Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
Published: 30th, April 2025 GMT
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp.এছাড়াও পড়ুন:
Barin jama’a su kare kansu ne ke rura rashin tsaro — Sojoji
Rundunar Sojin Najeriya, ta ce barin jama’a da aka yi don su kare kansu ne ke rura wutar rikici a Jihar Filato.
Birgediya Janar MA Etsy-Ndagi, Shugaban Hulɗar Sojoji Da Fararen Hula ne, ya bayyana haka a lokacin da yake hira da ’yan jarida a Jos.
An rufe duk makarantu a Kebbi Ma’aikatan lantarki na shirin shiga yajin aiki a faɗin NajeriyaYa ce barin al’umma domin su kare kansu bai haifar da ɗai mai ido ba, illa ƙara tsananta rikice-rikice.
Jihar Filato na fama da rikice-rikice tun daga shekarar 2001, inda mutane da dama suka rasu, wasu kuma suka jikkata.
Wasu ƙungiyoyi a jihar sun yi kiran da a bar jama’a su kare kansu saboda yawan hare-hare da suke fuskanta.
Sai dai Janar Etsy-Ndagi ya ce rikici tsakanin manoma da makiyaya ya koma wani yanayi na ɗaukar fansa, inda kowane ɓangare ke kai wa juna hari.
Ya ce dole ne sojoji su ƙwace dukkanin makaman da ke hannun jama’ar gari domin kawo ƙarshen hare-haren ramuwar gayya.
A cewarsa: “Domin tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyi, dole mu tabbatar an ƙwace makamai daga hannun kowa, kuma babu wanda yake ƙera makami. Hakan ne zai ba da damar samun zaman lafiya.”
Ya ƙara da cewa: “Rikicin ya ɗauki wani sabon salo. Manoma suna zargin makiyaya da lalata musu amfanin gona, makiyaya kuma suna zargin manoma da satar musu shanu.
“Rikici na tsananta. Ba ma goyon bayan al’umma su kare kansu, muna kare jama’ar da ke fuskantar tashin hankali kuma muna ba su goyon baya.”
Ya kuma buƙaci mutanen jihar su zauna lafiya da juna tare da haɗa kai da jami’an tsaro domin tabbatar da zaman lafiya da ci gaban yankunansu.
Ya jaddada cewar Rundunar Sojin Najeriya za ta ci gaba da yaƙar matsalar tsaro a sassan ƙasar nan.