Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen
Published: 28th, April 2025 GMT
Mutane da dama daga nahiyar Afirka ne suke cikin mutane kimani 50 wadanda suka rasa rayukansu sanadiyyar hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan wani gidan kaso a lardin Sa’ada na kasar Yemen.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran Al-Masirah yana cewa makaman Amurka sun fada kan wani gidan yarin da aka kebewa yan Afrika, kuma yawansu ya kai 115, amma har yanzun ba’a san yawan wadanda suka rasa rayukansu a gidan yari.
Labarin ya kara da cewa har yanzun ma’aikatan agaji suna aikin ceto a wurin, sannan hotunan da suka fara bayyana sun nuna gawaki da dama. Amma Al-Masirah ta bayyana cewa akalla mutane 68 sun rasa rayukansu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Muhimman Kamfanonin Jiragen Sama A Duniya Sun Farfado Da Zirga-Zirgaf Zuwa Iran
Kamfanin jiragen sama na UAE airlines ko emirate ya sake farfado da zirga zirga zuwa kasar Iran bayan da aka rufe sararin samaniyar kasar Iran a ranar 13 ga watan Yunin da ya gabata.
Jaridar National ta kasar Amurka ta bayyana cewa kasashe da dama a duniya sun dakatar da zirga zirga zuwa JMI saboda yakin da HKI da Amurka suka kai mata daga 13 ga watan zuyi har zuwa kwanaki 12.
Labarin ya kara da cewa kasashen Iraki da Jordan sun dakatar da zuwa kasar Iran saboda yaki kuma saboda gwamnatin Iran ta hana jiragen sama tashi ko kuma zuwa kasar.
A ranar Alhamis ne JMI ta gabata ne hukumomin Iran suka bude sararin samaniyar kasar wanda ya nuna al-amura suna komawa kamar yadda suke bayan yakin kwanaki 12. A halin yanzu dai tashar jiragen saman na Esfahan ne kawai ba’a sake budewa ba, mai yuwa sai kwani m asu zuwa idan an kammala gyare gyaren da yakamata a yi, bayan hare-haren da HKI ta kai mata.