Jaridar The Guardian Mafi Yawan ‘Yan Gudun Hijiran Sudan Ne A Gidan Yarin Kasar Girka
Published: 29th, April 2025 GMT
Jaridar The Guardian ta Buga Labarin Cewa: Gidajen yarin Girka sun cika makil da ‘yan gudun hijirar Sudan
Jaridar The Guardian ta kasar Britaniya ta ruwaito cewa: Mahukuntan kasar Girka na tsare da daruruwan bakin haure ba bisa ka’ida ba a karkashin wata doka mai tsauri da ta fara aiki a shekara ta 2014 kuma dokar ta kunshi hukunta masu laifin daurin shekaru 25 a gidan yari.
Jaridar ta The Guardian ta ruwaito cewa: Masu fasakwaurin mutane da aka yanke wa hukunci sun zama rukuni na biyu mafi girma a gidajen yarin Girka, bayan masu safarar miyagun kwayoyi.
Jaridar ta bayyana cewa ‘yan Sudan su ne rukuni na hudu mafi girma na masu neman mafaka a kasar Girka, inda suka zarce ‘yan ciranin gargajiya na wasu kasashe kamar ‘yan Siriya da Falasdinawa.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: The Guardian
এছাড়াও পড়ুন:
Wata 6 Da Haramta Kauyawa Day A Kano: Badalar Na Ci Gaba Da Gudana
Misali, a lokutan hare-haren, an kone gidaje da dama, inda wasu ahali ma, wanda yawansu ya kai, har zuwa 15, aka shafe su, daga doron kasa, a lokacin da suke kan bacci, a gidansu.
Wasu daga cikin wadanda suka tsallake Rijiya da baya daga hare-haren na ‘yan ta’addar, sun bayyna yadda ‘yan ta’addar, suka cinnawa wasu shaguna da ke a wata kasuwa, da ka mayar a matsayin wajen kwanan, ‘yan gudun hijira, wuta.
Duk da kokarin da wasu matasa da kuma kokrin jami’an tsaro na dakile maharani, hakan ya faskare su, hatta wani daya daga cikin jami’in tsaro da aka tura wanzar da tsaro, ya rasa ransa.
Duk a 2025, a watan Afiiru an kai hare-hare a Logo da Ukum, inda aka kashe sama da 50.
Abin takaicin shi ne, duba da cewa akasarin masu kai hare-haren, sai sun sanar sanar suke kai hare-haren.
A gafe daya kuma, shuwagabbin alumma a wadannan yankunan su kan ankarar da hukumomi kafen kai hare-haren, amma abin takaici, mahukuntan, ba su daukar matakan dakile kai hare-haren.
A kwanan baya, Shugaba Bola Tinubu, ya umarci manyan Hafshoshin sojin kasar, da su gaggauta, kawo karshen kai hare-haren, tare da dawo da zaman lafiya a jihar.
Kazalika, ya danganta kashe-kashen, a matsayin na rashin imani da janyo koma baya, inda kuma ya yi kira ga jagororin ‘yan siyasa da shuwagabanin alumomi da ke a jihar, musamman a yankunan da lamarin yafi yin kamari, da su dakatar da rura wata, kan rikice-rikicen, musamman kan yadda suke furta kalaman kiyayya.
Fafaroma, Leo na 14, a na sa bangaren, ya yi tir da kashe-kashen a jihar, inda ya danta lamarin da kisan Kiyashi.
Hakazalika, Gwamnan jihar Hyacinth Alia, a martaninsa, ya bukaci Gwamnatin Tarayya da ta kawo wa jihar dauki, wanda ya yi nuni da cewa, Biniwe ba wai dokar ta baci take bukata ba, daukin gaggawa take bukata, ta hanyar tura jami’an tsaro da kayan aiki, domin a yaki, masu kai hare-haren.
Sai dai, wannan furucin na gwamnan, tamkar holoko ne, kawai, domin alummar jihar, sun gaji, da yin wani zaman makoki, sun fi bukatar, a samar masu da jami’an tsaro, su kuma koma su ci gaba da noma gonakansu, suna kuma son su ci gaba da barcinsu, da idanuwansu, biyu, a rufe, ba tare da wata fargabar, za a kai masu hari a yayin da suke kan yin barcinsu ba.
A gafe daya kuma, ana ci gaba da cacar baki a tsakanin Gwamna Alia da wasu jiga-jigai na jihar, inda Gwamnan a kwanan baya, ya yi zargin cewa, akwai wasu ‘yan siyasar jihar, da ke zaune Abuja, suke ci gaba da kara rurar wutar rikici a jihar, ciki har da ma wasu jiga-jigan ‘yan Majalisar kasa da suke wakiltar mazabunsu, a majalisar.
Koda yake dai, ‘yan Majalisar, sun karyata wannan ikirarin na Gwamnan, inda suka zargi Alia, da kin wanzar da dokar barin yin kiwo a bainar jama’a a jihar.
Bai wai kawai cafko masu aikata ta’asar ya kamata ayi, ya zama wajibi, a hukunta su, kamar yadda dokar kasar, ta tanada.
Bugu da kari, dole ne Gwamnatin Tarayya, ta gagauta daukar matakai, tare da kuma taimakawa Gwamnatin jihar, domin ta samu karfin tarwatsa masu kai wa alumomin, hare-haren da kare alumomin.
Ya kuma zama wajbi, a sake yin nazari, kan batun iyakokin jihohi da batun burtanin masu kiwon dabbobi da kuma karfafa dangantaka, a tsakanin Fulani makiyaya da sauran alumomin da ke a jihar.
Hakazalika, ya zama wajibi, Gwamnatin Tarayya ta hada taron tattaunawa na kasa, kan batun na kai hare-haren.
Wannan Jaridar, ita ma, ta bi sahun sauran ‘yan Nijeriya, wajen mika ta’aziyyarta, bisa rasa rayukan da hare-haren ya rutsa da su tare da kuma kira da a dauki matakan gaggawa kan batun, ba wai kawai, yin bayanai ba.
Lokaci ya yi, da za a kawo karshen rikice-rikice da nuna kiyaya, a tsakanin juna.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp