HausaTv:
2025-05-18@16:50:55 GMT

 Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6

Published: 30th, April 2025 GMT

Wani bon kirar hannu da aka dasa akan hanyar dake hada Rann da Gamboru a jihar Borno ya yi sanadiyyar mutuwar mutane 6.

Daga cikin wadanda su ka rasa rayukansu sanadiyyar tashin bom din sun hada mata da kananan yara kamar yadda majiyar ‘yan sanda ta sanar.

Kungiyar nan mai suna; gwamnatin musulunci a yammacin Afirka ce ta sanar da daukar alhakin kai hari na ranar Litinin din da ta gabata.

Bugu da kari sauran wadanda su ka rasa rayukan nasu manoma ne da suke cikin motar a-kori-kura da ta taka nakiya.

Baya ga wadanda su ka rasa rayukansu, wasu mutanen su 3 sun jikkata,kuma tuni an dauke su zuwa asibiti domin yi musu magani.

Wani dan sintiri da yake aiki da rundunar fararen hula masu taimakawa jami’an tsaro, Abba Madu, ya shaida wa manema labaru cewa; Da alamu an dasa bom din domin ya tashi da jami’an tsaro da suke yin sintiri akan wannan hanyar.

Kungiyoyin ‘yan ta’adda sun saba dasa irin wadannan nakiyoyin da bama-baman akan hanyar da jami’an tsaro suke bi.

Kungiyar nan da take kiran kanta; Gwamnatin Musulunci a yammacin Afirka wacce a takaice ake kira; “ISWAP” ce ta dauki nauyin kai harin.

Tun a 2009 ne yankin Arewa maso gabashin kasar ta Najeriya yake fama da matsalar kungiyoyi masu dauke da makamai da su ka hada Bokoharam, sannan kuma daga baya waje 2016, kungiyar gwamnatin musulunci a yammacin Afirka.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Jam’iyyar NNPP wadda Dakta Boniface Aniebonam ya kafa a shekarar 2001, ta samu ƙarfi sosai a Jihar Kano bayan tsohon Gwamna Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya shiga cikinta a shekarar 2022 tare da mabiyansa na Kwankwasiyya.

Shigowarsa ta farfaɗo da jam’iyyar, inda ta samu gagarumar nasara a zaɓen 2023 ta hanyar lashe kujerar gwamna da wasu kujerun majalisa.

Sai dai rikicin cikin gida da na shugabanci sun dabaibaye jam’iyyar, wanda hakan ya haddasa ficewar wasu manyan ’ya’yanta zuwa APC, lamarin da ke haifar da tambaya kan makomar NNPP a Kano.

Shin NNPP za ta kai labari a Kano, musamman bayan ficewar wasu jiga-jiganta?

NAJERIYA A YAU: Kuskuren JAMB Da Ya Haddasa Faduwar Ɗalibai A Jarabawa DAGA LARABA: Tasirin Mulkin Karɓa-Karɓa A Najeriya

Wannan shi ne batun da shirin Najeriya A Yau na wannan lokaci zai yi duba.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunana
  • Mummunan Hatsarin Mota Ya Kashe Mutane 7, Wasu 11 Sun Raunato
  • Riƙaƙƙun ’yan daba da dilolin ƙwaya 31 sun shiga hannu a Kano
  • Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno
  • Kudaden da sojojin Afirka suka kashe a bara ya karu da dala biliyan 52 a shekarar 2024
  • Tinubu ya ƙaddamar da jirage 2, ya buƙaci a kawo ƙarshen matsalar tsaro
  • NAJERIYA A YAU: Shin Jam’iyyar NNPP Za Ta Kai Labari A 2027?
  • Mutum 10 sun rasu kan rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Mutum 10 sun rasu sakamakon rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Tsaro: Tinubu ya ƙaddamar da rundunar tsaron daji a faɗin Najeriya