Iran ta Bayyana cewa: TattaunawarMuscat Wata Dama Ce Ta Samun Zaman Lafiya Kan Batutuwan Masu Sarkakiya
Published: 26th, April 2025 GMT
Mai ba da shawara ga Jagoran juya juya halin Musulunci kan harkokin siyasa ya bayyana cewa: Tattaunawar Muscat wata dama ce ta samun zaman lafiya kan batutuwa masu sarkakiya
Ali Shamkhani mai ba Jagoran juyin juya halin Musulunci shawara kan harkokin siyasa ya yi tsokaci kan tattaunawar ba na kai tsaye ba da ake yi tsakanin Iran da Amurka a babban birnin kasar Omani na Muscat.
A cikin jerin sakonnin da ya wallafa a shafinsa na twitter, Shamkhani ya bayyana cewa: Fiye da kwanaki 100 ke nan da Trump ya hau kan karagar mulki, yana mai cewa: “Ba a warware manyan batutuwan da suka shafi Yemen, Gaza, Ukraine, da rikicin haraji ba, baya ga gibin kasafin kudi, har yanzu ba a warware ba.”
Ya ci gaba da cewa: “A cikin wannan yanayi, tattaunawar Muscat ta bayyana a matsayin wata dama ta samun nasara ta hadin gwiwa tsakanin bangarorin da abin ya shafa (Amurka da Iran).”
Shamkhani ya kammala rubutunsa a twitter da cewa: Wadannan shawarwarin sun ginu ne a kan manyan ka’idoji guda uku: gaskiya (wanda ke tabbatar da cewa babu wata karkata daga manufofin da aka sa gaba); Ma’auni (wanda ke buƙatar ɗaga duk takunkumin da aka sanya); Da kuma bin doka (wanda ke ba da tabbacin haƙƙin haɓakawa cikin tsarin dokokin ƙasa da ƙasa).
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Bayyana Adawa Da Keta Hurumin ‘Yanci Tsaro Da Ikon Mulkin Yankunan Iran
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp