Iran Ta Bukaci Kasashen Indiya Da Pakistan Da Hada Kai Don Yakar Ta’addanci
Published: 27th, April 2025 GMT
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeskiyan ya bayyanawa firai ministocin kasashen Indiya da Pakistan a maganar da yayi da su ta wayar tarho a jiya Asabar, kan cewa mu hada kai gaba daya don yaki da ayyukan ta’addanci a yankin.
Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Pezeshkiya yana fadawa shuwagabannin kasashen biyu, kan cewa akwai bukatar hada kai tsakanin kasashen biyu da sauran kasashen yankin don yi ki da ayyukan ta’adanci.
Shugaban ya kara jaddada yin allawadai da hare-heren da aka kai cikin kasar Indiya a makon da ya gabata. Ya kuma jajantawa Narendra Mudi firai ministan kasar kasar ta India. Harin dai yan bindiga a garin Pahalga na yankin Kashmir dake karkashin ikon kasar Indiya suka kai, hare-hare kan wasu yan yawan shakatawa wuta sun kuma kashe akalla mutane 27. Tun lokacin ya zuwa yanzu dai sojojin kasashen biyu sun yi musayar wuta a tsakaninsu.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Rasha ta ayyana tsagaita wuta ita kaɗai a yakinta da Ukraine
Fadar Kremlin ta kasar Rasha ta ayyana tsagaita wuta na kwana biyu ita kaɗai a yakinta da kasar Ukraine.
Shugaba Vladimir Putin ya sanar a ranar Litinin cewa Rasha za ta aiwatar da tsagaita wutar ne daga tsakar dare na 8 ga Mayu zuwa tsakar dare na 10 ga Mayu.
A ranakun da za a tsagaita wutar ne Rasha ke bikin karshen da yakinta da kasar Jamus a shekarun 1941 zuwa 1945, wanda aka fi sani da Yakin Duniya na Biyu a yawancin duniya.
A Rasha ana kiran yakin na Duniya na biyu da sunan Babban Yaƙin Ceton Kasa.
Shekara 10 ina sayar da sassan jikin ɗan Adam — Wanda ake zargi Dukan farar hula saboda sanya kayan sojoji laifi ne — Janar Chibuisi