Leadership News Hausa:
2025-05-18@16:09:50 GMT

Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai

Published: 29th, April 2025 GMT

Nijeriya Na Ke Yi Wa Biyayya Ba Wani Ko Jam’iyya Ba – El-Rufai

“Lokacin da abubuwa suka fara lalacewa a lokacin shugaba Buhari, na fito na faɗi gaskiya. Lokacin da tsarin sauya fasalin Naira ya jefa jama’a cikin wahala, na ƙalubalanci gwamnati duk da cewa jam’iyyar APC ce ke kan mulki. Na fi biyayya ga Nijeriya fiye da kowane mutum,” in ji shi.

El-Rufai ya ƙaryata jita-jitar cewa fushinsa da gwamnatin Shugaba Tinubu ne ya sa ya fice daga APC.

Ya ce yana da shekaru 65, kuma babu wani abu da ya rage masa a siyasa da zai nema, sai dai kawai yana jin cewa matsalolin Nijeriya sun yi tsanani sosai wanda ba zai zauna ya yu shiru ba.

“Zan iya yin ritaya cikin kwanciyar hankali, amma Nijeriya na fuskantar babbar barazana. Wannan ba don kaina ba ne – don ceton ƙasa ne,” in ji shi.

Ya kuma bayyana cewa dole a zaɓi shugaban ƙasa mai nagarta da hangen nesa, ba wai kawai din ya fito daga wata jiha ba.

“Matsalolin da muke fuskanta sun fi girman la’akari da inda mutum ya fito. Muna buƙatar shugabanni masu hangen nesa da ƙwarewa don gyara Nijeriya,” ya bayyana.

Da yake magana kan sauya sheƙar wasu ‘yan siyasa zuwa APC, El-Rufai ya ce jam’iyyar SDP tana mayar da hankali ne kan gina goyon baya daga jama’a, ba wai kawai neman manyan ‘yan siyasa ba.

“Gwamna ɗaya yana da ƙuri’a ɗaya ne kawai. Jama’a ne ke yin zaɓe, ba manyan ‘yan siyasa ba,” ya jaddada.

A ƙarshe, El-Rufai ya ce tafiyar SDP tana ci gaba da karɓuwa a dukkanin sassan Nijeriya, ba a yankuna kaɗan kaɗai ba.

“Muna ci gaba da gina goyon baya a faɗin ƙasar nan. Aikin gina ƙasa yana faruwa ne a tsakanin talakawa, ba kawai a kafafen yaɗa labarai ba,” in ji shi.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Ziyara

এছাড়াও পড়ুন:

Mutum ɗaya ya rasu a rikicin manoma da makiyaya a Yobe

Wani rikici da ya ɓarke tsakanin manoma da makiyaya a ƙauyen Chikuriwa da ke Ƙaramar Hukumar Nangere a Jihar Yobe, ya yi sanadin mutuwar mutum ɗaya tare da jikkata wasu.

Rahotanni sun nuna cewa rikicin ya faru ne da yammacin ranar Litinin, 13 ga watan Mayu, 2025 bayan da wani makiyayi ya shigar da shanunsa cikin gonar wani manomi, abin da ya tayar da rikici.

Yajin aiki: Jami’ar KASU ta shiga rudani BUA ya yi alkawarin karya farashin shinkafa

A lokacin da rigimar ta ɓarke, an harbi wani manomi mai suna Babayo Maina Osi da kibiya a goshinsa, wanda hakan ya jikkata shi.

Wata majiya daga ƙauyen ta ce rikicin ya ƙazanta sosai har ya rikiɗe zuwa faɗa tsakanin manoma da makiyaya.

A lokacin wannan faɗa ne aka harbi wani mutum mai suna Usman Mohammed, mai shekara 35 da kibiya, wanda daga bisani ya rasu a Babban Asibitin Nangere.

Jami’an tsaro sun isa wajen domin daƙile rikicin da kuma hana ya ƙara rincaɓewa.

Rahoton ya bayyana cewa an ƙwato shanu biyu, awaki 29 da raguna daga hannun manoman da ake zargi sun ƙwace daga hannun makiyaya.

A yanzu haka, an gayyaci shugabannin ɓangarorin biyu domin tattaunawa da kuma tabbatar da cewa irin wannan rikici bai sake faruwa ba a nan gaba.

Duk ƙoƙarin da wakilin Aminiya ya yi don jin ta bakin kakakin ‘yan sandan jihar, DSP Dungus Abdulkareem, ya ci tura, domin bai daga wayarsa ba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Motar da aka shekara 10 ana tara kuɗinta ta ƙone bayan awa 1 da sayen ta
  • Kyakkyawan Tunanin Kwankwaso Na Kafa Jami’ar Kimiyya Ta Wudil Ta Zama Alkairi Ga Al’umma – Alhaji Abdukadir
  • Ban sauya sheƙa ba, makircin siyasa da ƙarya ake min — Kwankwaso 
  • Tsohon Fira Ministan Gwamnatin Isra’ila Ya Bukaci A Tsige Netanyahu Daga Kan Fira Ministan Isra’ila
  • Iran ta ce babu wata rubutaciyar shawara da ta samu daga Amurka
  •  Fira Ministan Spain: Ba Za Mu Yi Mu’amala Da Isra’ila  Mai Kisan Kiyash
  • Chadi: An Kama Tsohon Fira Minista Kuma Jagoran ‘Yan Hamayyar Siyasa
  • Kwankwaso ya fice daga NNPP tun a 2023 — Shugaban jam’iyya
  • Mutum ɗaya ya rasu a rikicin manoma da makiyaya a Yobe
  • Faɗuwar Farashi: Masu Ɓoye Abinci Don Ya Yi Tsada, Asara Kawai Suke Ƙirgawa , In Ji BUA