Ministan Harkokin Wajen Iran Ya Ce Kasarsa A Shirye Take Ta Sulhunta Tsakanin Pakistan Da Indiya
Published: 25th, April 2025 GMT
Ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa: Iran a shirye take ta inganta fahimtar juna tsakanin Indiya da Pakistan
Ministan harkokin wajen Iran Sayyid Abbas Araqchi ya sanar a yau Juma’a cewa: kasarsa a shirye take ta yi aiki mai kyau a fagen sulhunta tsakanin Indiya da Pakistan don inganta fahimtar juna tsakanin bangarorin biyu a wannan mawuyacin lokaci.
Da yake tsokaci game da abubuwan da suka faru a baya-bayan nan tsakanin Indiya da Pakistan, Araqchi ya bayyana cewa: “Indiya da Pakistan kasashe ne ‘yan uwan juna kuma masu makwabta da Iran, kuma suna da alakar al’adu da wayewa tun shekaru aru-aru.”
Ministan harkokin wajen na Iran ya kara da cewa: “Suna daukar kasashen Indiya da Pakistan a matsayin sauran makwabtansu, kuma masu matsayin fifiko na farko.” Don haka Iran a shirye take ta yi amfani da dukkanin kwarewarta wajen kyautata alaka tsakanin Pakistan da Indiya, don inganta fahimtar juna a tsakanin bangarorin biyu a cikin wannan lokaci mai wuyar gaske.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: Indiya da Pakistan
এছাড়াও পড়ুন:
Ya Kamata Shugaba Tinubu Ya Ƙulla Alaƙa Ta Kut-da-kut Tsakanin Hukumar Shige Da Fice Da Kwastam – Babandede
“Iyakar kasa ba wai kawai yanki ne na tsaro ba. Yanki ne na al’adu; yanki ne na tarihi; haka nan ma yanki ne na tattalin arziki. Kula da shige da fice na da matukar amfani ga ci gabanmu. Wajibi ne Nijeriya ta zuba jari a kan kula da nau’in mutanen da take tacewa wajen shiga kasa da kuma irin mutanen da muke tacewa wajen fita daga kasa.
“Dole ne mu yi nazarin nau’in ayyukan da bakin-haure ke yi da kuma yadda suke shafar tattalin arzikinmu. Muna bukatar tsame mutanen da ke kawo cikas ga ci gabanmu”, in ji Babandede.
ShareTweetSendShare MASU ALAKA