Mai ba da shawara ga Jagoran juya juya halin Musulunci kan harkokin siyasa ya bayyana cewa: Tattaunawar Muscat wata dama ce ta samun zaman lafiya kan batutuwa masu sarkakiya

Ali Shamkhani mai ba Jagoran juyin juya halin Musulunci shawara kan harkokin siyasa ya yi tsokaci kan tattaunawar ba na kai tsaye ba da ake yi tsakanin Iran da Amurka a babban birnin kasar Omani na Muscat.

A cikin jerin sakonnin da ya wallafa a shafinsa na twitter, Shamkhani ya bayyana cewa: Fiye da kwanaki 100 ke nan da Trump ya hau kan karagar mulki, yana mai cewa: “Ba a warware manyan batutuwan da suka shafi Yemen, Gaza, Ukraine, da rikicin haraji ba, baya ga gibin kasafin kudi, har yanzu ba a warware ba.”

Ya ci gaba da cewa: “A cikin wannan yanayi, tattaunawar Muscat ta bayyana a matsayin wata dama ta samun nasara ta hadin gwiwa tsakanin bangarorin da abin ya shafa (Amurka da Iran).”

Shamkhani ya kammala rubutunsa a twitter da cewa: Wadannan shawarwarin sun ginu ne a kan manyan ka’idoji guda uku: gaskiya (wanda ke tabbatar da cewa babu wata karkata daga manufofin da aka sa gaba); Ma’auni (wanda ke buƙatar ɗaga duk takunkumin da aka sanya); Da kuma bin doka (wanda ke ba da tabbacin haƙƙin haɓakawa cikin tsarin dokokin ƙasa da ƙasa).

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa

Ƴan ta’adda da ake zargin Boko Haram ne sun kashe mutane 10 na yawucin dabbobi da kuma mambobin jami’an tsaron sa kai (CJTF) a garin Kwapre, dake cikin ƙaramar hukuma ta Hong a Jihar Adamawa.

Shugaban ƙaramar hukuma, Hon Usman Wa’aganda, ya tabbatar da wannan lamarin ga LEADERSHIP ta waya a ranar Lahadi a Yola, inda ya bayyana cewa wani mutum da ya samu raunuka daga harin ‘yan ta’addan yana samun kulawar likita a wani asibiti da ba a bayyana sunansa ba.

Daidaikun Kasashe Za Su Kara Karfi Idan Suka Hada Hannu Tare ‘Yansanda Sun Kama Wani Kato Bisa Zargin Cin Zarafin Wata Mata A Adamawa

Wa’aganda ya ce ‘yan ta’addan sun ƙone gidaje da dama da kuma amfanin gona, yana mai cewa wannan harin ba na farko bane, domin garin ya sha hare-hare sau da dama wanda ya haifar da asarar rayuka da dukiyoyi.

Ya nemi hukumomin tsaro su ƙara tura jami’ai a yankin domin taimakawa wajen kare al’umma da kuma tabbatar da tsaro.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  • Karin Wata Kasa Da Bai San Ta Ba A Doron Duniya
  • Hajjin 2025: An Fara Yi Wa Maniyyata Allurar Rigakafi A Jigawa
  • Babu Wata Tattaunawa Tsakanin Sin Da Amurka Game Da Batun Haraji
  • Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Jaddada Cewa: Ci Gaba Da Killace Gaza Da Kashe Mutane, Laifi Ne Da Ba A Taba Yin Irinsa Ba
  • Akwai Ƙarin Gishiri A Yawan  Masu Sauyin Jam’iyya Zuwa APC – El-Rufai
  • Talata ce ɗaya ga watan Zhul Qi’ida — Sarkin Musulmi
  • Gwamnatin Tarayya Ta Umurci WAEC, NECO Su Koma Amfani Da CBT Nan Da 2026
  • Ministan Harkokin Wajen Kasar Iran Ya Tattauana Da Shugaban Hukumar IAEA
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa