Radio Nigeria Kaduna Hausa:
2025-06-15@13:22:15 GMT

An Gudanar Da Taron WASA Na Rundunar Sojin Najeriya A Gusau

Published: 26th, January 2025 GMT

An Gudanar Da Taron WASA Na Rundunar Sojin Najeriya A Gusau

Kwamandan runduna ta 1 ta sojojin Najeriya da ke Gusau, Birgediya Janar Opurum Timothy, ya bayyana  wa al’ummar jihar Zamfara da ma kasa baki daya aniyar rundunar sojojin Najeriya na ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a karshen taron wasannin rundunar sojojin Najeriya ta yammacin Afirka WASA 2024 da aka gudanar a Gusau.

Taro West African Social Activities WASA wani taro ne na shekara-shekara da rundunar sojojin Najeriya ke shiryawa domin  wasannin gargajiya na wannan  yankin na Afirka.

Taron na shekara-shekara yana tattaro Jami’ai, Sojoji, da iyalansu  cikin annashuwa domin wasannin al’adun da kuma bikin ƙarshen  shekara.

Janar Opurum wanda ya jaddada kudirin rundunar na kawar da ‘yan fashi da kuma dawo da zaman lafiya a Zamfara da yankin Arewa maso Yamma gaba daya, ya yi kira ga sojojin da su jajirce wajen gudanar da ayyukansu, yana mai jaddada cewa, sadaukarwarsu da  na da matukar muhimmanci wajen samun zaman lafiya mai dorewa.

Kwamandan Birgediya wanda ake yi wa lakabi da “Jar Kunama”, ya yabawa al’ummar Zamfara bisa yadda suke ba da hadin kai, musamman ta hanyar samar da muhimman bayanan sirri, wanda ya haifar da gagarumar nasara.

Tun da farko, Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara, wanda kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Meriga ya wakilta, ya yabawa rundunar sojojin Najeriya da sauran jami’an tsaro bisa namijin kokarin da suke yi na samar da zaman lafiya mai dorewa a fadin jihar ta Zamfara.

Taron WASA na bana a Gusau ya samu halartar manyan baki da suka hada da sarakunan gargajiya da shugabannin sauran hukumomin tsaro kamar rundunar sojojin saman Najeriya da jami’an tsaro da dai sauransu.

Muhimman abubuwan da suka faru a wajen taron sun hada da, baje kolin al’adu da raye-raye, wasan kokowa, da dai sauransu.

Yayin da wasu da dama da suka yi nasara suka je gida da kyaututtuka daban-daban da suka hada da man girki, shinkafa da sauran kyaututtuka.

Daga Aminu Dalhatu

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane

Sadeeƙ Umar da ake yi wa laƙabi da Mane, matashin ɗan wasan ƙwallon ƙafa ne da yake tashen taka leda a rukunin ’yan dagaji a Jihar Kano.

Matashin, wanda tauraronsa ke haskawa a fagen tamola ya yi fice ne bayan da ya kafa wani sabon tarihi na zura ƙwallaye 10 a raga a wasanni 10 da ya buga tare da ba da taimako sau 6 wajen wasu ƙwallayen a rukuni gasar wasannin ’yan dagaji aji 1 da aka fi sani da Amateur 1 a Jihar Kano.

An ciro gawarwaki sama da 200 daga jirgin Indiya da ya yi hatsari Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa

A cikin tattaunawarsa da Aminiya, Sadeeƙ Mane ya bayyana cewa, ƙwazo da sadaukar da kai ne suka taimaka masa wajen kafa wanna tarihi.

Sadeeƙ, wanda kamar sauran ‘yan wasa ya fara buga ƙwallon ne a cikin unguwa kafin daga bisani ya fara buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Togo da ke Unguwar Birget, Ƙaramar Hukumar Nasarawa a Jihar Kano.

Daga ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Togo, Sadeeƙ ya koma taka leda a ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Legend FC, inda a can ne bayan ya nuna bajinta a Gasar Cin Kofin Shugaban Ƙaramar Hukumar Nasarawa, Ƙungiyar Ƙwallon Ƙafa ta SBS Waliyya da ke buga wasa a matakin Amauteur 1 ta ɗauke shi.

A kakar bana Saƙeeƙ ya kafa tarihi, inda ya buga wasanni goma kuma ya zura ƙwallaye goma a raga.

Wannan nasara da ya samu ta sa ya lashe kyautar ɗan wasan da ya fi kowanne ɗan wasa zura ƙallaye a raga a wannan shekara.

Haka kuma an zaɓi Saƙeed a matsayin ɗan wasan da ya fi kowanne ɗan wasa ƙwarewa a wannan matakin.

Da yake ƙarin bayani kan yadda ya samu nasarar zura ƙwallaye 10 a cikin wasanni 10, Sadeeƙ ya ce, “na buga wasanni 10 kuma na zura ƙwallaye 10 a ragar abokan karawa.

A cikin wasanni 10 ɗin na zura ƙwallayen ne a wasanni 8, wato wasa 2 kacal ne ban ci ƙwallo ba. Wannan ne ya sa na zama ɗan wasan da ya fi zura ƙwallo a gasar.”

Da yake amsa tambayar ko me ne sirrin wannan nasarori haka?

Sadeeƙ Umar sai ya ce: “Ka san an ce in ka ji wane ba banza ba, wato in ba a sha gumi ba a sha rana. Don haka na jajirce ne da ba wa kaina horo da kuma sanya juriya a zuciyata. Wato ina nufin bayan horon da ake yi mana a filin wasa, ni a karan kaina ina fita, in yi gudu da dadare da sauran wasanni na motsa jiki masu wahala don in saba wa kaina,” in ji Mane.

Ya ƙara da cewa, “wannan shi ya sa za ka ga in na shiga fili bana gajiya har a tashi. Haka kuma, wannan shi ne dalilin da ya sa ake yi min laƙabi da shahararren ɗan wasan ƙasar Senegal ɗin nan mai suna Sadio Mane, wato ganin irin salon wasanmu ɗaya ne, kai har ma wasu na cewa, wai mun yi kama ko a fuska.”

Sadeeƙ Mane ya bayyana wa Aminya cewa, burinsa shi ne wata rana ya zama kamar Sadio Mane wato ya fita ƙasashe Turai, ya buga wa manyan ƙungiyoyin ƙwallo ƙafa na duniya wasa.

“Kamar kowane matashin ɗan ƙwallo, ni ma babban burina shi ne in buga ƙwallo a ƙasashen Turai, in shahara kamar Sadio Mane. Ina ji a raina wata rana zan buga wa manyan ƙungiyoyi kamar Chealsea da Liɓerpool da Barcelona,” in ji matashi ɗan wasan.

Sai dai Sadeeƙ ya bayyana cewa, ba kamar sauran matasan ’yan ƙwallo ba da suke son shiga Turai gaba-gaɗi, shi yana da burin ya buga wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars kafin ya tafi ƙasashen Turai da ƙwallo.

“A gaskiya ni in so samu ne, na fi son in fara buga wa Kano Pillars wasa kafin in je Turai. Saboda tunda na taso, ina son Pillars sosai. Haka kuma ina ga a matsayina na ɗan Kano zai zamo abin alfahari a gare ni a ce wata rana na sanya wa ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Kano Pillar riga, na ba da tawa gudunmawar,” in ji Mane.

Mane ya bayyana rashin samun haɗuwa da manajan masu ɗaukar matasan ‘yan wasa zuwa ƙasashen Turai, musamman a jihohin Arewa a matsayin wani babban ƙalubale da matasan ‘yan wasa masu hazaƙa ke gamuwa da shi a wannan yanki.

“Babban ƙalubalenmu a nan Kano da sauran jihohin Arewa shi ne wa zai taimake ka, ya haɗa kai da manajan da suke ɗaukar matasan ‘yan wasa zuwa Turai. Ka ga muna da matasa masu ƙwazo da basira sosai, sai dai ba ma samun wannan gatan. Ban san dalilin da ya sa manajojin ɗin ba sa son zuwa nan ba,” In ji Sadeeƙ Mane.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • ‘Yan Wasa Biyar Da Suka Taka Rawar Gani A Kofin Zakarun Turai
  • Rawar Da ‘Yan Wasan Afirka Suka Taka A Gasar Premier Ta Ingila
  • Dimokuradiyya A Shekara 26: Ba Yabo Ba Fallasa
  • Gwamnan Gombe Ya Yi Allah Wadai Da Kisan Da ‘Yan Daba Suka Yi Wa Amadi Kasiran
  • Sojoji sun kashe kasurguman ’yan bindiga 3 a Zamfara
  • Ƙwazo da juriya suka sa na zura ƙwallaye 10 a wasanni 10 – Mane
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Ranar Dimokuraɗiyya: Gwaman Zulum ya yi wa fursunoni 66 afuwa
  • Sojoji Sun Kashe Auta, Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda Da Wasu 13 a Jihar Zamfara
  • 12 ga Yuni: Najeriya na bikin ranar dimokuraɗiyya