Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
Published: 30th, April 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
Tsaro: Gwamnonin Arewa na shirin dakatar da haƙar ma’adinai
Gwamnonin Arewaci, na shirin dakatar da haƙar ma’adinai a wasu yankuna da ake fama da matsalar tsaro, domin daƙile ayyukan ’yan bindiga da sauran ƙungiyoyin ta’addanci.
Wannan batu ya fito ne daga taron haɗin gwiwa na Gwamnonin Arewa da Majalisar Sarakunan Gargajiya da aka yi a Kaduna daga 1 zuwa 2 ga watan Disamba, 2025.
’Yan sanda sun kama mutum 28 kan zargin lalata mata da yara a Yobe Tsaro: Gwamnatin Kano za ta fara amfani da jirage marasa matuƙa a iyakokintaShugaban ƙungiyar gwamnonin, Gwamna Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya ce lamarin tsaro ya kai wani mataki da ke buƙatar ɗaukar matakin gaggawa.
Ya bayyana cewa wuraren haƙar ma’adinai sun zama mafakar ’yan bindiga, masu garkuwa da mutane da ƙungiyoyin ta’addanci, inda suke tara kuɗi da shirya hare-hare.
Ya ce ’yan ta’adda suna amfani da waɗannan wurare wajen ɓoye makamai da tsara kai hare-hare.
“Dkatar da haƙar ma’adinai ne zai kawo zaman lafiya, dole mu ɗauki wannan mataki.”
Gwamnan ya ce Arewa na fuskantar matsaloli da dama; garkuwa da mutane, Boko Haram, rikice-rikicen karkara da talauci, wanda ke ƙara dagula tsaron yankin.
Ya ce dole a inganta tsaro tare da magance tushen matsalolin.
Ya kuma goyi bayan tsarin ’yan sandan jihohi, inda ya bayyana cewa bai kamata siyasa ta hana ɗaukar matakan tsaro ba.
Taron ya buƙaci Sarakunan Gargajiya da malamai su ƙara ƙoƙarin wanzar da zaman lafiya da fahimtar juna.
Hakazalika, an tattauna yawan yaran da ba sa zuwa makaranta da buƙatar inganta ilimi da sauran ɓangarorin tattalin arziƙi.