HausaTv:
2025-11-17@07:35:28 GMT

Jiragen Yakin Amurka Sun Kashe Mutane Da Dama A lardin Sa’ada Na Kasar Yemen

Published: 28th, April 2025 GMT

Mutane da dama daga nahiyar Afirka ne suke cikin mutane kimani 50 wadanda suka rasa rayukansu sanadiyyar hare-haren da jiragen yakin Amurka suka kai kan wani gidan kaso a lardin Sa’ada na kasar Yemen.

Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto kamfanin dillancin labaran Al-Masirah yana cewa makaman Amurka sun fada kan wani gidan yarin da aka kebewa yan Afrika, kuma yawansu ya kai 115, amma har yanzun ba’a san yawan wadanda suka rasa rayukansu a gidan yari.

Labarin ya  kara da cewa har yanzun ma’aikatan agaji suna aikin ceto a wurin, sannan hotunan da suka fara bayyana sun nuna gawaki da dama. Amma Al-Masirah ta bayyana cewa akalla mutane 68 sun rasa rayukansu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su

Babban lauya kuma mai kare haƙƙin ɗan Adam, Femi Falana (SAN), ya bai wa ƴan Nijeriya shawara da su kai Gwamnatin Tarayya ƙara don neman a mayar musu da kuɗin fansar da suka biya yayin da aka yi garkuwa da ƴan uwansu. Ya ce gwamnatin ta kasa sauke babban nauyin da kundin tsarin mulki ya ɗora mata na kare rayuka da dukiyoyin ƴan ƙasa.

Falana ya yi wannan jawabi ne a lokacin buɗe sabuwar shekarar Shari’a ta Tsangayar Shari’a ta Jami’ar Yakubu Gowon da ke Abuja. Ya ce yawaitar garkuwa da mutane a sassan ƙasar nan ya nuna gazawar gwamnati wajen tabbatar da kariya kamar yadda kundin tsarin mulki da Yarjejeniyar Afrika kan Haƙƙin Dan Adam suka tanada. Ya kuma soki bambancin yadda hukumomi ke tunkarar lamarin, yana mai cewa ana hanzari ne idan manyan mutane aka sace, amma an bar talakawa cikin tsoro da halin ƙaƙa-niki-ka-yi.

Falana Ya Kai Karar Gwamnatin Tarayya Da Jihohi Kan Yara Da Ba Su Zuwa Makaranta Tsauraran Manufofin Tattalin Arziƙin Tinubu Ya Ƙara Yawan Matalauta – Falana

Falana ya jaddada cewa kai gwamnati kotu zai taimaka wajen kare haƙƙin waɗanda suka biya kuɗin fansa, tare da matsa wa gwamnati ta inganta tsaro cikin gaggawa. Sabon rahoton Hukumar Kididdiga ta Kasa (NBS) ya nuna cewa ƴan Nijeriya sun biya Naira Tiriliyan 2.23 a matsayin kuɗin fansa tsakanin Mayu 2023 zuwa Afrilu 2024. Rahoton Crime Experience and Security Perception Survey (CESPS) na 2024 ma ya nuna cewa fiye da mutum miliyan 2.2 an yi garkuwa da su a wannan lokaci, tare da matsakaicin kuɗin fansa na kusan ₦2.7m ga kowane mutum.

ADVERTISEMENT

A cewar masana tsaro, garkuwa da mutane ya koma kasuwancin da ke samar da riba ga miyagu, lamarin da ke buƙatar tsauraran matakai daga gwamnati tare da ingantaccen tsari da haɗin gwuiwar jami’an tsaro.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara November 16, 2025 Manyan Labarai Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle November 16, 2025 Nazari Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna? November 16, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Falana Ya Shawarci Waɗanda Suka Biya Kuɗin Fansa Su Kai Gwamnati Kotu Don Ta Biya Su
  • Ɗan Najeriya ya kashe mahaifinsa, ya yanki ƙannensa da wuƙa a Amurka
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan
  • NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Da Dama
  • NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Halaka Dama
  • Mahara sun kashe matan aure sun ƙona gidansu a Kano
  • NAF Ta Ragargaza Mafakar Ƴan Ta’adda A Zamfara, Ta Hallaka Dama-Dama
  • Yadda ’yan bindiga suka kashe banga 16 suka sace mutane 42 a Neja
  • ’Yan bindiga sun kashe ’yanga 16 sun sace mutane 42 a Neja
  • Fashi Da Makami: An Yanke Wa ’Yan Nijeriya Hudu Mazauna Birtaniya Hukuncin Daurin Shekara 55 A Gidan Yari