An Gudanar Da Taron WASA Na Rundunar Sojin Najeriya A Gusau
Published: 26th, January 2025 GMT
Kwamandan runduna ta 1 ta sojojin Najeriya da ke Gusau, Birgediya Janar Opurum Timothy, ya bayyana wa al’ummar jihar Zamfara da ma kasa baki daya aniyar rundunar sojojin Najeriya na ci gaba da aiki tukuru domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali.
Ya bayyana haka ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a karshen taron wasannin rundunar sojojin Najeriya ta yammacin Afirka WASA 2024 da aka gudanar a Gusau.
Taro West African Social Activities WASA wani taro ne na shekara-shekara da rundunar sojojin Najeriya ke shiryawa domin wasannin gargajiya na wannan yankin na Afirka.
Taron na shekara-shekara yana tattaro Jami’ai, Sojoji, da iyalansu cikin annashuwa domin wasannin al’adun da kuma bikin ƙarshen shekara.
Janar Opurum wanda ya jaddada kudirin rundunar na kawar da ‘yan fashi da kuma dawo da zaman lafiya a Zamfara da yankin Arewa maso Yamma gaba daya, ya yi kira ga sojojin da su jajirce wajen gudanar da ayyukansu, yana mai jaddada cewa, sadaukarwarsu da na da matukar muhimmanci wajen samun zaman lafiya mai dorewa.
Kwamandan Birgediya wanda ake yi wa lakabi da “Jar Kunama”, ya yabawa al’ummar Zamfara bisa yadda suke ba da hadin kai, musamman ta hanyar samar da muhimman bayanan sirri, wanda ya haifar da gagarumar nasara.
Tun da farko, Gwamna Dauda Lawal na jihar Zamfara, wanda kwamishinan tsaro da harkokin cikin gida na jihar Meriga ya wakilta, ya yabawa rundunar sojojin Najeriya da sauran jami’an tsaro bisa namijin kokarin da suke yi na samar da zaman lafiya mai dorewa a fadin jihar ta Zamfara.
Taron WASA na bana a Gusau ya samu halartar manyan baki da suka hada da sarakunan gargajiya da shugabannin sauran hukumomin tsaro kamar rundunar sojojin saman Najeriya da jami’an tsaro da dai sauransu.
Muhimman abubuwan da suka faru a wajen taron sun hada da, baje kolin al’adu da raye-raye, wasan kokowa, da dai sauransu.
Yayin da wasu da dama da suka yi nasara suka je gida da kyaututtuka daban-daban da suka hada da man girki, shinkafa da sauran kyaututtuka.
Daga Aminu Dalhatu
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Jamhuriyar Benin – Soyinka
Marubuci kuma mai lambar yabo ta Nobel, Wole Soyinka, ya ce kamata ya yi Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya tura ɗansa, Seyi Tinubu, zuwa Jamhuriyar Benin domin “kwantar da” yunƙurin juyin mulki da bai yi nasara ba.
Soyinka ya soki matakin Tinubu na tura dakarun rundunar Sojojin Sama ta Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin bayan yunƙurin juyin mulki da aka yi domin kifar da Shugaba Patrice Talon daga mulki.
Ya yi wannan jawabi ne a bikin bayar da kyaututtuka na shekara karo na 20 da Cibiyar Binciken Kwakwaf ta Wole Soyinka (WSCIJ) ta shirya a Legas ranar Litinin.
Fitaccen marubucin ya tuna yadda ya ga jami’an tsaro masu makamai sosai suna gadin Seyi Tinubu a Legas.
Ya ce: “Shugaba Tinubu bai kamata ya tura Sojojin Sama da na ƙasa ba domin shawo kan wannan tayar da hankali da ke barazana ga tsaronmu da daidaituwarmu; a’a akwai hanyoyi mafi sauƙi na yin hakan.
“Bari in gaya muku inda Tinubu ya kamata ya nemi rundunar da za ta shawo kan wannan tayar da hankali, na nan a Legas ko ma a Abuja, amma babu buƙatar kiran sojojin ƙasa ko na sama.
“Zan gaya muku abin da ya faru a ɗaya daga cikin ziyarata zuwa gida watanni biyu da suka gabata, ina fita daga wani otel sai na ga abin da ya yi kama da wurin yin fim, wani matashi ya rabu da ’yan wasan ya zo ya gaishe ni cikin ladabi.
“Na kalli wurin sai na ga kusan rundunar sojoji ce gaba ɗaya sun mamaye filin otel ɗin a Ikoyi. Na koma cikin motata na tambaya wanene wannan matashin, sai aka gaya min.
“Na ga sojoji, haɗin jami’an tsaro masu makamai sosai, akalla 15 suna ɗauke da manyan makamai, abin da ya isa ya tsare karamar makwabciya kamar Benin.
“Na yi tunanin cewa a gaba mai girma shugaban ƙasa ya kamata kawai ya kira ya ce ‘Seyi je ka kwantar da fitina a can’. Na yi matuƙar mamaki har na fara neman Mashawaracin Shugaban Kasa a fannin tsaro,” in ji Soyinka.
Soyinka ya kuma ce ba Tinubu ne shugaban da ya fara mulkar Najeriya yana da ’ya’ya ba, don haka bai ga dalilin da zai sa a girke tarin jami’an tsaro kawai don su rika gadin dansa ba.