Aminiya:
2025-05-18@17:12:02 GMT

’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno

Published: 27th, April 2025 GMT

Mayakan Boko Haram sun halaka mutum goma sha biyu da jikkata karin biyu bayan wani hari da suka kai kan kauyen Bokko Ghide a Karamar Hukumar Goza ta Jihar Borno.

Wakilinmu ya ruwaito cewa cikin wadanda aka kashe akwai ’yan sa-kai biyu da wasu mutum 10 da suka fita debo itacen girki.

Sulhu da ’yan bindigar Katsina: Gaba aka ci ko baya? Abubuwan da suka faru yayin jana’izar Fafaroma Francis

Sarkin Gwoza, Alhaji Mohammed Shehu Timta, wanda ya tabbatar da faruwar lamarin, ya ce mayakan sun yi wa ’yan sa-kan kwanton bauna a kan hanyar Kirawa da ke gudunmar Pulka.

“Sun fita neman itace ne a jeji a ranar Asabar, yayin da yaran [mayakan Boko Haram] suka yi musu kwanton bauna, inda suka kashe mutum 10 sannan wasu suka ji munanan raunuka.

“Mun binne mutum 10 sannan biyu da suka jikkata an mika su asibiti.

“Abin takaici shi ne biyu daga cikin yan sa-kai sun sadaukar da rayuwarsu wajen kare mutanenmu wadanda aka kashe ranar Juma’a.”

Bayanai sun ce harin ya auku ne yayin da ake kokarin ganin an mayar da jama’ar yankin garuruwansu don su ci gaba da rayuwa, bayan kwashe shekaru da dama suna gudun hijira a wasu wurare saboda hare-haren na ’yan Boko Haram.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Boko Haram jihar Borno

এছাড়াও পড়ুন:

UNICEF Ya Ce; Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara 45 Cikin Kwana Biyu Kacal A Gaza

Asusun kula da kananan yara “UNICEF” na Majalisar Dinkin Duniya ya sanar da cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kashe yara 45 a Gaza cikin kwanaki biyu kacal

Asusun kula da kananan yara na Majalisar Dinkin Duniya UNICEF ya bayyana cewa: Sojojin mamayar Isra’ila sun kashe kananan yara 45 a Zirin Gaza a cikin kwanaki biyun da suka gabata, kuma wani abin tunatarwa shi ne cewa: Yara a Gaza na shan wahala da farko, suna fama da yunwa kowace rana kuma suna fuskantar hare-haren wuce gona da iri da muggan makamai kan mai uwa da wabi.”

A cikin wata sanarwa da Asusun ya fitar a ranar Juma’a, ya jaddada yi kira da a kawo karshen wahalhalu da kashe-kashen yara a kullum.

A nata bangare, Hukumar Lafiya ta Duniya ta bayyana cewa: “Hare-haren sojojin gwamnatin mamayar Isra’ila na ci gaba da yin mummunan tasiri ga cibiyoyin kiwon lafiya, ciki har da asibitin Turai na Gaza da ke Khan Yunis, wanda yanzu ya daina aiki.”

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa
  • ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno
  • Mutum 3 Sun Rasu, Wasu Sun Jikkata Yayin Da Bama-bamai Suka Tashi A Hanyar Borno
  • Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a Borno
  • UNICEF Ya Ce; Sojojin Mamayar Isra’ila Sun Kashe Kananan Yara 45 Cikin Kwana Biyu Kacal A Gaza
  • Mutum 3 sun mutu, 21 sun jikkata a turmutsitsin karɓar kuɗin tallafi a Borno
  • Cikin makonni kaɗan Obasanjo ya murƙushe Boko Haram — Atiku
  • Ɗaukar fansa: Sojoji sun ragargaji Boko Haram a Dajin Sambisa
  • Mutum 10 sun rasu kan rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Mutum 10 sun rasu sakamakon rikicin gona da dabbobi a Filato