Hajji 2025: Hukumar Alhazan Yobe ta gudanar da taro don mahajjata
Published: 26th, April 2025 GMT
Hukumar Alhazai ta Jihar Yobe ta gudanar da wani muhimmin taro ƙarƙashin jagorancin shugaban hukumar Alhaji Mai Aliyu Usman kan yadda za a tsara shirye-shiryen hajiin bana daga nan gida Najeriya zuwa ƙasa mai tsarki Saudiyya.
A yayin taron shugaban hukumar ya yi wa mambobin kwamitin alhazan ƙarin haske kan tsare-tsaren da aka yi don samun nasarar daidaitawa da jin daɗin alhazan da ke shirin gudanar da aikin Hajji na shekarar 2025.
Mai Aliyu ya ce, tuni gwamnatin jihar ta samar da duk wasu muhimman kayayyaki don sauƙaƙa tafiyar mahajjata, waɗanda suka haɗa da: jakunkuna, kayan sawa na maza da mata da kuma lambar tantancewa.
Wannan tallafi mai fa’ida yana nuna ƙudurin gwamnati na tabbatar da kwanciyar hankali, aminci, da daidaita aikin hajji na bana 2025.
Ya jaddada ƙudirin hukumar na ganin an gudanar da aikin hajji cikin kwanciyar hankali da lumana ga dukkan maniyyatan Jihar Yobe.
A yayin taron, shugaban hukumar, tare da mambobin kwamitin Hajji sun karɓi allurar rigakafin da ma’aikatan aikin hajji suka gudanar.
Wannan ya nuna yadda aka fara shirye-shiryen aikin hajji na shekarar 2025, tare da tabbatar da lafiya da amincin ga dukkan jami’ai da maniyyata.
Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da: Amirul Hajj, mai martaba Alhaji Abubakar Muhammad Ibn Grema (Mai Tikau), da Mohammed Mairami a matsayin sakataren kwamitin Alhaji Gana Fantami mamba a kwamitin, Sanata Alkali Jajere mamba sai mai shari’a Uwani mamba da sauran mambobin kwamitocin aikin hajji.
Taron ya kuma kasance wani dandali ga mambobin kwamitin don yin shawarwari kan muhimman dabaru da kuma fahimtar yadda za a samu gudanar da ingantaccen aikin hajji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Boko Haram ta kashe masu zaman makoki 7 a Chibok
Mayaƙan ƙungiyar Boko Haram sun kashe masu zaman makoki bakwai tare da jikkata wasu a ƙauyen Kopl da ke Ƙaramar Hukumar Chibok ta Jihar Borno.
Shugaban Karamar Hukumar, Honorabul Modu Mustapha, ya ce mayaƙan sun buɗe wa mutanen wuta ne a yammacin ranar Litinin, a yayin da suke shirin gudanar da addu’o’i ga ’yan uwansu da suka rasu.
Ya ce, “Sun taru ne domin yin addu’a lokacin da ’yan ta’addan suka sauka a kansu. Mun kwashe mutane da yawa da suka samu raunukan harsashi zuwa Babban Asibitin Mubi da ke maƙwabtaka da Jihar Adamawa.
“Adadin waɗanda suka mutu na iya ƙaruwa, saboda wasu sun tsere cikin daji da raunukan harsashi. Ana ci gaba da aikin nemowa da ceto waɗanda ke cikin daji,” in ji shi.
Bom ɗin Boko Haram ya kashe mutane 26 a Borno NAJERIYA A YAU: Dalilin karyewar farashin shinkafa a kasuwannin Najeriya Shugaban Majalisar Ƙoli ta Shari’ar Musulunci a Najeriya ya rasuSanatan Borno ta Kudu, Ali Ndume, ya ci gaba da yin Allah wadai da hare-haren, inda ya bayyana halin da ake ciki a matsayin abin da ya wuce tunanin dan Adam.
“Ko jiya ma, na samu kiran gaggawa cewa an kashe sama da ’yan banga 10 a wani yankin da ke tsakanin Karamar Hukumar Hawul ta Jihar Borno da garin Garkida a Jihar Adamawa.
“Al’ummata na fama da munanan asara ba tare da wani faɗa ba. A cikin wata guda da ya gabata kaɗai, an kashe sama da mutum dari a hare-hare da dama yankunan Sabon Gari da Izge da Kirawa da Pulka da Damboada Chibok da Askira Uba da wasu da yawa da ba zan iya lissafawa ba,” in ji Sanata Ndume.