Sayyid Fadlallah ya bayyana cewa: Ana samar da makamai ne domin kare kasa da kuma matsa wa abokan gaba

A cikin hudubar sallar Juma’arsa daga mumbarin masallacin Imamain al-Hassanain (amincin Allah ya tabbata a gare su) da ke Haret Hareik a kudancin birnin Beirut, Sayyid Ali Fadlallah ya yi kira da a dauki dukkan matakai na tursasawa makiya yahudawan sahayoniyya janyewa daga yankin kasar Lebanon da ta mamaye, da daina kai hare-haren wuce gona da iri kullum rana kan yankunan Lebanon, da kuma sakin mutanen da suka kama a matsayin fursunonin yaki.

Malamin ya bukaci dukkanin ‘yan kasar Lebanon, ba tare da la’akari da mazhabobin su ba, ko kungiyoyinsu, ko kuma matsayinsu na siyasa, da su tashi tsaye wajen gudanar da hakkokin da sukarataya a wuyarsu kan kasarsu, da kuma fuskantar wadanda ke yin zagon kasa ga ikon kasa da tsaro, da zaman lafiyarta, da kuma samun hadin kan muryarsu wajen tunkarar wadannan hare-haren da ke barazana ga zaman lafiyar cikin gida da zaman dukkan al’umma.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure

More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba

Wasu al’ummomi sun bayyana dalilan da suka sa suka karbi tsarin yin gwajin lafiyar ma’aurata kafin a daura musu aure.

A wasu lokutan, akan samu matsaloli sakamakon rashin gwajin jini kafin a hada mace da na miji aure. Matsalolin sun hada da yaduwar cututtuka, samun ‘ya’ya marasa lafiya da sauran wasu matsalolin.

NAJERIYA A YAU: Yadda Za A Dama Da Matan Arewa A Fannin Kimiyya DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta

Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan dalilan da suka sa wasu alummomin suka rungumi yin gwajin jini kafin aure.

Domin sauke shirin, latsa nan

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An Yaba Da Kwazon Shugaba Bola Ahmad Tinubu
  • Hare-hare: ’Yan bindiga sun raba mutum 5,000 da muhallansu a Katsina
  • Amurka Ta Ce HKI Ba Zata Fice Daga Kasar Lebanon Ba Sai An Kwance Damarar Hizbullah
  • Gidauniyar ‘Ya’yan Sarakunan Arewa Sun Marawa Sarkin Musulmi A Matsayin Shugaban Majalisar Sarakuna
  • Gwamnatin Tinubu ta mayar da Arewa saniyar ware – ACF
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  • Shugaba Xi Ya Aike Da Sako Ga Taron Wanzar Da Zaman Lafiya Na Matasan Kasa Da Kasa
  • Gwamnatin Katsina Ta Fara Bayar Da Maganin Zazzabi Kyauta A Asibitoci
  • ’Yan bindiga sun kashe mutum 5 a sabon hari a Alkaleri