Dubban Mutanen Burkina Faso Sun Yi Gangamin Nuna Goyon Bayan Shugaban Kasa Ibrahim Traore
Published: 1st, May 2025 GMT
Kwanaki kadan bayan wani furuci daga babban jami’in sojan Amurka a Afirka akan shugaban kasar ta Burkina, dubban mutanen kasar sun yi gangami na nuna goyon bayan Kaftin Ibrahim Traore
Gangamin na mutanen kasar Burkina Faso, ya biyo bayan maganganun da su ka fito daga kwamandan sojojin Amurka a Afirka Janar Michael Langley wanda ya zargi sojojin dake Mulki da amfani da ma’adanan kasar saboda kashin kansu maimakon yi wa mutane aiki.
Mahalarta gangamin sun daga kwalaye dake dauke da rubutun yin tir da furucin jami’in sojan na Amurka da kuma nuna goyon baya ga shugaban kasar.
Daga cikin mahalarta gangamin da akwai fitaccen mawakin kasar, Ocibi Joan,wanda ya siffata jami’in sojan Amurkan da dabbar daji mai cin mutane yana mai yin kira a gare shi da kasarsa da su daina yin karya.
Haka nan kuma ya kara da cewa: ” Mutanen Burkina ba su fada da kowa,amma a lokaci daya, ba za su bar masu wawason dukiyar kasarsu ba.”
Wani mutum da ya halarci gangamin Haruna Sawadogo ya fada wa manema labaru cewa, idan suna son ganin bayan Kaftin Traore ne, to su fara ta kan mutanen kasar.
Hakan nan kuma jaddada cewa ba za su bari abinda ya faru da Thoms Sankara ya faru dakanar Troare ba.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Mutane 44 Suka Mutu Bayan Mamakon Ruwa Da Aka Tafka A Beijing
Ruwan sama kamar da bakin kwarya tare da iska mai karfi da aka tafka a kwanan nan ya yi sanadin mutuwar mutane 44, yayin da wasu tara suka bace a birnin Beijing, kamar yadda aka bayyana a wani taron manema labarai da ya gudana a yau Alhamis.
A yayin taron manema labarai da gwamnatin birnin Beijing ta gudanar a yau game da rigakafin ambaliyar ruwa da bayar da agajin gaggawa, an bayyana cewa, bala’in ambaliyar ruwan da ya auku kwanan nan ya shafi mutane sama da 300,000 tare da lalata gidaje 24,000 a birnin Beijing.
Sai dai, yanzu haka birnin na Beijing na kara kokarin farfado da wutar lantarki, da share tituna, da kai muhimman kayayyaki ga mazauna yankin da suka rasa matsugunansu, sakamakon ambaliyar ruwa da zabtarewar kasa da suka auku sanadin mamakon ruwan sama mai karfi da aka tafka a tsaunukan da ke wajen birnin. (Mai fassara: Abdulrazaq Yahuza Jere)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp