Hajji 2025: Hukumar Alhazan Yobe ta gudanar da taro don mahajjata
Published: 26th, April 2025 GMT
Hukumar Alhazai ta Jihar Yobe ta gudanar da wani muhimmin taro ƙarƙashin jagorancin shugaban hukumar Alhaji Mai Aliyu Usman kan yadda za a tsara shirye-shiryen hajiin bana daga nan gida Najeriya zuwa ƙasa mai tsarki Saudiyya.
A yayin taron shugaban hukumar ya yi wa mambobin kwamitin alhazan ƙarin haske kan tsare-tsaren da aka yi don samun nasarar daidaitawa da jin daɗin alhazan da ke shirin gudanar da aikin Hajji na shekarar 2025.
Mai Aliyu ya ce, tuni gwamnatin jihar ta samar da duk wasu muhimman kayayyaki don sauƙaƙa tafiyar mahajjata, waɗanda suka haɗa da: jakunkuna, kayan sawa na maza da mata da kuma lambar tantancewa.
Wannan tallafi mai fa’ida yana nuna ƙudurin gwamnati na tabbatar da kwanciyar hankali, aminci, da daidaita aikin hajji na bana 2025.
Ya jaddada ƙudirin hukumar na ganin an gudanar da aikin hajji cikin kwanciyar hankali da lumana ga dukkan maniyyatan Jihar Yobe.
A yayin taron, shugaban hukumar, tare da mambobin kwamitin Hajji sun karɓi allurar rigakafin da ma’aikatan aikin hajji suka gudanar.
Wannan ya nuna yadda aka fara shirye-shiryen aikin hajji na shekarar 2025, tare da tabbatar da lafiya da amincin ga dukkan jami’ai da maniyyata.
Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da: Amirul Hajj, mai martaba Alhaji Abubakar Muhammad Ibn Grema (Mai Tikau), da Mohammed Mairami a matsayin sakataren kwamitin Alhaji Gana Fantami mamba a kwamitin, Sanata Alkali Jajere mamba sai mai shari’a Uwani mamba da sauran mambobin kwamitocin aikin hajji.
Taron ya kuma kasance wani dandali ga mambobin kwamitin don yin shawarwari kan muhimman dabaru da kuma fahimtar yadda za a samu gudanar da ingantaccen aikin hajji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi
Hukumar NDLEA ta bayyana cewa wata ƙungiyar masu safarar miyagun ƙwayoyi ce a filin jirgin sama na Kano ta boye jakunkunan ƙwayoyi a cikin kayan matafiyan.
An kama shugaban ƙungiyar, Ali Abubakar Mohammed (wanda aka fi sani da Bello Karama), tare da wasu abokan aikinsa.
Hukumar ta ce mutanen ukun ba su da laifi kuma an zalunce su ne kawai.
An saki su ne bayan bincike da kuma ƙoƙarin diflomasiyya na tsawon makonni.
Lamarin ya tayar da hankali kan tsaro a filayen jirgin sama a Nijeriya da yadda masu aikata laifuka ke amfani da fasinjoji marasa laifi.
Hukumar ta ce za a ɗauki ƙarin matakai don hana faruwar irin wannan lamari.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp