Sanarwar ta kuma zayyana matakan fadada adadin shaguna masu iya mayar da kudin haraji domin bunkasa samar da kayayyaki da hidimomi masu ruwa da tsaki.

 

Haka kuma, za a kara kafa kantunan sayar da kayayyaki masu mayar da kudin haraji ga baki a manyan wuraren sayayya da gefen tituna da wuraren bude ido da shakatawa da wuraren raya al’adu da filayen jiragen sama da otel-otel da tashoshin tafiye-tafiye.

(Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro

Daga Aliyu Muraki 

Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa ya ce gwamnonin Arewa sun amince su sayi na’urorin zamani na tsaro da kuma daukar matasa aiki don tallafawa ayyukan tsaro domin magance matsalolin rashin tsaro a yankin.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a zaman Majalisar Zartarwa ta Jihar da aka gudanar a Lafia, babban birnin jihar.

Gwamna Abdullahi Sule, wanda shi ne shugaban kungiyar gwamnonin Arewa ta Tsakiya, ya ce an cimma wannan matsaya ce a taron gwamnonin Arewa da aka yi a Kaduna kwanan nan.

 

A cewarsa, gwamnonin Arewa sun amince cewa kowace jiha za ta rika bada gudummawar Naira Biliyan Daya a kowane wata na tsawon shekara guda domin samar da kudin da zai taimaka wajen magance matsalolin tsaro a yankin.

Ya ce kwamitin gwamnonin Arewa zai gina sakatariyarsa a Kaduna, inda gwamnonin Arewa goma sha tara suka bayar da Naira Miliyan Dari Dari na tsawon shekara guda.

Gwamna Abdullahi Sule ya kuma yi karin bayani kan dakatar da ayyukan hakar ma’adinai a jihar Nasarawa, inda ya bayyana cewa wannan dakatarwar ba haramta dukkan ayyukan hakar ma’adinai na tsawon watanni shida ba ce, an dakatar da bayar da sabbin lasisi ne, har sai an kammala tantance sahihan masu hakar ma’adinai.

Manufar tantancewar ita ce gano masu hakar ma’adinai na gaskiya da kawar da masu hakar ma’adinai na fasa-kwauri wadanda ba sa kawo kudaden shiga ga jihar, tare da haifar da matsalolin tsaro.

Gwamnan ya bayyana cewa kasancewar masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba a jihar ta zama mafakar ‘yan bindiga, masu garkuwa da mutane da sauran matsalolin tsaro, wanda hakan ya sa aka bukaci tsauraran dokoki da ingantaccen tsari.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An dakatar da Shugaban Karamar Hukumar Lafia
  • Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Kasashen Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Duk Wani Rikici
  • Iran Da Kasashen Afrika Sun Daura Dammarar Karfafa Alakar Kimiyya Tsakaninsu
  • Tawagar Majalisar Amurka ta iso Nijeriya Don Bincika Zargin Tauye Haƙƙin Addini
  • Mutum 5 sun rasu sanadin gobara da faɗa wa rijiya a Kano
  • Iran Ta Zama Zakaran  Duniya A Wasan “Taekwondo” Na Masu Shekaru Kasa Da 21
  • Kwastam ta kama jirgin ruwan Brazil ɗauke da hodar iblis a Legas
  • Ma’aikatar Shari’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudin 2026 a Gaban Majalisa