Dubban Mutanen Burkina Faso Sun Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Shugaban Kasa Ibrahim Traore
Published: 1st, May 2025 GMT
Kwanaki kadan bayan wani furuci daga babban jami’in sojan Amurka a Afirka akan shugaban kasar ta Burkina, dubban mutanen kasar sun yi gangami na nuna goyon bayan Kaftin Ibrahim Traore
Gangamin na mutanen kasar Burkina Faso, ya biyo bayan maganganun da su ka fito daga kwamandan sojojin Amurka a Afirka Janar Michael Langley wanda ya zargi sojojin dake Mulki da amfani da ma’adanan kasar saboda kashin kansu maimakon yi wa mutane aiki.
Mahalarta gangamin sun daga kwalaye dake dauke da rubutun yin tir da furucin jami’in sojan na Amurka da kuma nuna goyon baya ga shugaban kasar.
Daga cikin mahalarta gangamin da akwai fitaccen mawakin kasar, Ocibi Joan,wanda ya siffata jami’in sojan Amurkan da dabbar daji mai cin mutane yana mai yin kira a gare shi da kasarsa da su daina yin karya.
Haka nan kuma ya kara da cewa: ” Mutanen Burkina ba su fada da kowa,amma a lokaci daya, ba za su bar masu wawason dukiyar kasarsu ba.”
Wani mutum da ya halarci gangamin Haruna Sawadogo ya fada wa manema labaru cewa, idan suna son ganin bayan Kaftin Traore ne, to su fara ta kan mutanen kasar.
Hakan nan kuma jaddada cewa ba za su bari abinda ya faru da Thoms Sankara ya faru dakanar Troare ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Bayanin Bayan Taron Doha Ya Yi Kira Da A Kafa Runduwar Hadin Gwiwa Ta Kare Kai
A yau Litinin ne dai kungiyoyin kasashen musulmi da na larabawa su ka yi taron gaggawa a birin Doha na kasar Qatar da aka tattauna harin wuce gona da iri da HKI ta kai wa kasar.
Bayanin bayan taron ya kunshi bangarori mabanbanta da su ka hada da daukar matakai kwarara domin taka wa HKI birki akan ta’addancin da take yi, da kuma hanyoyin kare kai anan gaba.
Kungiyar kasashen larabawan yankin tekun fasha ta sake jaddada muhimmancin aiki da dokar kafa rundunar hadin gwiwa ta kare kai daga duk wani wuce gona da iri daga waje.
Bugu da kari, mahalarta taron sun amince da dukar dukkanin matakan dokoki a fagen duniya domin hukunta jami’an HKI da su ka tafka laifukan yaki.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label Name* Email* Website Label Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Burkina Faso: Masu Ikirarin Jihadi Sun Kashe Fararen Hula 50 A Cikin Watanni Hudu September 15, 2025 Fira Ministan Spain: Bai Kamata A Rika Barin “Isr’ila” Tana Shiga Gasar September 15, 2025 Shugaban Kasar Iran Ya Gana Da Sarkin Kasar Qatar A Birnin Doha September 15, 2025 Dan Kasar Iran Mai Kirkira Ya Sami Kyautar Yabo A Kasar China September 15, 2025 Fizishkiyan: Wajibi Ne Musulmi Su Hada Kai Domin Dakatar Da Laifukan HKI September 15, 2025 Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Qatar, Turkiyya, Pakistan Da Labanon A Doha September 15, 2025 Kwamitin Kolin Tsron Kasar Iran Ya Amince Da Yarjejeniyar Da Aka Cimma Da Hukumar IAEA September 15, 2025 Jami’in Kasar Yemen Ya Aike Da Sako Ga Mahalarta Taron Birnin Doha Na Kasar Qatar September 15, 2025 Yawan Mutanen Da Suka Yi Shahada Sakamakon Kisan Kiyashin ‘Yan Sahayoniyya A Gaza Ya Kusaci 65,000 September 15, 2025 Gwamnatin Sudan Ta Ce: Babu Sulhu Da ‘Yan Tawayen Kasar Na Kungiyar Rapid Support Forces September 15, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci