HausaTv:
2025-09-18@09:08:53 GMT

Kissoshin Rayuwa: Imam Al-Hassan 114

Published: 28th, April 2025 GMT

114-Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na kissoshin rayuwa shiri wanda yake kawo maku kissiso da suka zo cikin alkur’ani mai girma ko kuma cikin wasu littafan wadanda suka hada da littafin dastane rastan, ko kum littafin mathnawi na maulana Jalaluddeen rumi.

Ko kuma cikin wasu littafan da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu na yau.

///… Masu sauraro idan kuna tare da mu a cikin shirimmu da ya gabata, a kuma cikin sirar Imam Al-hassan limami na biyu daga cikin limamai masu tsarki daga iyalan gidan manzon All..(s), kuma da na farko ga Fatimah(s) diyar manzon All..(s), sannan jikansa na farko.

A cikin shirimmu da ya gabata, mun yi maganar yadda Khalifa Uthman ya wanye da Ammar dan Yasir ( R), mun ji yadda Ammar ya tashi da shi da iyayensa suka fara karban musulunci a Makka, da kuma yadda suka yi shahada a hannun Abu Jahal, sannan yadda Ammar ya kubuta daga sahrrinsa bayan ya fadi abinda suke so, ba da sonsa ba. Amma alkur’ani ya sauka yana tabbatar masa da Imani.

Sannan munji yadda manzon All…(s) yake himmantuwa da al-amarin Ammar don Yasir ba don iyayensa su ne shahidar na farko a makka ko a musulunci ba, sai har da cewa yana da Ikhlasi da kuma tsoron All… don haka manzon All..(s) yana girmama Ammar dan yasir ne saboda tsoron All…da kusancinsa da shi. Saboda a hadisan da aka karbo daga gareshi (s) dangane da Ammar suna maganane a kansa, kamar . Inda yake cewa. All..kayi fushi da wanda yayi fushi da Ammar. Sannan manzon All..yayi masu alkawali da shiga aljanna tun suna Makka, inda yake cewa: Ya ku yan gidan yasir kuyi hakuri laillai makomarku aljanna ce.

Sannan munji yadda ya narke a cikin son Aliyu dan Abitalib (a) bayan wafatin manzon All… Da kuma yadda Khalifa Uthman ya sa aka dakeshi har ya suma, har sau biyu.

A cikin shirimmu nay au zamu yi magana kan yadda aka yi wa Imam Alhassan (a), dangane da wai yana son Khalifa Uthman, kuma yana bakin ciki da kissansa, wanda Taha Hussain ya kawo a cikin littafinsa –Fitnatul Kubra.

Wasu malaman tarihi sun ruwaito hadisan kariya sun jinginawa Imam Alhassan dan Aliyu dan Abitalib (a) dangane da Khalifa Uthman, sun riya cewa Imam Alhassan (a), yana daga cikin masoyan khalifa Uthman, kuma yana sonshi har cikin zuciyarsa. A cikin rayuwarsa da kuma bayan kashe shi.

Dr Taha Hussain yana daga cikin wadanda suka tafi a kan wannan ra’ayin, inda yake fada cikin littafinsa Ftnatul Kubra, yana cewa” Hassan (a) bai gushe ba yana son Uthman, ya kasance masoyin Uthman ne da gaske, sai dai bai zare takobi don neman fansar jininsa ba, don bayan ganin hakan hakkinsa ne, wasu lokutan yakan wuce gona da sonsa Uthman har sai da a fadawa babansa (Imam Ali) abinsa dai dace ba. Kamar yadda, masu ruwaye sun ruwato daga Ali (a) ya wuce dansa Imam Hassan (a) yana alwala, sai ya ce masa, ka kyautata alwala, sai ya bashi wannan amsar mai daci, inda wai yana ce masa (hakika kun kashe wani mutum a jiya yana kyautata alwala). Sannan Aliyu (a) bai kara wani abu ba sai wannan Kalmar, (hakika All..ya tsawaita sonka ga Uthman).

Sai dai idan muka dubi wannan ruwayar wanda Taha Hussain ya kawo shi don karfafa ra’ayinsa, hakaka Balaziri ya ruwaitoshi, dada Mada’in, a cikin littafinsa ‘Al-ansabul Al-ashraaf JZ 5 sh 81, Shi wannan Mada’ini an sanshi da kin iyalan gidan manzon All..(a) , wato nasibi ne, sannan an sanshi da kirkiro hadisai na yabo da goyon baya ga banu umayya, yana jinginawa manzon All..(s).

Kuma manufarsa da kirkiro wannan hadisin ita ce tsarakaka banu Umayya, ta jikan manzon All..(s) mai tsari Imam Hassan (a). Don ya nuna cewa salihan bayi kamar Jikan manzon All..(s) yana son Uthman. Banda raunin sanadin wannan hadisin, ga wasu karin abin lura a cikinsa.

01- Idan har da gaskiya ne, Imam Ali (a) ya na son yi wa dansa gyara a alwalarsa, to me yasa Imam Hassan (a) zai fada masa wannan kalmomi masu daci?, Sannan A lokacinda aka kashe Khalifa Uthman, Imam Hassan (a) yana dan shekara 32 a duniya bai iya alwala ba? Imam Hassan (a) ya tashi a gaban manzon All..(s) yana dan shekara 7 a duniya, kakansa manzon All..(s) ya kaura daga wannan duniya, amma bai koyawa jikansa na farko, alwala ba?

Sai ya yana dan shekara fiye da 30 ne babazansa zai koya masa al-walah, ? ko way a san wannan ba haka yake ba.

Sannan ina hadisin nan da aka bayyana cewa Imam Hassan da Hussain (a) suka ga wani dattijo bai iya alwala ba, sai tunda su yara ne a lokacin sai suka yi dubara ta kyautata masa al-walansa, inda dayansu yayi alwala irin na dattijo sai dayan kuma yayi alwala mai kyau, sai dattajan ya gano cewa da shi ake nufi sai ya gyara alwalansa. ?

Wanda ya nuna cewa Imam AlHassan da Alhussain (a) suna koyawa mutane alwala tun kakansu manzon All..(s) ya na da ransa a duniya.

02-Sun ce Imam Alhassan (a) yana daga cikin masu kare khalifa Uthman a lokacinda yan tawaye suka yiwa gidansa kofar rago, kuma yana haka tare da Umurnin babansa Imam Ali(a) ne, to ta yaya a wannan hadisin Imam Hassan yana zargin babansa da kashe Uthman? .

Al-hali mun san cewa Imam Hassan yana tare da mahaifinsa, a yakin Jamal da kuma yakin siffin, a lokacinda yayi wadanda suke tuhumarsa da kashe Khalifa Uthman, suna cewa suna yakarsa ne don daukar fansar jinin Uthman. Imam Alhassan da Alhussain duk suna tare da mahaifinsu a wadannan wurare suna goyon bayansa, kuma basa tuhumarsa da kashe Khalifa Uthman.

Wannan ya tabbatar mana cewa, Mada’ini ya kirkiro wannan hadinsin ne tare da manufar da muka bayyana.

03-Ayyukan Uthman ne suka kasheshi, ya dorawa mutanen Masar da Kufa danginsa suka yi ta kashe su da kuma zaluntarsu, sun kawo kokari a Madina ya ki amsa korafe-korafensu, a lokacinda ya amsa kiran mutanen masar, daga baya ya warware.

A nan sai suka ce ko ya sauka daga khalifanci ko kuma su kasheshi, da yaki sauka suka kashe kashe. Imam Ali (a) bai da hannu ko kadan wajen kissan Khalifa Uthman, ta yaya dansa Imam Hassan (a), kamar yadda ya zo a cikin Hadisin Mada’ini,  zai tuhum- babansa da kissan Uthman, kamar yadda wannan hadisin yake cewa,  ya san cewa ba haka ne ba.?  

Amma abinda ya faru kafin kissan Khalifa na uku,  shi ne cewa, Khalifa Uthman ya aikata abubuwan da dama wadanda basu dace ba, har sai ya kai ga ba wani kare shi a cikin sahabban manzon All..(s) a Madina.

Hatta, talha da zubai da Abdurrahman bin Auf, wanda ya dorashi kan khalifancin, kuma  wadanda ya yi masu ni’imoni, masu yawa, sun dawo daga rakiyarsa.

Duk sun dawo suna fushi da shi. Ta yaya wadannan sahabban manzon All..(s) da salihan bayi daga cikinsu wadanda muka ambata a baya, kamar Abuzar, Ammar, Abdullahi dan Mas’ud da Aliyu dan Abi talib da sauransu duk suna aibata shi. Amma sai Imam Hassan (a) ya zama ya na sonsa?. Ba zai yu ba.

Don haka tare da wannan zamu ga cewa, ba kuma wata kima ga wannan Hadisin a sanadinsa da mataninsa. Abin mamaki shi ne, ta yaya Taha Hussain bai yi bincike mai zurfi a cikin wannan hadisin ba har ya zo ya fada cikin wannan tatsuniyar.

Don haka a lokacinda ayyukan Uthman suka zama abin tattaunawa a ko ina a Madina da sauran manya manyan garuruwan musulmi, sai zabubbu cikin sahabban manzon All..suka taro suka yi shawara, suka kuma yanke shawara kan cewa dole ne su sauya shugabancin musulmi. Don haka suka aika wasiku zuwa manya manyan kasashen musulmi suna neman taimakonsu da makamai da kuma sojoji.

Ga Nassin abinda ya zo cikin daya daga cikin wasikun da suka rubuta. Wannan wasikar zuwa ga mutanen Masar.

{Daga muhijiruna na farko, da sauran shura, zuwa ga wadanda suke kasar Masar, daga sahabbai da kuma masu binsu wato (tabi’ina), Bayan haka:

Da ku zo wajemmu, ku kawo dauki ga khalifancin manzon All..(s) kafin ma’abutanta, su kwaceta su kwaceta, to lalle lillafin All.. an sauya shi (ba’a aiki da shi),kuma sunnar manzon All..(s) an sauya ta, kuma hukunce, hukuncen khalifofi biyu an sauyasu, Muna hada All…kan cewa duk wanda ya karabta wannan takardan, daga cikin sahabban manzon All…(s)  da suka saura, da mabiyansu da kyautatawa, face ya taho mana, don ya karbo mana hakkimmu, kuma mu bashi hakkinsa, to ku zo mana idan har kunyi Imani da All..da ranar lahirah, (ku zo ku) ku tsaida gaskiyar bisa tafarki bayyananniya wanda manzonku (s) ya barku a kanta, kuma wacce khalifofi suka barku a kanta, an rinjayemu kan hakkimmu, an mamaye dukiyarmu, kuma an shiga tsakanimmu da al-amarimmu, kuma khalifanci bayan bayan bayan manzon All..(s) ta kasance khalifancin annabi, kuma mai rahama, amma a yau ta zama mulki na zalunci, wato wanda ya sami rinjaye ya ci.. …}.

Wannan kadan Kenan daga wasikar da sahabbai muhajirun suka rubutawa suran sahabban a wasu wurare, kuma Ibn Kutaiba ya kawo ta a cikin littafinsa Al-imama wassiya shafi na 35.

Sannan wadan wasikar ta ambaci abubuwa da dama wadanda suka fadawa daular musulunci da musulmi saboda mulkin Uthman.

উৎস: HausaTv

কীওয়ার্ড: wannan hadisin

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu

Sojoji biyu sun ji rauni bayan wani harin kwanton baya da ’yan bindiga suka kai kan ayarin motocin Kwamandan kwamandan Rundunar Sojoji ta 382 Ƙaramar Hukumar Faskari ta jihar Katsina.

Lamarin ya faru ne a ƙauyen Ruwan Godiya, kan hanyar Sheme–Kankara, lokacin da tawagar Operation Fansan Yamma (OPFY) ke wucewa.

Ganau sun ce sojojin na kan hanyar ziyartar sansanonin sojoji a yankunan Faskari da Mabai da Ɗan Ali lokacin da aka kai musu hari.

Sai dai sun yi nasarar tunkarar ’yan bindigar har suka kuvuta, kodayake sojoji biyu sun samu raunuka na harbi kuma aka kai su asibitin sojoji domin jinya.

An kai wa sojojin harin ne a rana ɗaya da shugabannin al’ummar Faskari suka zauna da wakilan ’yan bindiga domin rattaba hannu kan yarjejeniyar zaman lafiya.

’Yan bindiga sun sace mutum 40 a masallaci a Zamfara Hauhawar farashi ya ragu a watan Agusta — NBS

Hakan ya sanya Faskari zama ƙaramar hukuma ta baya-bayan nan da ta shiga irin wannan sulhu bayan ƙananan hukumomin Ɗanmusa da Jibia, Batsari da Ƙanƙara, Kurfi da Musawa.

Yarjejeniyar na neman kawo ƙarshen tashin-tashina, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a jihar.

Amma akwai shakku kan ɗorewar ta, domin wasu daga cikin shugabannin ’yan bindigar sun bayyana cewa sulhun ya shafi ƙananan hukumomin da suka shiga yarjejeniyar kawai, lamarin da ya janyo tsoron cewa sauran wuraren da ba su rattaba hannu ba, suna iya ci gaba da fuskantar hare-hare.

Wasu mazauna Ruwan Godiya sun ce ayyukan ’yan bindiga na ƙara ta’azzara a sassan Katsina duk da yarjejeniyar sulhun da aka ƙulla da wasu daga cikin shugabanninsu.

Masana sun bayyana cewa hakan ya nuna raunin irin waɗannan tsare-tsare na sulhu, tare da tabbatar da buƙatar ƙarin sa-ido a yankunan da ke fuskantar barazana.

Sulhun Faskari da ’yan bindiga

Ƙaramar Hukumar Faskari ta zama ta baya-bayan nan a Jihar Katsina da ta shiga yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga, domin kawo ƙarshen kashe-kashe, garkuwa da mutane da kuma ƙaura da ake fama da su a yankin.

Kamar sauran sulhunan da aka kulla a ƙananan hukumomi guda shida, sharuddan yarjejeniyar sun ba wa ’yan bindiga damar shiga garuruwa da kasuwanni da asibitoci.

Haka kuma, za su sako duk wanda aka yi garkuwa da shi ba tare da sharaɗin ba. A sakamakon haka, al’umma za su iya komawa gona da kasuwanni cikin kwanciyar hankali ba tare da fargabar farmaki ba.

Yarjejeniyar ta biyo bayan taron al’umma da aka yi a Faskari, inda fitaccen shugaban ’yan bindiga, Ado Aliero, wanda ake nema ruwa a jallo, ya tabbatar wa manoma tsaronsu.

“Daga yau kowa ya koma gona cikin kwanciyar hankali; ba abin da zai faru a Faskari baki ɗaya,” in ji Aliero cikin wani bidiyo da Aminiya ta gani.

Aliero ya ɗora laifin rushewar yarjejeniyar da aka yi a baya kan cafke ɗansa, yana mai cewa ya bi duk hanyoyin lumana, amma abin ya gagara, kafin ya koma tayar da hankali.

A wani bidiyo daban kuma, wani ɗan bindiga da aka gani sanye da rigar harsashi ya zargi hukumomi da nuna wariya da rashin adalci, yana mai cewa sulhu na gaskiya zai tabbata ne kawai idan aka yi adalci ga kowa.

Sai dai duk da rahotannin da ke cewa jami’an gwamnati da na tsaro sun halarci taron, gwamnatin Jihar Katsina ta nesanta kanta daga wannan yarjejeniyar.

Akwai masu kawo cikas — Gwamna Raɗɗa

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umar Raɗɗa, ya ce duk da irin ƙalubalen tsaro da ake fuskanta, gwamnatinsa na samun ci-gaba, sai dai akwai masu ƙoƙarin kawo cikas.
Ya bayyana haka ne a wani taron shawarwari da aka gudanar a Katsina ranar Lahadi, wanda ya tattaro manyan masu ruwa da tsaki ciki har da sarakunan gargajiya da shugabannin siyasa da shugabannin tsaro da masana, ’yan kasuwa da shugabannin addini.
Gwamnan ya ce tsaro ne ginshiƙin ajandar ci-gabansa tare da ilimi da noma da kiwon lafiya da kuma tallafa wa ƙanana da matsakaitan ’yan kasuwa.
Ya sanar da cewa gwamnati za ta gina gidaje 152 ga iyalan da aka raba da muhallansu a Jibia, tare da shirya shirin tallafa wa tubabbun ’yan ta’adda da suka domin kada su koma ɓarna.
Haka kuma ya yaba wa jami’an sa-kai da ƙungiyoyin tsaro na gari da suka taimaka wajen dawo da ƙwarin gwiwa a tsakanin jama’a.
Cikin manyan da suka halarci taron akwai tsohon Gwamna Aminu Bello Masari da dattijo Sanata Abu Ibrahim da fitaccen dan kasuwa Alhaji Ɗahiru Mangal da Sarkin Daura Alhaji Faruk Umar Faruk da tsohon Ministan Sufurin Jiragen Sama, Hadi Sirika, Ministan Gidaje Arc. Ahmed Ɗangiwa, da kuma Hadiza Bala Usman mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsare-tsare.
Sauran sun hada da tsohon Daraktan DSS Alhaji Lawal Daura, tsohon Daraktan NIA Ambasada Ahmed Rufai, tsohon Shugaban Kamfanin na NNPC Injiniya Abubakar Yar’adua da Babban Alƙalin jihar Alhaji Musa Ɗanladi, da kuma manyan hafsoshin soja da dama da suka yi ritaya.
Hakazalika, an samu halartar manyan jami’ai, malamai daga jami’o’i da ƙungiyoyin ƙwadago da ƙungiyoyin farar hula da ’yan kasuwa da sauran shugabanni daga sassa daban-daban na jihar.
Gwamna Radda ya jaddada cewa zai ci gaba da karɓar suka da shawarwari daga masu kishin ƙasa, tare da kira ga haɗin kai domin shawo kan matsalolin tsaro da tattalin arziki da jihar ke fama da su.

Abin da mahalarta suka ce

A nasa vangarenm Mataimakin Gwamnan Jihar Katsina, Faruk Lawal Joɓe, ya bayyana cewa gwamnatin Raɗɗa ta samar da sama da ayyuka 35,903 a fannoni daban-daban ta karkashin manufar “Gina Makomarka.”

Joɓe ya bayyana ce an samar da ayyukan ne ta hanyar ɗaukar malamai da shugabannin unguwanni da jami’an tsaro na sa da mafarauta da sauransu domin su riƙa taka rawa wajen wanzar da zaman lafiya.

Ya kuma yi ƙarin haske kan aikin Sabunta Birane na Katsina State Urban Renewal da ya lashe Naira biliyan 74.9 wanda ya shafi manyan ayyuka a Daura da Funtua da Katsina.

Ayyukan sun haɗa da gina sabuwar hanyar Eastern Bypass mai tsawon kilomita 24, titi mai hannu biyu a cikin Katsina, gyaran tituna a Daura da Funtua, da kuma kammala wasu muhimman hanyoyin karkara.

A nasa jawabin, Kwamishinan Tsaro na Cikin Gida, Dakta Nasir Muazu, ya ce gwamnatin Raɗɗa ta ɗauki matakin rashin tattaunawa da ’yan bindiga.

Ya ce abubuwan da ke haifar da ta’addanci sun haɗa da son zuciya da rikice-rikicen albarkatu da sauyin yanayi, da kuma rashin adalci a cikin al’umma.

Ya ƙara da cewa daga 2011 zuwa 2015 matsalar ta tsaya a ƙananan hukumomi biyar, amma ta bazu zuwa 25 a lokacin tsohon Gwamna Aminu Masari bayan shirin afuwa ya faskara.

Kwamishinan ya bayyana cewa hare-haren soji sun lalata maɓoyar ’yan bindiga da dama, sun buɗe manyan hanyoyi, sannan mutum 628 da suka tsira daga hare-hare sun samu kulawar lafiya a bana.

Ya ce yanzu dakarun Community Watch, masu aikin sa-kai da ’yan banga suna mara baya ga jami’an tsaro da ke amfani da jirage marasa matuƙa da makamai da motocin aiki.

Shugaban Ƙungiyar ƙwadago (TUC) na jihar, Muntari Abdu Ruma, ya gargaɗi gwamnati ta yi taka-tsantsan da yarjejeniyar zaman lafiya da ’yan bindiga lura da yarjejeniyar Kankara ta 2016 da ta gagara.

Haka kuma, shugaban ƙungiyoyin farar hula na jihar, Malam Abdulrahman Abdullahi, ya ce akwai buƙatar ƙarin haɗin kai tsakanin jihohin Arewa maso Yamma wajen yaki da ’yan bindiga. Ya yi nuni da cewa ziyarar da dattawan Katsina suka kai wa Shugaba Bola Ahmed Tinubu a bisa jagorancin Gwamna Raɗɗa ta fara haifar da sakamako mai kyau a Ƙanƙara da Faskari, amma dole a ci gaba da ayyuka cikin tsari.

A nasa ɓangaren, Sanata Ibrahim Tsauri na jam’iyyar adawa PDP, ya ce taron ya fi karkata wajen bayyana nasarorin gwamnati fiye da ba wa mahalarta dama su yi sharhi.

Duk da haka ya ce idan aka ci gaba da irin waɗannan taruka, za su iya kawo sauyi ga jihar bayan shekaru 15 na ƙalubale.

An ce mahalarta taron sun yi alkawarin mara wa gwamnati baya wajen shawo kan matsalar samari, musamman shaye-shaye da sauran laifuka.

Sauran muhimman shawarwarin sun haɗa da haɗe hanyoyin sadarwa a wuri guda da nufin samun nasarar wannan abu da aka sanya a gaba.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Mataimakin Gwamnan Zamfara Ya Jajantawa Al’ummar Gumi
  • Gobara ta kashe manyan jami’an hukumar FIRS 4 a Legas
  • Gwamnati ta ƙaddamar da jiragen ruwa na zamani 20 a Sakkwato
  • An kama ɗaya daga cikin manyan kwamandojin IPOB
  • Gwamna Namadi Ya Taya Malaman Makarantu Da Suka Yi Fice A Jihar Murna
  • Tinubu bai shirya gudanar da sahihin zaɓe ba a 2027 – Buba Galadima
  • Jihar Jigawa Ta Amince Da Karin Kasafin Kuɗi Na Naira Biliyan 75 Na Shekarar 2025
  • NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
  • ’Yan bindiga sun kai wa sojoji hari a ranar da ake zaman sulhu
  • Dole sai mun tantance wa’azi kafin a yi —Gwamnan Neja