Hakan ya sa ya gana da ƴan jarida cikin fushi da ta kai ya faɗi wasu kalaman.

An tambaye shi ko ya san cece-kucen da batunsa ya haifar kafin fuskantar Rangers a Europa League, Amorin sai ya ce yana magana da kansa ba da ƴan wasa ba.

Sai dai ya amince da dukkan sakamakon da ya faru a United tun bayan da ya kama aiki a cikin Nuwamba – Ya samu maki 11 da rashin nasara shida daga wasa 11 a Premier League – wannan ba abin a yaba bane.

”Ina magana da kaina fiye da ƴan wasa, kamar yadda Amorim ya ce ”Amma wasu lokutan yana da wuya na ɓoye fushi na.”

United tana gurbin da za ta iya kai wa zagayen ƴan 16 a Europa League kai tsaye, an fitar da ita a League Cup, kuma tana ta 13 a teburin Premier League.

Har yanzu akwai batun da ake tambaya kan dakikin da United ba ta kokari a gida, wadda aka doke wasa huɗu daga biyar da ta yi baya.

An doke United wasa shida daga 12 da ta yi a Old Trafford a Premier League – ƙwazo mafi muni tun bayan 1893-94.

Watakila United ta fuskanci wasannin gaba da kwarin gwiwa, saboda mai tsaron baya, Victor Lindelof ya koma atisaye bayan jinya, haka shima Marcus Rashford ya fara karɓar horo, wanda ake alakanta shi da wasu ƙungiyoyin.

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe

Ya kuma nuna jin daɗinsa da irin nasarorin da aka samu a ƙarƙashin jagorancin Kwamared Alhassan Yahayan, inda ya ce an ɗora ƙungiyar kan kyakkyawan turbar da ya kamata don ta ci gaba da taka rawar gani wajen bunƙasa aikin jarida a Nijeriya.

 

Yahaya ya jaddada cewa akwai kyakkyawar dangantaka tsakanin gwamnatin Jihar Gombe da ‘yan jarida, yana mai bada tabbacin cewa wannan kyakkyawar alaƙa da haɗin gwiwa za su kasance ginshiƙin gudanar da mulki a jihar.

 

“Mu a Jihar Gombe muna alfahari da daɗaɗɗiyar dangantakar da muka ƙulla da ‘yan jarida; ‘yan jarida abokan aikinmu ne masu ƙima a fagen kawo ci gaba, kuma muna ci gaba da jajircewa wajen ganin sun ci gaba da yin aiki a yanayin da zai bunƙasa sana’o’insu da ‘yancinsu,” inji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma bada tabbacin cewa gwamnatinsa za ta ci gaba da haɗa gwiwa da NUJ da sauran ƙungiyoyin yaɗa labarai don ba su damar ci gaba da kuma gudanar da muhimmiyar rawar da suke takawa wajen ankarar da gwamnati da wayar da kan jama’a.

 

Gwamna Inuwa ya ƙara da cewa, “Gudunmawar da kuka bayar na da matuƙar muhimmanci wajen inganta demokraɗiyya, da riƙon amana, da kuma shugabanci na gari a Nijeriya, muna godiya da irin rawar da kuke takawa wajen faɗakar da jama’a, da kare gaskiya, da kuma inganta manufofin gaskiya da adalci,” in ji Gwamna Inuwa Yahaya.

 

Ya kuma jaddada ƙudurin gwamnatin jihar na yin haɗin gwiwa mai ɗorewa da ‘yan jarida, inda ya jaddada muhimmancinsu wajen ci gaban Jihar Gombe dama Nijeriya baki ɗaya.

 

“Muna fatan ƙara ƙarfafa haɗin gwiwarmu da NUJ, kuma muna da yaƙinin cewa, tare, za mu ci gaba da gina ƙasa mai wadata, zaman lafiya da ci gaba,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sanƙarau ta kashe mutum 55 saboda rashin tsafta a Kebbi
  • Cikar NUJ Shekaru 70: ‘Yan Jarida Abokan Hulɗa Ne Wajen Aza Kyakkyawar Makoma – Gwamnan Gombe
  • Za Mu Bi Doka Domin Dawo Da Haƙƙinmu – Fubara
  • El-Rufai Ya Shiga Tsilla-tsilla Bayan Rasa Kujerar Minista – APC
  • DAGA LARABA: Abin da doka ta ce kan dakatar da zaɓaɓɓen Gwamna
  • Nijar Ta Fice Daga Kungiyar Kasashen Da Ke Amfani Da Faransanci
  • Nijar Ta Fice Daga Kungiyar Kasashen Da Ke Amfani Da da Faransanci
  • Ba A Taɓa Shugaban Ƙasar Da Ya Kai Mahaifina A Nijeriya Ba – Ɗan Shugaba Tinubu
  • Ba A Taɓa Shugaban Ƙasar Da Ya Kai Mahaifina A Nijeriya Ba – Ɗan Shugaban Tinubu
  • Tsohon Ɗan Takarar Gwamna A Legas  Ya Koma APC Daga PDP