Sanarwar ta kuma zayyana matakan fadada adadin shaguna masu iya mayar da kudin haraji domin bunkasa samar da kayayyaki da hidimomi masu ruwa da tsaki.

 

Haka kuma, za a kara kafa kantunan sayar da kayayyaki masu mayar da kudin haraji ga baki a manyan wuraren sayayya da gefen tituna da wuraren bude ido da shakatawa da wuraren raya al’adu da filayen jiragen sama da otel-otel da tashoshin tafiye-tafiye.

(Fa’iza Mustapha)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA

Assalamu alaikum masu sauraro barkammu da warhaka barkammu da sake saduwa a cikin shirimmu na duniyar mu a yau. Shiri wanda yake kawo maku labarai masu muhimmanci a makon da ya gabata wadanda suka shafi siyasa, tattalin, arziki, zamantakewa tsaro da sauransu, inda muke masu Karin bayani sannan daga karshe mu ji ra’ayin masana dangane da su da fatan masu sauraro zasu kasance tare da mu a cikin shirimmu nay au

/////… Madalla, masu sauraro zamu fara shirimmu da labarimmu na farko wanda yake cewa majalisar gwamnoni a hukumar IAEA ta amince da wani kuduri na takurawa JMI a taron da ta yi a ranar Alhamis 22 ga watan Nuwamban da muke ciki. Kuduri wanda kasashen E3 ko Traiko na kasashen Turai wato Ingila, Faransa da Jamus suka gabata, inda a ciki suka bukaci majalisar ta bukaci Iran ta gaggauta bayyana yadda tayi da Ruwan makamashin Yuranium wanda ta tashe kafin yakin kwanaki 12 a cikin wantan Yunin da ya gabata, wato yakin da Amurka da HKI suka kaiwa kasar Iran karkashin jagorancin Amurka.

Har’ila yau kudurin ya bukaci JMI ta bude kofa ga ma’aikata masu bincike na hukumar IAEA su shiga kop ina a cikin kasar don binciken, na ba zata saboda gano irin ayyukan da take gudanarwa a shirinta na makamashin Uranium.

Kudurin wanda ya wuce da dakyer ya sami amincewa kasashe 19 banda su kasashen 3 da suka gabatar da ita, ta sami wakilan kasashe 12 wadanda basu halarci zaman ba.

Kudurin ya nuna cewa kasashen 3 da kuma Amurka suna son amfani da hukumar IAEA don cimma wasu manufofinsu dangane da Shirin makamashin nukliyar kasar Iran wadanda suka kasa cimmasu a yakin kwamani 12 da suka kaiwa JMI.

Abbas Aragchi ministan harkokin wajen kasar Iran ya yi allawadai da abinda majalisar gwamnonin suka gabatar a kan Shirin nukliyar kasar Iran. Ya kuma kara da cewa JMI ba zata dauki kudurin da wani muhimmanci ba. Ya kuma bayyana kudurin a matsayin wanda baya bisa doka.

Ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran a nan Tehran ta bayyana cewa, kusan rabin gwanonin majalisar sun yi watsi da kudurin basu amince da shi ba, kama daga wadanda suka kauracewa zaman da wadanda suka ki amincewa da shi da kuri’unsu da kuma wadanda sula halarci taron amma suka ki kada kuri’unsu.

Ma’aikatar ta kara da cewa kudurin ya sabawa asalin ka’idojin yarjeniyar NPT ta hana yaduwar makaman Nukliya a duniya, wacce ta bawa kasashen duniya damar sarrafa makamashin nukliya don ayyukan zaman lafiya.

Bayanin ma’aikatar ya kara da cewa, gwamnonin basa da hurumi na sake dawo da kudurin kwamitin tsaro na MDD, wanda ya maida kokarin Amurka da kawayenta daga kasashen turai saniyar ware kan wannan bukatar.

Daga karshe ma’aikatar ta bayyana cewa, kudurin ya kasa cika sharuddan kafa hukumar ta IAEA, na ci gaba da manufofin kafa ta. Sannan kasashen suna son kawo hargitsi a cikin dokokin kasa da kasa a wannan hukumar saboda son cimma manufofinsu a kan kasar Iran, wand aba zasu taba kaiwa ba.

Sannan a nashi bangaren, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Iran Isma’il Baghaea, ya bayyana cewa kudurin ba zai je ko in aba, kuma wadan nan kasashe sun yi kokarin amfani da hukumar IAEA a matsayin makami don yakar Iran. Wanda hakan ya sabawa dokokin kasa da kasa, ya kuma sabawa manufar kafa hukumar.

Ya ce kudurin ya kasa samun, rinjayen da yakamata don haka bai da wani karfin da za iyi tasiri. Sannan ya jefa rarraba a cikin gwamnonin hukumar.

Daga karshe Isma’il Baghaea y ace kasashen yamma basa nufin Al-khairi ga Iran, kuma dukkan maganganun da suke kan neman tattaunawa da kasar Iran da kuma bin hanyar Diblomasiyya don warware matsalolin da suka dabaibaye Shirin nukliyar kasar Iran ba gaskiya ne ba.

A wani labarin kuma JMI ta bada sanarwan daga yanzu ta yi watsi da yarjeniyar da ta kulla da shugaban hukumar IAEA a birnin Alkahira, wacce ta bawa hukumar dama ayyukan binci a kasar Iran tun bayan da ta koresu a karshen yakin kwanaki 12 wanda Amurka da HKI suka kai mata.

A cikin watan Satumba ne ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi da kuma shugaban hukumar ta IAEA Rafael Grossy suka rattabawa yarjeniyar hannu a birnin Alkahira don bawa hukumar wata dama da gudanar da bincike da ta saba a wasu cibiyoyin Nukliyar kasar ta Iran, wadanda suka hada da cibiyar bada wutan lantarki dake Buhshar na kudancin kasar.

Labarin ya ce a halin yanzu wannan yarjeniyar ta tashi daga aiki, bayan da hukumar ta amince da wannan yarjeniyar wacce take allawadai da kasar ta Iran.

JMI dai tana zargin hukumar IAEA , musamman shugabanta Rafael Grossy ta hannu a yakin kwanaki 12 da Amurka da HKI suka kaiwa kasar a cikin watan Yulin da ya gabata. Sannan ta shimfidaya wadannan kasashe hanya ta kaiwa cibiyoyin makamashin nukliya ta kasar hare-hare tare da rahotanni da kuma maganganun da shi Grossin yayi ta yi kafin a fara yakin.

Har’ila yau Tehran tana zargin Grossy da mikawa makinta asiran ayyukan makamashin nukliya na kasar ta Iran, wanda bai kamata ta yi hakan ba. Saboda cin amanane, kuma sabawa dokokin gudanar da hukumar ne. Banda haka Grossy ya kasa yin Allah wadai da hare-haren da Amurka da kuma HKI suka kaiwa cibiyoyin makamashin nukliya na kasar Iran da suke Fordo, Natanz da kuma Esfahan a karshen yakin kwanaki 12 a cikin watan Yunin da ya gabata. Wanda ya nuna irin yadda shugaban na hukumar IAEA yake aiki tare da makiyan JMI a wannan bangaren.

Tun bayan yakin na watan yuli na wannan shekaran ne, gwamnatin kasar Iran ta sallami dukkan ma’aikatan hukumar IAEA daga kasar daga baya ba bada izini ga wasu daga cikinsu don sanya ido a kan ayyukanta a cibiyar Nukliyar kasar da ke Bushar.

A wani labarin kuma HKI ta ci gaba da kai hare-haren kan kasashen larabawan da take mamaye da su a makon da ya gabata. Wannan duk tare da abinda ake kira sulhu da ta kulla da wasu daga cikinsu.

A kasar Lebanon kamar yadda ta saba da keta hurumin tsagaita wutan da ta kulla da kungiyar Hizbullah a cikin watan Nuwamban shekara ta 2024, a makon da ya gabata jiragen yakin HKI sun kai hare-hare kan kudancin kasar Lebanon tare da kai wasu da dama ga shahada. Banda haka ta kai hare-hare a kan wani filin wasan kwallo a sansanin yan gudun hijiran Falasdinawa mafi girma a yankin wato, Ainul Helwa. Inda ta kai falasdinwa akalla 15 ga shahada.

Banda haka a zirin gaza da take mamaye da shi, duk tare da tsagaita budewa juna wuta wanda ta cimma da kungiyar Hamas tare da shugabancin Donal Trump shugaban kasar Amurka yan watanni da suka gabata.

Jiragen yakin HKI ta ci gaba da kai hare-hare a yankin inda a makon da ya gabata ta kashe falasdinawa da dama. Wannan tare da cewa, ta hana kwararar kayakin agaji ko kuma shigowarsu cikin zirin gaza.

A yankin yamma da Jordan kuma, sojojin HKI suna ci gaba da korar falasdinawa daga gidajensu, da kashesu da kuma rusa gidajensu.

Kungiyar palasdinawa ta PFLP (The Popular Front for the Liberation of Palestine) ta bada sanarwan cewa idan halin da ake ciki a yankin yamma da kogin Jordan, to kuwa ana kusa da boren Intfada na 3. Kungiyar ta bayyana cewa, a jiya jumma’a ce sojojin yahudawan suka kashe Amr Al-Mabo dan shekara 18 a duniya da kuma Sami Mashayikh dan shekara 16 a duniya a garin Kafar Aqab da ke arewacin birnin Qudus wanda ya tada hankalin Falasdinawa da dama a yankin yamma da kogin Jordan.

Kungiyar tashe Falasdinawa da dama a yankin suna fushi iya wuya.  Kuma mai yuwa hakan ya kai ga Intifada na 3, wanda zai zama yaki a yankin da sojojin HKI.

Kungiyar ta yi  kira ga kungiyoyin kasa da kasa sus u dauki matakan da suka dace kafin lokaci ya kure, don halin da ake ci a yankin yamma da kogin Jordan ba zai dore ba. Tace akwai bukatar kasashen duniya su kauracewa gwamnatin yahudawan su kuma dorawa shuwagabanninsu takunkuman tattalin arziki masu tsanani.

Tun bayan fara yakin tufanul aksa a ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 gwamnatin yahudawan suka fara kissan falasdinawa da korarsu daga yankin da kuma rusa gidajensu fiye da yadda ta saba.

Kuma tun lokacin ya zuwa yanzu sun kashe falasdinawa da dama, sun kuma kori wasu wadanda yawansu ya fi dubu 40. Banda haka ta rusa dubban gidajen Falasdinawa a yankin. Duk wannan da nufin kara mamaye yankin da kuma maida kasar Falasdinu ta yahudawa zallah.

Kungiyoyin kasa da kasa da wadanda suka hada da MDD sun bayyana cewa, dukkan gine-ginen da HKI ta yi a yankin yamma da gogin Jordan basa bisa doka, kuma sun bukaci a rusa su.

Tun bayan yakin shekara 1967 zuwa yanzu yahudawan sun gina dubban gidaje wa yahudawan sahyoniyya kimani 700,000 a yankin yamma da kogin Jordan. Kuma firai ministan HKI Benyamin Natanyahu ya sha nanata cewa ba zai taba amincewa da samuwar kasar Falasdinu a kan kasar da suka ginawa yahudawa ba.

Masu sauraro a nan zamu dasa aya a cikin shirimmu nay au sai kuma wani mako idan All..ya kaimu. Muna dauke da wani sabon shiri idan Allah ya kaimi. A halin yanzu ni Tahir Amin nake cewa wassalamu alaikum wa rahamatullahi wa barakatuhu.

Share

0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Ghalibaf: Makiya Sun Sawya Dabarbarun Yaki Da Iran November 22, 2025 Tsohon Ma’aikacin CIA Ya Ce HKI Ta Yi Barazanar Amfani Da Makaman Nukliya Kan Iran November 22, 2025 Yan Majalisar Dokokin Amurka Sun Sami Rarrabuwar Kai Dangane Da ‘Keshe Kiristoci A Najeriya’ November 22, 2025 Kasar Ukraine Ta Ki Amincewa Da Sabon Shirin Amurka Na Kawo Karshen Yaki A Kasar November 22, 2025 Yan Wasan Kasar Iran Sun tashi Da Lambobin Yabo 81 A Wasannin Zumunci Tsakanin Kasashen Musulmi November 22, 2025 Shugaban Rasha yace Ba zai Janye Ayyukan Soji  Da Yake Yi A Kasar Ukrain Ba November 21, 2025 Kwamitin Sulhu Na MDD Ya yi Tsokaci Kan Rashin Tsaro A Najeriya November 21, 2025 Araqchi: Iran Ta Shirya Tsaf Fiye Da Kowanne Lokacin  Musamman Bayan Yakin Kwanaki 12 November 21, 2025 China ta ce Ya Kamata A Aiwatar Da Sakamakon Taron Kolin Tianjin Don Inganta Kungiyar SCO November 21, 2025 Iran Ta yi Gargadi Game Da Sakamakon Da  Zai Iya Faruwa A Yankin Bayan Shigar Isra’ila Kasar Siriya November 21, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci About Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS News Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Explore Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS Ka’idojin Amfani Hakkin Mallaka Ku Tuntube Mu Jaridu Sitemap RSS

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Hukumar Alhazai Ta Jihar Jigawa Za Ta Mayar Da Rarar Kudi Ga Maniyyatan 2026
  • Rundunar Sojan Iran Tana Cikin Shirin Mayar Da Martani Akan Kowace Barazana
  •  Madagascar: An Bayyana Jadawalin Farko Na Gwamnatin Rikon-Kwarya Da Kuma Manyan Zabuka
  • Duniyarmu A Yau: Sabon Kuduri Mai Yin Allawadai Da Iran A Hukumat IAEA
  • DSS ta mayar da Nnamdi Kanu gidan yarin Sakkwato
  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara
  • Jihar Jigawa Ta Amince da Naira Biliyan 3.5 a Matsayin Kudaden Tallafin UBEC 2025
  • CORET, ECOWAS Sun Hada Matasa Da Wasu Abokan Hulda Don Inganta Kiwo Da Madara
  •  Iran Tana Cikin kasashe 10 Na Farko Da Su Ka Fi Yawan Wuraren Tarihi
  • Ribadu ya jagoranci tawaga zuwa Amurka don ƙaryata zargin yi wa Kiristoci kisan ƙare dangi