A soma laluben watan Zhul Qi’da — Sarkin Musulmi
Published: 26th, April 2025 GMT
Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Abubakar ya da umarnin fara duban watan Zulki’ida na shekarar 1446 daga gobe Lahadi, 29 ga watan Shawwal, wanda ya yi daidai da 27 ga watan Afrilun 2025.
Hakan na ƙunshe cikin wata takarda da Wazirin Sakkwato kuma shugaban kwamitin bai wa majalisar Sarkin Musulmi shawara kan harkokin addinin musulunci, Farfesa Sambo Wali Junaid ya raba wa manema labarai.
Sarkin Musulmi ya ce duk wanda ya samu ganin jinjirin watan ya sanarwa hakimi ko uban ƙasa mafi kusa da shi don sanar da majalisar sarkin musulmi.
A ƙarshe sanarwar ta ce Sarkin ya roƙi Allah Ya kawo wa Nijeriya zaman lafiya da ci gaba mai ɗorewa.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Sarkin Musulmi Watan Dhul Qa ada Sarkin Musulmi
এছাড়াও পড়ুন:
Bai Dace A Mika Wuya Ga Wanda Ya Nuna Fin Karfi Da Matakan Haraji Ba
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp