An kashe Shugaban coci da wata mace a Benuwe
Published: 25th, April 2025 GMT
A wani sabon tashin hankali ya yi sanadiyyar rasa rayukan wani shugaban cocin Roman Katolika da wata mata a ƙauyen Ayua da ke gundumar Mbayer/Yandev a ƙaramar hukumar Guma a Jihar Benuwe.
Shedun gani da ido sun ce lamarin ya faru ne a daren ranar Talata, lamarin da ya sa mazauna yankin da ke kewayen yankin Mbagwen da ke ƙaramar hukumar Guma ƙaurace wa gidajensu sakamakon hare-haren da ’yan bindiga ke kaiwa.
Waɗanda aka kashen dai sun haɗa da: David Hur, shugaban shiyyar Cocin Anter Catholic da Misis Lydia Utuu ta ƙauyen Ayua.
Majiyoyi sun yi zargin cewa rikicin ya samo asali ne sakamakon wata arangama tsakanin wani makiyayi da wani mazaunin ƙauyen.
Rahotanni sun ce makiyayin ya yi yunƙurin wanke kansa ne a wata hanyar ruwa ɗaya tilo da al’umma ke da shi bayan ya sha daga ciki. Wani ɗan unguwar ya nuna rashin amincewarsa, wanda hakan ya haifar da rikici inda ake zargin makiyayin ya kai masa farmaki da adda.
“Mutumin ya yi neman agaji don jawo mutanen ƙauyen zuwa wurin, amma hargitsin ya kaure da sauri zuwa wani mummunan yanayi,” kamar yadda wani mazaunin garin ya shaida wa wakilinmu ta wayar tarho.
Har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto, mazauna yankin sun bar gidajensu da yawa. Har yanzu dai ana zaman ɗar-ɗar, tare da yin kira ga gwamnati da jami’an tsaro su shiga tsakani domin daƙile ci gaba da zubar da jini.
Kakakin rundunar ’yan sandan Jihar Benuwe, CSP Catherine Anene ba ta amsa tambayoyi kan lamarin ba don ƙarin haske a lokacin haɗa wannan rahoto.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Makiyayi Mbayer Yandev
এছাড়াও পড়ুন:
Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Lin Jian, ya yi karin haske game da taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, wanda shugaban kasar Sin Xi Jinping zai halarta a Kazakhstan, yana mai cewa, Sin na da yakininta hanyar taro, ita da sauran kasashen yankin tsakiyar Asiya biyar, za su zurfafa dunkulewa, da amincewa da juna, da gina matsaya guda ta fuskar hadin gwiwa, da zurfafa daidaiton dabarun ci gaba, da daga matsayin hadin gwiwarsu a fannoni daban daban, da kara kuzarin gina al’umma mai makomar bai daya ta Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya.
Bisa gayyatar da shugaban jamhuriyar Kazakhstan Kassym-Jomart Tokayev ya yi masa, shugaba Xi Jinping zai halarci taron koli na Sin da kasashen yankin tsakiyar Asiya karo na biyu, tsakanin ranekun 16 zuwa 18 ga watan nan na Yuni. (Saminu Alhassan)
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp