Leadership News Hausa:
2025-11-02@19:36:10 GMT

Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai

Published: 29th, April 2025 GMT

Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai

“Lokacin da abubuwa suka fara lalacewa a lokacin shugaba Buhari, na fito na faɗi gaskiya. Lokacin da tsarin sauya fasalin Naira ya jefa jama’a cikin wahala, na ƙalubalanci gwamnati duk da cewa jam’iyyar APC ce ke kan mulki. Na fi biyayya ga Nijeriya fiye da kowane mutum,” in ji shi.

El-Rufai ya ƙaryata jita-jitar cewa fushinsa da gwamnatin Shugaba Tinubu ne ya sa ya fice daga APC.

Ya ce yana da shekaru 65, kuma babu wani abu da ya rage masa a siyasa da zai nema, sai dai kawai yana jin cewa matsalolin Nijeriya sun yi tsanani sosai wanda ba zai zauna ya yu shiru ba.

“Zan iya yin ritaya cikin kwanciyar hankali, amma Nijeriya na fuskantar babbar barazana. Wannan ba don kaina ba ne – don ceton ƙasa ne,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa dole a zaɓi shugaban ƙasa mai nagarta da hangen nesa, ba wai kawai din ya fito daga wata jiha ba.

“Matsalolin da muke fuskanta sun fi girman la’akari da inda mutum ya fito. Muna buƙatar shugabanni masu hangen nesa da ƙwarewa don gyara Nijeriya,” ya bayyana.

Da yake magana kan sauya sheƙar wasu ‘yan siyasa zuwa APC, El-Rufai ya ce jam’iyyar SDP tana mayar da hankali ne kan gina goyon baya daga jama’a, ba wai kawai neman manyan ‘yan siyasa ba.

“Gwamna ɗaya yana da ƙuri’a ɗaya ne kawai. Jama’a ne ke yin zaɓe, ba manyan ‘yan siyasa ba,” ya jaddada.

A ƙarshe, El-Rufai ya ce tafiyar SDP tana ci gaba da karɓuwa a dukkanin sassan Nijeriya, ba a yankuna kaɗan kaɗai ba.

“Muna ci gaba da gina goyon baya a faɗin ƙasar nan. Aikin gina ƙasa yana faruwa ne a tsakanin talakawa, ba kawai a kafafen yaɗa labarai ba,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

Maganin Nankarwa (3)

Yawan shafa man kade a wurin ma yana rage ta sosai.

Daga karshe Ina kira ga mata da su daure da zarar sun haihu su fara neman hanyan magance wannan matsalar kuma ku sani cewa wannan hadin gargajiya ne babu Kemikal a cikinsa don haka yana daukar lokaci kafin a ga canji kamar, sati biyu idan ba ki ga canji ba sai ki dauki wani kuma.

Allah shi ne masani. Allah yasa mu dace.

Ga hanyoyi guda 5 da za’a iya magance su a saukake ba tare da amfani da mayuka masu illlata fata ba

Hanya ta 1: Dankalin Hausa

Dankali yana dauke da sinadarin sitaci da yake lausasa fata da kuma sinadarin da yake hana fata lalacewa wato antiodidant. Haka kuma dankali yana dauke da sinadarin bitamin C, potassium, thiamin, riboflabin, iron, zinc da sauran su.

Yanda ake amfani da shi:

A yanka Dankali sannan a shafa a hankali a kan Nankarwar. Sai a bar shi na tsawon mintuna 15 zuwa 20, sannan a wanke da ruwan dumi. A maimaita haka a kullum

Hanya ta 2: Alo bera

Ruwan da ke cikin Alo bera yana dauke da sinadarin Collagen wanda aka san shi da gyara fatar da ta lalace da kuma kara laushin ta, kyanta da kuma yarintar ta.

Yanda ake amfani da shi:

A karya itacen Alo bera guda sai a shafa ruwan a kan Nankarwa. A bar shi tsawon awa 2 zuwa uku sai a wanke da ruwa. A maimata hakan a kullum har sai an samu sakamako mai kyau.

Hanya ta 3: Man kadanya da koko Bota

Hadin man kadanya da koko Bota yana dauke da sinadarin bitamin E da kuma sinadaran da ke hana fata lalacewa

Yadda ake amfani da shi

Za’a samu Koko Bota karamin cokali 2, da man kadanya shima karamin cokali 2, sai sinadarin Bitamin E karamin cokali 1. Za’a narka man kadanya da kuma man koko Bota sai a kara bitamin E din a ciki a gauraya. Za’a dura gaba daya a cikin mazubi a ajiye ana shafawa a kan Nankarwar kullum.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Dalilin Da Ya Sa Hukumar NIWA Ta Fara Gyaran Hanyoyin Ruwa A Jihar Legsa November 2, 2025 Manyan Labarai Tsokaci Dangane Da Juyin Mulki A Nahiyar Afirka November 2, 2025 Labarai Barazanar Amurka Kan Kisan Kiristoci A Nijeriya: Tinubu Da Trump Za Su Gana Kwanan Nan — Bwala November 2, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tinubu ya yanke hulɗa da Amurka kawai — Sheikh Gumi
  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Taron APEC Na 2026 Da Za A Shirya A Kasar Sin Zai Bude Sabon Babin Na Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • Maganin Nankarwa (3)
  • Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik
  • ‘An Kashe Masu Zanga-zanga Akalla 500 a Tanzania’
  • Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Gina Gidaje 52 A Babban Birnin Jihar
  • Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
  • Babu wani uzuri da za a yi wa sabbin hafsoshi kan matsalar tsaron Nijeriya — Tinubu