Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci Na Iran Ya Ce: Maganar ‘Yan Sahayoniyya Rudu Ne Maras Amfani
Published: 29th, April 2025 GMT
Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci ya bayyana kalaman gwamnatin ‘yan sahayoniyya a matsayin wani rudu da ba shi da amfani da har zai yi tasiri a zaman tattaunawan Iran da Amurka Wanda ba na kai tsaye ba, yana mai cewa duk wani hari ko da karami ne za a kai kan Iran zai zama tamkar tartsatsin wuta da zai iya janyo tashin gobara da zai iya kona yankin gaba daya.
A jawabin da ya gabatar yayin taron kolin majalisar shawarar Musulunci ta Iran a yau Talata, Muhammad Baqir Qalibaf ya bayyana cewa: Firai ministan gwamnatin yahudawan sahayoniyya mai laifi ne mai zubar da jinin fararen hula, saboda neman hana mutuwarsa a fagen siyasa, kuma yanzu yana yin barazana ga al’ummar Iran mai girma. Qalibaf ya yi nuni da cewa, wannan mutum mai rauni yana son canza haryar tafiyarsa a kullum rana saboda tsoron kada a kama shi sakamakon kasancewarsa mai laifi da yafi zama abin ki a tarihin wannan zamani.
Qalibaf ya kara da cewa; Bayan shafe shekaru da dama Netanyahu yana yaudarar kafafen yada labarai, a halin yanzu gwamnatin yahudawan sahayoniyya ta fito fili kuma ta bayyana hakikanin fuskar wannan azzalumi ga duniya, musamman ga matasan Amurka da Turai. Qalibaf ya kara da cewa babu wani abin da wannan gwamnatin ta cimma sai kai hare-haren bama-bamai kan makarantu da asibitoci, kuma ba ta cimma burin da ta ayyana a farkon yakin ba, kuma halin da ake ciki yana da matukar rashin tabbas.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani
Sakataren Majalisar Tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Ba suna cewa ba za su gudanar da tattaunawa ba ne, amma tattaunawar dole ta kasance ta gaskiya
Sakataren Majalisar Tsaron Kasa ta Iran, Ali Larijani, ya tabbatar da cewa: Ba za a iya kwantar da hankalin makiya ta hanyar yin sassauci da rashin gindaya sharaɗi ba.
Da yake jawabi a wani taron masana ilimin bil’adama a birnin Tehran fadar mulkin kasar Iran ‘yan kwanaki da suka gabata, Larijani ya bayyana cewa: “Hanya madaidaiciya ta gyara halayen makiyansu tana cikin ƙarfafa haɗin kan ƙasa, kuma tushenta shine gyare-gyaren tattalin arziki da dawo da kwanciyar hankali ga rayuwar mutane.”
Sakataren Majalisar Tsaron kasar Iran ya jaddada cewa: Ba za a iya kwantar da hankalin makiya ta hanyar yin sassauci da rangwame kan hakki ba gami da rashin gindaya sharaɗi ba, yana mai ƙarawa da cewa: “Mutanen da suka amince kan wajabcin inganta sinadarin Uranium, yanzu suna cewa bai kamata Iran ta yi ba; su masu neman duk wata dama ce kan cimma munanan manufofinsu.”
Larijani ya nuna cewa: Babu ƙarshen buƙatun Amurka, kamar yadda suke cewa: “Bayan hana inganta Uranium, zasu bukaci rage karfin makaman kasar Iran tare da bukatar yin ayyukan kasa kamar yadda suka Sanya ake yi a yankin.” Ya bayyana: “Yana ganin akwai buƙatar juriyar ƙasa kan waɗannan buƙatun, kuma Iran da al’ummar kasarta dole ne su tsaya su kalubalanci duk wata mummunar manufa kansu.”
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Gwamnatin Isra’ila Tana Ci Gaba Da Hana Masu Jinya Zuwa Kasashen Waje Neman Magani Daga Gaza November 2, 2025 Kasar Qatar Ta Ba Da Tallafin Gaggawa Ga Al’ummar Sudan Bayan Gumurzun El-Fasher November 2, 2025 IAEA : Babu wata shaida da ke nuna cewa Iran na kera makaman nukiliya November 2, 2025 Amurka : zamu dauki matakin soja idan Najeriya ta gaza kawo karshen kashe Kiristoci November 2, 2025 Hamas ta musanta zargin Amurka na cewa tana sace kayan agaji a Gaza November 2, 2025 Wasu Yan Ta’adda Sun Kashe Dakarun Sa Kai 2 A Kudu Maso Gabashin Iran November 2, 2025 Sojojin Amurka Na Kara Fuskantar Venezuwela Adaidai Lokacin da Trump Ke Musanta Batun Kai Hari November 2, 2025 Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon November 2, 2025 Iran Ta Gargadi Isra’ila Kuma Tasha Alwashin Kare Shirinta Na Nukiliya November 2, 2025 Shugaban AmurkaTrump ya yi barazanar daukar matakin soji kan Najeriya November 2, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci