Hajji 2025: Hukumar Alhazan Yobe ta gudanar da taro don mahajjata
Published: 26th, April 2025 GMT
Hukumar Alhazai ta Jihar Yobe ta gudanar da wani muhimmin taro ƙarƙashin jagorancin shugaban hukumar Alhaji Mai Aliyu Usman kan yadda za a tsara shirye-shiryen hajiin bana daga nan gida Najeriya zuwa ƙasa mai tsarki Saudiyya.
A yayin taron shugaban hukumar ya yi wa mambobin kwamitin alhazan ƙarin haske kan tsare-tsaren da aka yi don samun nasarar daidaitawa da jin daɗin alhazan da ke shirin gudanar da aikin Hajji na shekarar 2025.
Mai Aliyu ya ce, tuni gwamnatin jihar ta samar da duk wasu muhimman kayayyaki don sauƙaƙa tafiyar mahajjata, waɗanda suka haɗa da: jakunkuna, kayan sawa na maza da mata da kuma lambar tantancewa.
Wannan tallafi mai fa’ida yana nuna ƙudurin gwamnati na tabbatar da kwanciyar hankali, aminci, da daidaita aikin hajji na bana 2025.
Ya jaddada ƙudirin hukumar na ganin an gudanar da aikin hajji cikin kwanciyar hankali da lumana ga dukkan maniyyatan Jihar Yobe.
A yayin taron, shugaban hukumar, tare da mambobin kwamitin Hajji sun karɓi allurar rigakafin da ma’aikatan aikin hajji suka gudanar.
Wannan ya nuna yadda aka fara shirye-shiryen aikin hajji na shekarar 2025, tare da tabbatar da lafiya da amincin ga dukkan jami’ai da maniyyata.
Waɗanda suka halarci taron sun haɗa da: Amirul Hajj, mai martaba Alhaji Abubakar Muhammad Ibn Grema (Mai Tikau), da Mohammed Mairami a matsayin sakataren kwamitin Alhaji Gana Fantami mamba a kwamitin, Sanata Alkali Jajere mamba sai mai shari’a Uwani mamba da sauran mambobin kwamitocin aikin hajji.
Taron ya kuma kasance wani dandali ga mambobin kwamitin don yin shawarwari kan muhimman dabaru da kuma fahimtar yadda za a samu gudanar da ingantaccen aikin hajji.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Saudiyya
এছাড়াও পড়ুন:
Ambaliya: Gwamnatin Kano ta fara tsaftace magudanan ruwa
Yayin da damina ke ƙara ƙaratowa, Gwamnatin Jihar Kano, ta fara wani aikin tsaftace manyan magudanan ruwa domin daƙile aukuwar ambaliyar ruwa.
An fara aikin ne a yankin shataletalen Baban Gwari, ɗaya daga cikin wuraren da ambaliya ke yawan aukuwa a Birnin Kano.
Harin Isra’ila a kan Iran ya jefa yankin Gabas ta Tsakiya cikin zama dar-dar NAJERIYA A YAU: Rashin Aikin Yi Da Hanyoyin Magance Su A NajeriyaMa’aikatar Muhalli da Sauyin Yanayi ce ke jagorantar aikin tsaftace magudanan ruwan.
Wannan mataki na daga cikin shirin gwamnatin jihar na kare rayuka, dukiyoyi, da kuma inganta ababen more rayuwa.
A lokacin ƙaddamar da aikin, Kwamishinan Muhalli da Sauyin Yanayi, Hashim Muhammad Dahiru, ya bayyana cewa an zaɓi Baban Gwari saboda muhimmancinsa da kuma yadda wajen yake a lokacin damina.
Ya ce wajen ya daɗe da zama wajen zubar da shara barkatai da kuma toshe hanyoyin ruwa.
Ya ƙara da cewa wannan wajen ba wai kawai muhimmiyar mahaɗa ba ce, amma kuma yana ɗaya daga cikin manyan hanyoyin ruwa da ke da alaƙa da ruwan Jakara da Kwarin Gogau.
Kwamishinan ya bayyana cewa mazauna yankin da masu wucewa sun sha fuskantar ambaliya da ta shafi rayuwarsu, lafiyarsu da kuma zirga-zirgarsu.
Ya ce wannan aikin ba na al’ada ba ce, illa alama ce da ke nuna cewa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin kare muhalli da kuma samar da birni mai jure sauyin yanayi da ambaliya.
Ya yaba wa Gwamna Abba Kabir Yusuf bisa jagoranci da goyon bayan da ya bai wa ma’aikatar wajen aiwatar da wannan aiki.
Ya ce gwamnatin ta amince da sanya tsaftace magudanan ruwa a matsayin aikin da za a riƙa gudanarwa a kowace shekara domin tabbatar da tsaftar hanyoyin ruwa a faɗin jihar.
Haka kuma, gwamnatin ta bayar da kwangilar gyaran shataletalen Baban Gwari domin inganta zirga-zirga da rage yawan ambaliya, ta hanyar gina sabbin hanyoyin ruwa.
Kwamishinan ya bayyana cewa waɗannan matakai suna nuna irin hangen nesa da damuwar gwamnan jihar kan lafiyar jama’a da kuma kare su daga illolin da ke zuwa da ambaliya da sauyin yanayi.
Ya buƙaci jama’a da su daina zubar da shara barkatai, musamman a cikin magudanan ruwa, ya kuma buƙaci su riƙa ɗaukar nauyin tsaftace muhallinsu.
Ya ce gwamnatin za ta yi nata aikin, amma ana buƙatar haɗin gwiwar kowa da kowa domin a cimma nasara.
Ya kuma buƙaci ma’aikata da abokan aikin muhalli da su gudanar da aikinsu da kulawa da gaskiya, yana mai cewa aikin ba wai tsaftace magudanan ruwa ba ne kawai, amma aikin ne na kare rayuka, daƙile haɗura da kuma gina sabuwar Kano mai tsafta da lafiya.
A ’yan shekarun nan, yankin Baban Gwari ya yi ƙaurin suna wajen yawan aukuwar ambaliya, har ma da rasa rayuka da dukiyoyi.
Wannan ya sa gwamnatin jihar ta ɗauki matakin gaggawa domin magance matsalar kafin saukar daminar bana.