Jagora Ya Bada Umurnin A Gudanar Bincike Mai Zurfi A Fashewar Tashar Jiragen Ruwa Na Shaheed Rajae
Published: 28th, April 2025 GMT
Jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminae, a karon farko da yayi magana dangane da fashewar tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae ya gabatar da Ta’ziyya ga iyalan wadanda suka rasa rayukansu ko suka jikata a wannan hatsarin. Ya kuma bukaci a gudanar da bincike mai mai zurfi don gano musabbabin fashewar.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto jagoran yana bada umurni ga ma’aikatar shari’aa a kasar ta gudanar da cikekken bincike don sanin abinda ya faru saboda daukar matakan da suka dace don hana irin wannan sake faruwa nan gaba, sannan idan akwai wadanda suka yi kuskure a hukunta su.
Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya bayyana cewa gobarar da ta taso a tashar jiragen ruwa na Shahid Rajae, daya daga cikin tashoshin jirage masu muhimmanci a tattalin arzikin kasar, don haka dole ne a kara daukar matakan tsaro da amincin tashar don hana irin wannan sake faruwa.
Sanadiyyar wannan hatsarin majalisar dokokin kasar ta shelanta makoki a duk fadin kasar a yau Litinin. Sannan shugaban kasa Masoud Pezeshkiyan ya ziyarci tashar jiragen ruwa na Shahida Rajae don ganewa idanunsa abubuwan da suka faru da kuma barnan da aka tabka.
Ya zuwa yanzun wadanda suka rasa rayukansu sun kai 40 sannan wadanda suka rasa rayukansu sun kai dubu guda.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: wadanda suka
এছাড়াও পড়ুন:
Sin Ta Fitar Da Jerin Sakamakon Tattaunawar Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Tawagar Kasar Da Ta Amurka Suka Cimma
A nata bangare, Amurka za ta dage aiwatar da matakai bisa bincikenta karkashin sashe na 301 na dokar cinikayya ta 1974, wanda zai shafi sashen jiragen ruwa na Sin, da hidimomin sufurinsu, da na kirar jiragen ruwan na Sin da karin shekara daya. Sakamakon hakan, ita kuma Sin za ta dage aiwatar da matakan martani ga sashen Amurka a wannan fanni da shekara daya, da zarar Amurkan ta aiwatar da na ta matakan.
Kakakin ya ce “An Kai Ruwa Rana” kafin cimma wannan sakamako, kuma Sin na fatan ganin ta ci gaba da aiki tare da tsagin Amurka, ta yadda za su hada karfi wajen tabbatar da an aiwatar da sakamakon, da ingiza karin tabbaci, da daidaito cikin dangantakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin sassan biyu, da kuma tattalin arzikin duniya baki daya. (Saminu Alhassan)
ShareTweetSendShare MASU ALAKA