’Yan bindiga sun sace matashiya bayan karɓar kuɗin fansa a Kano
Published: 26th, January 2025 GMT
’Yan bindiga sun kai hari garin Garo da ke Ƙaramar Hukumar Kabo a Jihar Kano cikin daren ranar Lahadi, inda suka sace wata budurwa mai suna Zainab Auwalu, bayan sun karɓi kuɗin fansa Naira miliyan takwas daga hannun mahaifinta.
Zainab, wadda ta kammala makarantar sakandare kwanan nan, an sace ta a gidan mahaifinta, Alhaji Auwalu.
Shaidu sun bayyana cewa ’yan bindigar, kimanin su 10, sun shiga garin da babura ɗauke da muggan makamai.
Sun shiga gidan Alhaji Auwalu da misalin ƙarfe 1:30 na dare, inda suka shafe awanni suna cin karensu ba babbaka, sannan suka tafi da kuɗin fansa tare da sacw ‘yarss.
Wani mazaunin garin, Haruna Muhammad, ya ce harin ya jefa al’ummar garin cikin firgici.
Mutane da yawa na zargin cewa wasu mazauna garin ne suka bai wa ’yan bindigar bayanai.
Kakakin ’yan sandan jihar, Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin.
Ya bayyana cewa jami’an tsaro na ƙoƙarin bin sahun ’yan bindigar da kuma ceto matashiyar.
Ko da yake satar mutane da fashi ba su yawaita a Jihar Kano ba, garuruwa irin su Garo da sauran yankunan Arewacin Kano da ke kusa da jihohin Kaduna da Katsina, sun sha fuskantar hare-haren ’yan bindiga.
উৎস: Aminiya
এছাড়াও পড়ুন:
Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Aike Da Sako Ga Al’ummar Iran Bayan Harin Da Iran Ta Fuskanta
Jagoran juyin juya halin Musulunci ya aike da sako ga al’ummar Iran bayan harin da yahudawan sahayoniyya suka kai kan kasar
A yammacin jiya ne Jagoran juyin juya halin Musulunci Ayatullah Sayyid Ali Khamenei ya gabatar da sakon ta gidan talabijin ga al’ummar Iran bayan harin ta’addanci na baya-bayan nan da yahudawan sahayoniyya suka kaddamar kan kasar Iran.
Jagoran juyin juya halin Musuluncin ya bayyana a cikin wani sakon da ya aike ta gidan talabijin ga al’ummar Iran cewa: Sojojin Iran za su yi aiki da dukkanin karfinsu, kuma za su mayar da martani kan wannan mugunyar aniya ta ‘yan sahayoniyya kaskantattu marasa tunani da basira.
Jagoran ya jaddada cewa: Yahudawan sahayoniyya ba za su fita cikin wannan aika-aika ba, kuma wajibi ne al’ummar Iran su tabbatar da cewa ba za a yi sassauci ko sakaci kan hakan ba.