2025-07-25@14:56:14 GMT
إجمالي نتائج البحث: 3534

«yin kwalliya»:

    Sai dai Sanatoci sun yi watsi da bayanin, inda suka zargi Ojulari da yin watsi da Majalisar. Kwamitin yana binciken tambayoyin tantancewa daga shekarar 2017 zuwa 2023, wanda ya nuna sabanin da ya kai Naira tiriliyan 210, ciki har da bashin da ba a tabbatar da shi ba na Naira tiriliyan 103. ‘Yan majalisar sun firgita cewa Naira tiriliyan 3 zuwa 5 ne kawai aka rubuta a cikin asusun ribar da kamfanin ya samu a cikin shekaru shida. “Wannan gayyatar ba tilas bace,” in ji Wadada. Ya kara da cewa kwamitin ba yana zargin hukumar ta NNPC da laifin sata bane amma ya jaddada cewa girman sabanin ya bukaci a yi karin haske kai tsaye. Ya bayyana rashin bayyanar Ojulari...
    Aƙalla mutum 14; ciki har da mata da ƙananan yara ƙanana ne, suka rasu a wani sabon hari da aka kai a Jihar Filato. Harin ya faru ne da yammacin ranar Alhamis a Gundumar Mangor da ke Ƙaramar Hukumar Bokkos. ‎Sarkin Katsinan Gusau ya rasu Yadda aka mayar da yaran da aka sace a Kano masu wanke-wanke a Kudu Waɗanda aka kashe suna kan hanyarsu ta dawowa daga kasuwar mako-mako da ke garin Bokkos, lokacin da wasu ’yan bindiga suka buɗe musu wuta. Wannan hari na zuwa ne wata guda bayan wani hari da aka kai wa wasu ‘yan ɗaurin aure daga Zariya a Jihar Filato, inda aka kashe su. Ƙungiyar Bokkos Cultural Development Forum (BCDF), ta tabbatar da faruwar...
    Koda ya ke dai, a lokacin ‘yansanda sun yi nisa ban gudanar bincike, amma babu wanda suka iya kamawa, kuma ba a kara shigar da wata sabuwar kara a gaban kotu ba, duk tsawon wadannan shekarun. Wannan bukatar da Muyiwa ya biro da ita, tamkar bude wani sabon babi ne, kan batun hallaka manyan mutane a kasar, wadda za a iya cewa, tun daga 1999, har zuwa yau, amma shiru ake ji, kan daukar wani kwakwaran mataki. A wani taro a kwanan baya, babban Lauya SAN Cif Kanu Agabi, ya bijiro da zargin yadda ake gaza hukunta masu aikata manyan laifuka a kasar, inda kuma ake samun dogon jan kafa, kan shari’ar da ta shafi, marasa karfi a kasar. Wannan...
    “Sauran su ne Lawan Haruna, Opurum Patrick, Agbo James da Georgewill Onwubiko da sauransu. “Shugaban PSC ya ce su tuna cewa su abokai ne ga kowa, kuma ya kamata a kowane lokaci su yi daidai da abin da ‘yan Nijeriya ke bukata. Ya kuma ba su tabbacin cewa hukumar za ta ci gaba da yin iya kokarinta don ganin an inganta yanayin aikinsu.” Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Ya ce tituna a Arewa sun lalace kuma gwamnati tana nuna rashin kulawa ga yankin. “Jiya da jirgi zan biyo na taho, amma aka ɗage jirgi daga ƙarfe 3 na yamma zuwa 8 na dare, sai na taho ta mota. Daga Abuja zuwa Kaduna zuwa Kano abin takaici ne. Wannan aikin titi tun lokacin farkon hawa gwamnatin APC ake yinsa.” Kwankwaso ya kara da cewa ana gudanar da manyan ayyuka a Kudu cikin hanzari, amma an bar ayyuka masu mahimmanci a Arewa babu kulawa. “Muna jin ana gina titi daga Kudu zuwa Gabas. Muna maraba da ci gaba a ko’ina a Nijeriya. Amma gwamnati tana ɗaukar duk arzikin ƙasa ta zuba a ɓangare ɗaya kaɗai, ba ta yin aiki da...
    Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta jaddada cewa: Dole ne kasashen duniya su dauki matakin dakatar da kisan kare dangi a Gaza Mataimakin shugaban kasar Iran na farko Muhammad Reza Aref ya jaddada cewa: Dole ne a kawo karshen kisan gillar da yahudawan sahayoniyya suke yi a yankin Zirin Gaza cikin gaggawa ta hanyar daukar matakai na zahiri da kuma dauri daga kasashen duniya. Aref ya rubuta a shafinsa na X a jiya Alhamis cewa: “Mutuwar mutanen da ba su ji ba ba su gani ba saboda yunwa sakamakon hana isar da abinci ga al’ummar Gaza da aka zalunta ya kasance tare da yin shiru na kunya daga kungiyoyin kare hakkin bil’adama na kasa da kasa.” Ya kara da cewa: “Dole...
    Ministan harkokin wajen kasar Iran ya jaddada cewa: Babu shakka Iran za ta ci gaba da inganta sinadarn Uranium Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Araqchi ya bayyana a jiya Alhamis dangane da tattaunawar da Iran za ta yi da kungiyar kasashen Turai da za a yi a yau Juma’a a birnin Istanbul na Turkiyya cewa; Za a ci gaba da inganta sinadarin Uranium a cikin kasar Iran, kuma kasar ba za ta yi watsi da wannan hakkin na al’ummar Iran ba. A cikin bayanin da ya yi a gefen ziyarar da ya kai ga iyalan shahidan Laftanar Janar Baqiri, Araqchi ya kara da cewa; Ko da yaushe Jamhuriyar Musulunci ta Iran a shirye take ta ci gaba da shirinta...
    Ya ce, nan da shekarar 2030 za a bukaci hekta miliyan 300 domin samar da bukatar abinci. Don haka ne ya ce taken taron ranar yaki da kwararowar hamada na 2025 na da matukar tasiri domin tabbatar da daukan matakan da suka dace wajen kiyaye hamada da gurbacewar muhalli. A cewarsa, yunkurin zai tunkari manyan kalubale kamar matsalar tattalin arziki da karancin abinci, karancin ruwa, da sauyin yanayi. Lawal ya jaddada cewa cimma muradun ci gaban zamantakewa da tattalin arzikin Nijeriya ba zai yuwu ba idan ba tare da kare muhalli da kuma kula da filaye da albarkatun kasa ba. Ya kara da cewa gwamnati na ba da fifiko ga al’amuran muhalli kuma ta samar da cibiyoyi, manufofi, tsare-tsaren ayyuka,...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba Bayan hadin kai da karfafa fahimtar juna wadanda hidimar kasa take kawowa, akan samu wasu masu hidimar da sukan yi amfani da duk wata dama da suka samu don neman na sakawa a bakin salati. Yayin da wasu masu hidimar kasa sukan kama sana’a ko su saka hannun jari a inda aka tura su, wasu kuwa komawa garuruwansu suke yi bayan sun kammala. NAJERIYA A YAU: Cututtukan da rumar daki ke haifarwa ga jikin mutum DAGA LARABA: Abubuwan da ya kamata yara su yi yayin hutun makaranta Shirin Najeriya a Yau na wannan lokaci zai yi nazari ne a kan irin damar da masu yi wa kasa hidima suke da ita a garuruwan...
      Kashe- Kashen 2025 Ya Fi Na 2024 Alkaluman bincike sun bayyana cewar ‘yan ta’adda sun dauki rayukan mutane a rabin wannan shekarar fiye da na shekarar 2024 da ta gabata kamar yadda Hukumar Kula da ‘Yancin Dan- Adam ta kasa ta bayyana a wannan watan. Kamar yadda alkaluman suka nuna, akalla mutane 2, 266 ne suka bakunci lahira a hannun ‘yan ta’adda a rabin shekarar 2025, idan aka kwatanta da mutane 1, 083 a rabin farko na shekarar 2024 da kuma mutane 2, 194 a bakidaya shekarar. Rundunar sojojin Nijeriya na fafatawar yaki da mayakan Boko- Haram da sauran ‘yan ta’adda a Arewa Maso- Gabas, ta’addanci da garkuwa da mutane a Arewa Maso- Yamma, hare- haren makiyaya da manoma...
    Asusun ba da lamuni na duniya IMF ya fada a wannan alhamis cewa yana shirin aikewa da tawaga zuwa kasar Senegal a cikin watan Augusta domin tattauna yadda aza magance matsalar basussukan da ke kan kasar  da kuma fara tattaunawa kan tsarin sabon shirin lamuni. Kasar Senegal na fama da bashin biliyoyin daloli da gwamnatin da ta shude ta karba, lamarin da ya sanya asusun lamuni na duniya IMF ya dakatar da shirin ba da lamuni ga kasar. A nasa bangaren kuma, wani mai magana da yawun IMF ya ce, “Asusun na bukatar karin bayanai kafin ya karfafa kimanta halin da ake ciki na basussukan kasar Senegal, sannan yana bukatar yarjejeniya kan muhimman matakan gyara.” Ya kara da cewa, “Da...
    Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya bayyana cewa yana yawan karanta rantsuwar kama aiki da ya yi domin tunatar da kansa nauyin da ya dauka na yi wa al’umma hidima bisa gaskiya da amana. Babban Sakataren Yada Labarai na Gwamna, Hamisu Mohammed Gumel, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da ya fitar a ranar Laraba bayan nadin sabon shugaban karamar hukumar Gumel. A wajen bikin da aka gudanar a zauren majalisar gwamnatin jihar da ke Dutse, Gwamna Namadi ya yi nuni da cewa rayuwa na da kurarran lokaci, don haka ya kamata shugabanni su kasance masu tsoron Allah da kuma sanin nauyin da ke kansu. “Rayuwa ba ta da tabbas, hakazalika shugabanci ba wasa ba ne”....
    Tsohon Gwamnan Kano, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso ya zargi Shugaba Bola Tinubu da mayar da yankin Arewacin Nijeriya saniyar ware, yana mai cewa shugaban ya fi mayar da hankali wajen gina kudancin ƙasar ta hanyar amfani da albarkatun ƙasar. Kwankwaso ya bayyana haka ne yau Alhamis a wajen taron bana kan shawarwari na masu ruwa da tsaki a Jihar Kano. Gwamnatin Yobe ta bada tallafi ga iyalan ’yan banga da suka rasu Hulk Hogan ya mutu yana da shekara 71 A cewarsam Tinubu ya yi watsi da halin da yankin arewacin ƙasar ke ciki wajen gina Kudancin Najeriya da kuma samar musu da kayan more rayuwa. “Bayanai da muka samu na nuna cewa kamar rabin kasafin kuɗi na tafiya zuwa...
    Gwamnatin Jihar Yobe ta raba tallafin kuɗi ga iyalan ’yan banga da suka rasa rayukansu da kuma waɗanda suka samu raunuka a bakin aiki.   Kuɗaɗen wanda Daraktan ayyuka na musamman, Muhammad Alhaji Baba ya miƙa a madadin sakataren gwamnatin jihar sakamakon umarnin da Gwamna Mai Mala Buni ya bayar na a yi hakan. Hulk Hogan ya mutu yana da shekara 71 An rantsar da Nentawe sabon shugaban APC na ƙasa Wannan shiri dai wani ɓangare ne na shirin jin daɗin jama’a na jaha ga jami’an tsaro domin tabbatar da cewa, iyalan ’yan banga da abin ya shafa sun samu tallafi. A ƙarƙashin shirin, kowane dangin ɗan banga da ya rasu ya karɓi Naira dubu ɗari ₦500, yayin da waɗanda suka jikkata...
    Kafafen watsa labarun HKI sun ce wani mutum a cikin motar da yake tukawa ya nufi kan ‘yan sahayoniya a mahadar “Hahsrun” a kusa da “Kafar-Yona”dake yammacin Tul-Karam. Bayan da matumin ya take ‘yan sahayoniyar ya fice daga yankin ba tare an iya tsayar da shi ba. Majiyar ta kara da cewa; 9 daga cikin ‘yan sahayoniyar da su ka jikkata sojoji ne. Tashar talabijin din ta 12: ta ambaci cewa; Wanda ya take sojojin ya iya gudu daga wurin, ba tare da an tsayar da shi ba. Ita kuwa jaridar ‘ Yasrael Home” ta bayyana cewa; An baza ‘yan sanda a wurin da aka kai hari, domin gano inda maharin yake. Kungiyoyin Falasdinawa sun yi maraba da wannan harin,...
    Ministan Noma na Iran Gulam Riza Nuri Qazlajeh ya fada a yau Alhamis cewa; Iran tana a cikin kasahe biyar na sahun gaba da su ka yi fice wajen  dabbobi. Minstan wanda yake jawabi a wani kamfani na samar da nono, ya ce, Iran tana da niyyar kara yawan dabbobin da suke samar da nono ta hanyar kyautata da kula da lafiyarsu, domin rage dogaro da waje samar da nama da kuma nono.” Haka nan kuma ministan na noma ya kara da cewa; Kara yawan dabbobin da ake samarwa a cikin gida,wata lalura ce ta tattalin arziki, da kuma kishin kasa.  Ministan Noma na Iran ya kuma kara da cewa, ma’aikatar tasu tana kokarin ganin mayar da Iran zama cibiyar...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Majiyar asibitocin yankin Gaza ta tabbatar da cewa, Falasdinawa 115 sun yi shahada sanadiyyar yunwa saboda karewar abinci a cikin yankin. Ita kuwa hukumar Agajin MDD dake aiki a Falasdinu “Unrwa” ta sanar da cewa tana da dubban manyan motoci da suke cike da kayan abinci suna jiran a ba su umaranin shiga Gaza.” Motocin suna dauke da kayan abinci, ruwa da magani a cikin kasashen Jordan da Masar.  A wani bayani da ofishin gwamnatin Gaza ya fitar a yau Alhamis, a cikin yankin Gaza duk wani abinci, ruwa da magani duk sun kare, don haka a halin yankin yankin yana da bukatuwa da buhunan filawa 500,000 a kowane mako.  An shiga kwanaki 145 da HKI ta rufe dukkanin mashigar...
    Shahararren ɗan kokawa ɗan ƙasar Amurka mai ritaya Terry Gene Bollea wanda aka fi sani da Hulk Hogan ya rasu yana da shekara 71 a duniya. A cewar TMZ da sauran rahotanni, likitoci sun mayar da martani a gidansa na Clearwater, da ke Florida da sanyin safiyar Alhamis kan Hulk Hogan ya kamu da bugun zuciya da ya yi ajalinsa. An rantsar da Nentawe sabon shugaban APC na ƙasa Kwalara: Mutum 13 sun mutu sama da 236 na jinya a Neja Daga nan an ɗauki Hogan da wuri aka saka shi cikin motar ɗaukar marasa lafiya. Duk da damuwa na kwanan da aka bayyana game da lafiyarsa – ciki har da larurar wuyansa a farkon wannan shekara, matarsa ​​Sky ta...
    Kwanan nan, darektar zartaswa ta hukumar kula da matsugunan dan Adam ta MDD, Anacláudia Rossbach, ta yi hira da wakilin babban rukunin gidajen rediyo da talabijin na Sin wato CMG, a hedkwatar hukumar kula da matsugunan dan Adam ta MDD dake Nairobi, babban birnin Kenya. Yayin da aka ambato sakamakon da ya fi jawo hankali da Sin ta samu yayin kyautata kauyuka zuwa matsayin birane da garuruwa, Rossbach ta bayyana cewa, Sin ta cimma nasarar kawar da talauci ga mutane miliyan 800, da kuma tafiya a kan hanyar kyautata kauyuka zuwa birane da garuruwa, kuma wannan darasi ne da ya cancanci kasashen Afirka wadanda suke fuskantar kalubalen kyautata kauyuka zuwa birane su yi koyi da shi. Ta ce, nan da...
    A cewar ministan, shi da sauran abokan aikin sa, Ministan Lafiya, Farfesa Muhammad Ali Pate, da Ministan Kuɗi, Mista Wale Edun, sun halarci bikin ƙaddamar da ɗaya daga cikin manyan ayyukan, wanda ya gudana a Jihar Katsina.   Cibiyoyin da aka ƙaddamar na cikin zagaye na farko na shirin gina sababbin cibiyoyin maganin ciwon daji guda shida a manyan Asibitocin Koyarwa na Tarayya a ƙasar nan.   Wannan cigaba wani muhimmin mataki ne wajen rage wahalar da marasa lafiya ke fuskanta wajen samun ingantacciyar kulawa, da kuma hana fita ƙasashen waje don neman magani.   Gwamnatin ta tabbatar da cewa sauran cibiyoyin da suka rage za su kammala nan ba da jimawa ba domin cika alƙawarin samar da ingantaccen tsarin...
    Aikin gina tsibirin ciniki maras shinge na Hainan na kasar Sin ya samu gagarumin ci gaba sosai, inda gwamnatin kasar Sin ta sanar a jiya cewa, a ranar 18 ga watan Disamban bana, za a kaddamar da manufar kafa “kwastam mai zaman kansa a duk faɗin tsibirin ciniki maras shinge na Hainan” a hukumance, wadda ke nufin saukaka bincike da ragewa ko soke haraji. “Ana iya cin moriyar manufofin ba da fifikon harajin kudi a tsibirin Hainan”, sannan “mu’amalar Hainan da kasashen duniya za ta kasance cikin ’yanci da lumana”. A ra’ayin jama’a na kasa da kasa, wannan wani muhimmin mataki ne ga kasar Sin na kara fadada bude kofa ga ketare, wanda ba bunkasa ci gaban tattalin arzikin kasar...
    An samu ɓarkewar cutar amai da gudawa wato kwalara a ƙananan hukumomi shida na Jihar Neja, inda rahotanni suka ce mutum 13 ne suka mutu tare da wasu mutane sama da 236 da ke jinya a asibiti. An fara samun ɓullar cutar ne a Ƙaramar hukumar Shiroro tun a ranar Lahadin da ta gabata zuwa Ƙananan hukumomin Bosso da Minna da Magama da Bida da Munya, inda jami’an kiwon lafiya suka tabbatar da ƙaruwar ɓullar cutar a ƙananan hukumomin da abin ya shafa. Jirgin Rasha mai dauke da mutum 50 ya yi hatsari a China Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe Majiyoyi sun bayyana cewa, yankunan Chanchaga a Minna da Bosso da Shiroro na daga cikin...
    An samu ɓarkewar cutar amai da gudawa wato kwalara a ƙananan hukumomi shida na Jihar Neja, inda rahotanni suka ce mutum 13 ne suka mutu tare da wasu mutane sama da 236 da ke jinya a asibiti. An fara samun ɓullar cutar ne a Ƙaramar hukumar Shiroro tun a ranar Lahadin da ta gabata zuwa Ƙananan hukumomin Bosso da Minna da Magama da Bida da Munya, inda jami’an kiwon lafiya suka tabbatar da ƙaruwar ɓullar cutar a ƙananan hukumomin da abin ya shafa. Jirgin Rasha mai dauke da mutum 50 ya yi hatsari a China Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe Majiyoyi sun bayyana cewa, yankunan Chanchaga a Minna da Bosso da Shiroro na daga cikin...
    An cimma matsaya kan zaɓensa bayan wata ganawa da aka yi a Abuja tsakanin Shugaba Bola Tinubu da gwamnonin APC. Ana sa ran manyan shugabannin jam’iyyar za su tabbatar da naɗinsa a yau Alhamis. Farfesa Yilwatda, ya fito ne daga Jihar Filato da ke yankin Arewa ta Tsakiya, yankin da suke da alhakin riƙe kujerar shugabancin jam’iyyar. Wasu daga cikin ‘ya’yan jam’iyyar sun ce kasancewarsa Kirista zai taimaka wajen daidaita shugabanci, duba da cewa shugaban ƙasa da mataimakinsa Musulmai ne. Shugabannin jam’iyyar na fatan Farfesa Yilwatda zai kawo sabon salo, tare da haɗa kan jam’iyyar kafin tunkarar zaɓe mai zuwa. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura...
    Wani jrigin saman fasinjoji mallakin kasar Rasha da ke dauke da mutum 50 ya yi hatsari a kusa da yankin Amur na kan iyakar kasar China. Kafar yada labarai ta Sky News ta rawaito cewa jirgin wanda ke dauke da fasinjoji, ciki har da kananan yara biyar da kuma ma’aikatan jirgi su shida, ya fadi ne ranar Alhamis ba tare da ko mutum daya ya rayu ba. “Ma’aikatan ceto sun gano wasu sassan jirgin na ci da wuta,” kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya rawaito jami’an ceton na cewa. Reuters ya kuma ce jirgin wanda mallakin kamfanin Angara Airlines ne, ya fadi ne a kusa da Tyndra, wani gari da ke yankin na Amur, bayan hanyar da yake...
    Ruwan sama kamar da bakin kwarya hade da iska sun yi ajalin mutum biyar sannan wasu 92 suka samu munanan raunuka a kananan hukumomi bakwai na jihar Yobe. Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (SEMA) Dr Goje ne ya tabbatar da hakan a ranar Laraba a Damaturu. Ya ce iftila’in ya shafi al’ummomi 48 ne a fadin kananan hukumomin da lamarin ya faru. Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace Dr Goje yan kuma ce bala’in ya shafi gidaje 1,264, tare da raba mutum 5,022 da muhallansu. Shugaban ya kuma ce hukumarsa tare da hadin gwiwar kungiyar bayar da tallafi...
    Ruwan sama kamar da bakin kwarya hade da iska sun yi ajalin mutum biyar sannan wasu 92 suka samu munanan raunuka a kananan hukumomi bakwai na jihar Yobe. Shugaban Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta jihar (SEMA) Dr Goje ne ya tabbatar da hakan a ranar Laraba a Damaturu. Ya ce iftila’in ya shafi al’ummomi 48 ne a fadin kananan hukumomin da lamarin ya faru. Matar aure ta kashe mijinta a kan abinci a Yobe Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace Dr Goje yan kuma ce bala’in ya shafi gidaje 1,264, tare da raba mutum 5,022 da muhallansu. Shugaban ya kuma ce hukumarsa tare da hadin gwiwar kungiyar bayar da tallafi...
    Kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya ya fara tattauna masifar da ta faru a Gaza tare da jaddada kawo karshen kisan kiyashi  yanki Kwamitin tsaron Majalisar Dinkin Duniya ya gudanar da wani sabon zama domin tattauna batutuwan da suke faruwa a Gaza da kuma tabarbarewar al’amuran jin kai a yankin, inda ake ci gaba da yin kiraye-kirayen gaggauwa da kuma kira ga kasashen duniya da su dauki kwararan matakai na kawo karshen bala’in da ya biyo bayan yakin kisan kare dangi a yankin. Majalisar Dinkin Duniya ta yi kira da a hanzarta dakatar da tilastawa al’ummar Gaza gudun hijira kamar yadda ta bukaci gwamnatin mamayar Isra’ila da ta ba da damar kai agajin jin kai ga al’ummar Zirin Gaza. Mataimakin babban...
    Asusun Kula da Kananan Yara na Majalisar Dinkin Duniya ya yi gargadi karuwar bala’i na jin kai a Gaza Kazem Abu Khalaf, kakakin hukumar UNICEF a Falasdinu, ya tabbatar da cewa: Abin da ke faruwa a Gaza ba a taba ganin irinsa ba, yana mai cewa har yanzu yana ci gaba da tuntubar wasu ma’aikatan jin kai da dama da suka yi balaguro zuwa yankunan da ake fama da rikici, da bala’o’i, da wuraren yaki a duniya, kuma dukkansu, ba tare da togiya ba, sun amince cewa, ba su taba ganin wani yanayi mai kama da abin da ke faruwa a Gaza ba. Abu Khalaf ya yi nuni da cewa: Mutanen yankin Zirin Gaza sun fara fama da yunwa, sannan...
    Ministan lafiya na kasar Kamaru, Manaouda Malachie ya bayyana jiya Talata 22 ga wata a Yaounde cewa, hadin-gwiwar Kamaru da Sin a bangaren kiwon lafiya ta haifar da babban alfanu ga jama’ar Kamaru, kana alama ce dake shaida dangantakar kut da kut gami da dadadden zumunci tsakanin jama’ar kasashen biyu. A wajen bikin cika shekaru 50 da kaddamar da hadin-gwiwar Sin da Kamaru ta fuskar kiwon lafiya wanda aka yi a jiya Talata a birnin Yaounde, minista Malachie ya gabatar da jawabi yana mai cewa, hadin-gwiwar kasashen biyu ta fuskar kiwon lafiya ta shaida cewa, kwalliya za ta iya biyan kudin sabulu, idan aka raya hulda mai aminci, da sahihanci kuma bisa muradu iri daya tsakanin kasa da kasa. Gwamna...
    Wani mummunan al’amari ya faru a Ƙaramar Hukumar Fika da ke Jihar Yobe, inda wata mata mai shekara 35, ta kashe mijinta da itace bayan rikici ya ɓarke a tsakaninsu a kan abinci. Rahotanni sun nuna cewa matar wacce ’yar garin Abba ce, ta ɗauki katon itacen girki ta rafka wa mijinta bayan rikici ya ɓarke a tsakaninsu. Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 95 a Neja, sun ceto mutum 138 da aka sace Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan sama da mutum 100 Kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Dungus Abdulsalam, ya ce bayan faruwar lamarin, an sanar da ’yan sanda kuma nan take suka kama wacce ake zargi. Marigayin ya rasu nan take, kuma ya bar mata biyu da...
    Hukumomin rikon kwaryar Siriya sun rufe hanyoyin zuwa birnin Sweida bayan sake bullar wani tashin hankali Dakarun gwamnatin Siriya na ci gaba da rufe hanyoyin da ke shiga lardin Sweida da ke kudancin kasar tun daga wayewar garin ranar Asabar, bayan kazamin fadan da aka gwabza tsakanin kabilar Bedouin da mayakan Duruz a cikin birnin. A halin da ake ciki, ana ci gaba da kokarin da ake yi na cikin gida da waje na wanzar da tsagaita bude wuta da kare fararen hula. Ana zaman dar dar a lardin Suwayda da ke kudu maso yammacin kasar Siriya, inda dakarun gwamnati ke ci gaba da rufe hanyoyin da ke shiga lardin tun da safiyar Asabar, bayan kazamin fadan da aka gwabza...
    Dakarun Sojin Najeriya sun kashe gomman ’yan ta’adda a Ƙananan Hukumomin Rijau da Mariga a Jihar Neja. ’Yan ta’addan sun fito ne daga Jihar Zamfara, yayin da suke tafiya a kan babura ɗauke da muggan makamai. Zamfarawa sun yi zanga-zanga kan kisan mutum sama da 100 Nentawe Yilwatda ne zai zama sabon shugaban APC na ƙasa Sojoji tare da taimakon jiragen yaƙi na sama sun kai farmaki bayan samun bayanan sirri. Aƙalla ’yan ta’adda 95 aka kashe a yayin artabun. Sojojin sun kuma lalata babura 18 tare da ƙwato bindigogi kirar AK-47. Sai dai an yi rashin sa’a soja guda ɗaya ya rasa ransa a yayin fafatawar. Dakarun sun sake kai wani farmaki na biyu inda suka ƙwato makamai da...
    Tawagar kwararru daga hukumar makamashin Nukliya IAEA zata ziyarci kasar Iran nan ba da daewa ba. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Kazem Gharibabadi mataimakin ministan harkokin wajen kasar a bangaren sharia da kuma harkokin kasashen waje ne ya bayyana haka. Ya kuma kara da cewa tawagar zata tattauna da Jami’an gwamnatin kasar Iran kan yadda mu’amalar hukumar zata kasance da Iran.  Gharibabadi ya bayyana cewa idan kasashen yamma sun yi kokarin amfani da shrin SnapBack na yarjeniyar JCPOA zasu gamu da maida martani mai tsanani, sannan ya kara da cewa mu’amala da hukumar IAEA da kasar Iran zata sauka saboda amfani da karfi kan cibiyoyin nukliyar kasar Iran wanda Amurka da HKI suka yi a kallafeffen...
    Dakarun Sojin Operation Hadin Kai, sun daƙile hare-haren Boko Haram a garuruwan Monguno da Bitta da ke Jihar Borno, tare da wani kashe babban Kwamandan Boko Haram mai suna Ibn Khalid. Sun kuma kashe ’yan ta’adda da dama, ciki har da wani babban kwamandan ƙungiyar. NAJERIYA A YAU: Cututtukan da rumar daki ke haifarwa ga jikin mutum Tinubu ya sake miƙa buƙatar karɓo bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare Mataimakin Daraktan Hulɗa da Jama’a na Rundunar, Kapten Reuben Kovangiya, ya ce sojojin sun yi jarumta wajen hana ’yan ta’addan shiga Monguno. Ya ce sojojin sun yi amfani da manyan makamai wajen mayar da martani, inda suka kashe ‘yan ta’adda da dama, ciki har da wani babban kwamandan Boko Haram mai...
    Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya miƙa wa Majalisar Dokokin Tarayya buƙatar ƙara ranto bashin Dala miliyan 347 daga ƙetare, ƙarƙashin shirin ciyo bashin na gwamnatin tarayyar na 2025 zuwa 2026. Hakan na ƙunshe cikin wata takarda da Tinubu ya aikewa majalisar, wadda Shugaban Majalisar Wakilai, Tajudeen Abbas ya karanto a zamansu na yau Laraba. Dalilin da muka gaza biyan ma’aikata mafi ƙarancin albashi — Gwamnatin Borno WFP zai dakatar da tallafin abinci da kiwon lafiya a Nijeriya Takartar ta ambato shugaban ƙasar na cewa karɓar rancen ya zama tilas saboda buƙatar ƙarin kuɗi da aka yi a aikin babbar hanyar Lagos zuwa Calabar, wanda ya tashi daga Dala miliyan 700 zuwa Dala miliyan 747 — ƙarin Dala miliyan 47 ke...
    Gwamnatin Borno ta bayyana yawan ma’aikata a matsayin dalilin da ya sanya ƙananan hukumomin jihar ba za su iya biyan mafi ƙarancin albashin ma’aikata na Naira dubu 70,000 ba. Gwamnatin ta ce ta umarci shugabannin ƙananan hukumomin jihar su samar da tsari mai ɗorewa domin ƙaddamar da fara aikin mafi ƙarancin albashin. WFP zai dakatar da tallafin abinci da kiwon lafiya a Nijeriya Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi Babban sakataren ma’aikatar kula da ƙananan hukumomi da masana’antu, Modu Alhaji cikin wata sanarwa da ya fitar ya ce yawan ma’aikatan ne ya haifar da jinkiri wajen fara biyan mafi ƙarancin albashin. Modu ya yi bayanin cewa a wasu lokutan gwamnatin tarayya na turo ƙasa da Naira...
    Kungiyoyin agaji da kuma na hakkokin bil’adama sun yi gargadi akan yunwar da ake fama da ita a Gaza, tare da yin kira ga gwamnatoci da su yin matsin lamba domin kawo karshe killace Gaza da aka yi, da kuma shigar da kayan agaji a cikin yanki. Kungiyoyin sun kuma dorawa HKI alhakin halin da mutanen Gaza suke ciki na yunwa. Daga cikin kungiyoyin da su ka fitar da bayani da akwai Majalisar ‘yan gudun hijira ta kasar Norway” da “Refugee International” da wasu da adadinsu ya kai 111, sun yi gargadi akan yadda yunwa take yaduwa a cikin Gaza. Bayanin ya kunshi cewa; Mazauna yankin Gaza suna fama da yunwa saboda killace su da Isra’ila ta yi, kuma a...
    Shirin Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya bayyana cewa daga ƙarshen watan Yuli, zai dakatar da tallafin gaggawa na abinci da kiwon lafiya ga mutum miliyan 1.3 a Arewa maso Gabashin Nijeriya saboda ƙarancin kuɗi. Darektan WFP a Nijeriya, David Stevenson, ya ce kayan abinci da na kiwon lafiya sun ƙare gaba ɗaya, kuma rabon da ake yi yanzu shi ne na ƙarshe. Matasa 3 sun rasu yayin wanka a rafi a Bauchi 2027: Obi zai iya takara ba tare da ni ba — Datti Baba-Ahmed Ya ce tallafin zai tsaya ne daga ƙarshen watan Yuli, lokacin da aka ƙiyasta kayan abinci da na kiwon lafiyar za su ƙare gaba ɗaya. Idan ba a samu tallafi cikin gaggawa ba,...
    Babban abin dubawa a nan shi ne ko mene ne hikimar tura irin wadannan bakin haure zuwa kasashen Afirka? Misali kamar bakin hauren da Amerika take son turawa Nijeria, ’yan asalin kasar Venezuela, ko kuma bakin hauren da Sudan ta kudu ta karba ’yan asalin Myammar, da Cuba da Vietnam, al’adunsu da harshensu sun sha banban da na ’yan Afirka. Sabo da haka babu wata alaka tsakanin juna. To idan ba domin isgilanci da gadara ba, ta yaya Mr. Trump zai nemi tursasawa kasashen Afirka karbar irin wadannan bakin haure maimakon ya tasa keyarsu zuwa kasashensu na asali?(Lawal Mamuda) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye...
    Hukumar Raya Yankin Arewa Maso Gabas (NEDC), tare da haɗin gwiwar Gwamnatin Jihar Yobe, sun fara rabon kayayyakin gini ga mutanen da ambaliyar ruwa ta shafa a ƙananan hukumomi 13 na jihar. Wannan taimako na da nufin tallafa wa mutanen da ambaliya ta rushe musu gidaje. Tinubu na amfani da ƙarfin mulki wajen tsoratar da ’yan adawa — Sule Lamido An kone babur din ‘barayin waya’ a Kano A lokacin da aka fara rabon kayayyakin a Damaturu, wakilin babban daraktan NEDC, Farfesa Ibrahim Ali Abbas, ya ce hukumar ta kawo kayayyakin rufin gida da sauran kayan gini don taimaka wa mutane su gyara ko sake gina gidajensu. Baya ga wannan, hukumar ta kuma bai wa Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa...
    Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Sule Lamido, ya zargi Shugaba Bola Tinubu da amfani da hukumomin gwamnati wajen danne ’yan adawa. Ya bayyana hakan ne yayin wata hira da ya yi da manema labarai a Kano. Uwa ta kashe ’ya’yan cikinta biyu saboda kuncin rayuwa An kone babur din ‘barayin waya’ a Kano Lamido, ya ce hukumomi irin su EFCC ana amfani da su ne wajen matsa wa ’yan adawa lamba. Ya bayar da misalin tsohon Gwamnan Delta, Ifeanyi Okowa, wanda ke fuskantar tuhuma kan zargin aikata almundahana. A cewarsa bayan Okowa ya koma jam’iyyar APC, an daina tuhumarsa. Ya kafa misali da wata magana da Sanata Adams Oshiomhole ya taɓa yi. Ya ce: “Da zarar ka shiga APC, an yafe...
    Ana zargin wata uwa a jihar Enugu da kashe ’ya’yanta biyu saboda tsananin kuncin rayuwa. Lamarin ya faru a unguwar Trans Ekulu da ke yankin birnin na Enugu. An kone babur din ‘barayin waya’ a Kano Natasha za ta sake komawa kotu kan hana ta shiga harabar majalisa An ga gawarwakin yara biyu a gidan lokacin da jami’an tsaro sukashiga ciki, lamarin da ya tayar da hankulan jama’ar unguwar. Yaran da ake zargin uwar tasu da kashewa sun hada da yarinya mai suna Esther Arinze mai shekara hudu da haihuwa da kuma kaninta mai suna  Chibusoma. Ana zargin an yi amfani da makami mai kaifin gaske wajen ji wa yaran raunuka a jikunansu kafin su rasu. Majiyar labarinmu da rundunar...
    Kwamishinan Ilimi na Jihar, Dokta Ali Haruna Makoda, ya buƙaci iyaye da su tabbatar da cewa ‘ya’yansu sun koma makaranta a kan lokaci. Ya yi gargaɗin cewa duk ɗalibin da ya makara wajen dawowa makaranta zai iya fuskantar hukunci. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya zargi tsohon shugaban kasar Barack Obama da cin amanar kasa tare da yin kira da a yi masa shari’a Shugaban kasar Amurka Donald Trump ya zargi magabacinsa, Barack Obama da cin amanar kasa, inda ya bukaci a gurfanar da shi a gaban kuliya kan wani rahoton sirri da ya nuna cewa; Jami’an gwamnatin Obama sun murguda bayanai game da katsalandan din Rasha a zaben Amurka na shekara ta 2016. Kalaman na Trump sun zo ne yayin wani taron manema labarai a ofishin Oval, wanda shugaban kasar Philippines Ferdinand Marcos ya halarta. Yana cewa:”Bisa ga abin da ya karanta…tsohon shugaba Obama ne ya fara wannan badakalar,” ya kara da cewa Obama shi ne “shugaba” na...
    More Podcasts Najeriya a Yau Daga Laraba A duk lokacin da aka ce an kammala zangon karatu, dalibai kan samu hutu don hutawa da yin wadansu abubuwa na daban da kuma ba su damar shakuwa da ’yan uwa da abokan arziki. Kamar yadda masana harkar harkar ilimi suka saba fadi, yawan karatu kan taho da nashi irin matsalolin, ya kuma kamata a ce ana ware wa dalibai wasu lokuta na musamman don samun hutu daga karatun da suka koya. NAJERIYA A YAU: Yadda tsadar taki ke hana noman masara da shinkafa DAGA LARABA: Makomar Siyasar Najeriya Bayan Rasuwar Shugaba Buhari Shirin Daga Laraba na wannan makon zai yi nazari ne kan abubuwan da ya kamata yara su ringa yi yayin...
    “Farfaɗowa na samuwa, kuma a bayyane yake cewa sabon yanayi na sauyi yana faruwa a Kaduna,” in ji shi. Ya jaddada cewa kyakkyawar gwamnati na nufin kula da buƙatun al’umma, musamman waɗanda rikici ya shafa. “Muna share hawayen waɗanda rikice-rikice suka shafa. Muna haɗa kan al’umma. Muna tabbatar da cewa kowa yana da wajen zama da jin cewa yana da muhimmanci,” in ji Tinubu. Shugaban ya yaba wa gwamnatin Jihar Kaduna, ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro, da kuma hafsan hafsoshin tsaro bisa matakan soja da na lumana da suke ɗauka don shawo kan matsalar tsaro. “Zaman lafiya na gaskiya sai an gina shi, ba zai zo da ƙarfi ko tsoratarwa ba,” in ji shi. Ya...
    Shugaba Masoud Pezeshkian ya yi watsi da hankoron Amurka na tunzura kawayenta, musamman gwamnatin Haramtacciyar Kasar Isra’ila, na yunkurin kawo karshen shirin nukiliyar Iran. Shugaban an Iran ya bayyana hakan ne yayin wata hira da gidan talabijin na Aljazeera na kasar Qatar a wannan  Talata, inda ya bayyana cewa, za a ci gaba da inganta sinadarin Uranium a kasar Iran nan gaba bisa tsarin dokokin kasa da kasa. Wannan yunkuri yasa an ga bangarorin biyu na Amurka da Isra’ila suna matsa lamba a kan sauran bangarori na duniya, tare da bayyana Shirin na Iran a matsayin mai matukar hadari ga duniya, da nufin samun goyon bayan kasashen duniya kan bakaken manufofisu a kan kasar ta Iran. Dangane da zargin da...
    Sakatare-janar na kungiyar Hizbullah Sheikh Naim Qasem ya fitar da wata sanarwa inda ya yi kakkausar suka da Allah wadai da abin da ya bayyana a matsayin yakin kisan kare dangi da Amurka da Isra’ila ke yi wa al’ummar Palasdinu a Gaza, yana mai zargin kasashen duniya da yin shiru a kan laifukan da suka zarce dukkan matakan jin kai da kuma kyawawan dabi’u na ‘yan adataka. “Abin da al’ummar Falasdinawan da ake zalunta ke jurewa a Gaza, tun daga cin zarafi na Amurka da Isra’ila, zuwa ta’addanci, kisan kiyashi, jefa su a cikin yunwa, da kashe jama’a, ya wuce duk wani mataki na lamirin dan adam,” in ji Sheikh Qassem. Ya kuma yi kakkausar suka ga gazawar manyan kasashen...
    Amurka ta yanke shawarar ficewa daga hukumar kula da ilimi da kimiya da al’adu ta Majalisar Dinkin Duniya UNESCO a karo na biyu saboda matakin da ta dauka na shigar da Falasdinu a matsayin mamba. Mataimakiyar sakatariyar yada labaran fadar White House Anna Kelly ta sanar da matakin a cikin wata sanarwa a ranar Talata. Kelly ta ce dalilin da ya suka dauki wannan kan hukumar UNESCO, shi ne ta tallafa wa shirye-shiryen da Amurka ke kallonsu a matsayin wadanda ba su dace da muradunta ba. “Shugaba Trump ya yanke shawarar janye Amurka daga UNESCO, wadda  ke kula da ayyuka a bangaren raya al’adu da ilimi da zamantakewar al’umma, saboda daukar wau matakai  wadanda ba su dace da manufofin Amurka...
    Wata sabuwar tashin-tashina ta sake kunno kai a yankin kahon Afirka a daidai lokacin da shugaban kasar Eritrea Isaias Afwerki ya yi gargadi kai tsaye ga firaministan Habasha Abiy Ahmed, inda ya yi kashedin sake kaddamar da wani yaki. Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da kasar Habasha ke kokarin shiga bangaren ruwa Eritra da kuma tabarbarewar dangantakar bangarorin biyu tun bayan rikicin Tigray. A cikin wani jawabi da ya yi ta gidan telebijin, shugaba Afwerki ya yi gargadin cewa adadin yawan jama’ar Habasha ba zai tabbatar da nasarar soji ba, yana mai nuni da dabarun yakin da  Habasha ta yi amfani da su a yakin da ya gabata, yana mai cewa duk da yawan sojojinta amma bata...
    A cewar Ringim, idan ana so a sami cigaban da ya shafi kowa da kowa a Arewacin Nijeriya da ma ƙasa baki ɗaya, to ana buƙatar siyasa irin ta Kwankwaso wadda ke mayar da hankali kan talakawa da gaskiya a mulki. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Gwamnan Jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, ya sanya hannu kan kudurin dokar da ta kafa Hukumar Hisba a matsayin hukuma ta dindindin a ƙarƙashin gwamnatin jihar. Hakan na kunshe ne a wata sanarwa da Sakataren Yada Labarai na gwamnan Hamisu Muhammad Gumel ya fitar ga manema labarai a Jigawa. Sanarwar ta bayyana cewa bikin sanya hannun ya gudana ne a zauren majalisar zartarwa na fadar gwamnati dake Dutse, inda manyan jami’an gwamnati suka halarta, ciki har da Mataimakin Gwamna, Injiniya Aminu Usman, da mambobin Majalisar Dokokin Jihar Jigawa karkashin jagorancin Mataimakin Kakakin Majalisar, Hon. Sani Isyaku. Ta ce Gwamna Namadi ya bayyana cewa wannan rana na ɗaya daga cikin manyan nasarorin da aka cimma, bayan kai-komo na sama...
    Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin Guo Jiakun, ya ce taron koli na Sin da kungiyar Tarayyar Turai ta EU karo na 25 dake tafe, zai taimaka wajen bunkasa tattaunawa bisa matsayin koli, da zurfafa shawarwari, da hadin gwiwa tsakanin sassan biyu, lamarin da zai biya bukatu da moriyarsu, da ma na sauran sassan duniya baki daya. Guo Jiakun, ya jaddada muhimmancin taron, kasancewar ya zo a gabar da harkokin cudanyar kasa da kasa ke fuskantar yanayi na tangal-tangal, da ma karuwar daukar matakan kashin kai daga bangare guda, da kariyar cinikayya. Ya ce, hadin gwiwar sassan biyu, ya haifar da manyan nasarori a baya, wanda hakan ya bunkasa ci gaba da daukakarsu, tare da samar da tarin alfanu ga...
    Babbar Kotun Tarayya da ke Bauchi ta yanke hukunci a kan gwamnatin jihar Bauchi da ta biya tsohon Akanta-Janar na jihar, Dakta Sa’idu Abubakar, Naira miliyan 100 a matsayin diyyar take masa haƙƙi da kuma tsare shi ba bisa ƙa’ida ba. Kotun ta kuma umarci gwamnati ta wallafa ban haƙuri a manyan jaridu guda biyu cikin kwanaki 14. Mai Shari’a Aminu Garba ya yanke wannan hukunci ne a ƙarar da Dakta Abubakar ya shigar, yana zargin gwamnati da jami’anta da take masa haƙƙi, da kama shi ba tare da bin ƙa’ida ba, da musgunawa. Ya bayyana cewa hakan ya saɓawa tanade-tanaden kundin tsarin mulki da kuma yarjejeniyar kare haƙƙin bil’adama ta Afrika. Tsohon Sakataren Gwamnatin Bauchi, Ibrahim Kashim, Ya Fice...
    Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Kungiyar ta malaman musulumi ta fitar da fatawa da a ciki ta bukaci gwamnatoci da al’ummar musulmi da su yunkura cikin gaggawa domin kawo karshen killace yankin Gaza da aka yi, da kuma wajabcin kai musu abinci da magunguna. Kungiyar malaman musulmin ta kuma bayyana abinda HKI take yi na killace mutanen Gaza fiye da miliyan biyu da haka su abinci da magani,musamman mata, yara da manya,wani babban laifi ne da ba shi da tamka a cikin tarihi, tana mai yin kira ga al’ummu da gwamnatoci da su motsa saboda su taimaki raunana. Kwamitin fatawa da yake a karkashin wannan kungiyar ta malaman musulmi, ya dogara da ayoyin alkrur’ani da hadisan ma’aiki ( s.a.w) da manufofi na shari’a da ka’idoji...
    Yar wasan gaba ta Nijeriya, Chinwendu Alozie, ce ta tabbatar da nasara da kwallon da ta jefa kafin tashi daga wasan. Wannan nasara ta ba wa tawagar ta Justin Madugu damar kaiwa wasan ƙarshe na gasar.   Yanzu haka, Super Falcons za su kara da ƙasar da za ta yi nasara tsakanin Moroko, wacce ke masaukin baki, da Ghana, a wasan da za a buga daga baya a yau Talata.   Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe Shiga zaurenmu na WhatsApp
    Shugaban kasar Iran Mas’ud Fizishkiyan ya bayyana cewa; Batun kare hakkin bil’adama da ake yi a duniya ba komai ba ne sai karya. Shugaba Fizishkiyan ya yi ishara da yadda masu ikirarin kare hakkin bil’adama suke sa kafafunsu suna take hakkin mutanen Gaza da cikin kasashen yammacin Asiya da kuma tafka manyan laifuka. A yau Talata ne dai shugaban kasar ta Iran ya gabatar da jawabi a wurin bikin girmama shahidan kallafaffen yaki na kwanaki 12, ya bayyana cewa: “A cikin wannan duniyar wacce take riya ci gaba da wayewa, a gaba idon duniya, ake yanke wa mutanen Gaza ruwan sha da abinci, a hana mata da kananan yara. Haka nan kuma ake tafka laifukan da su ka kunshi kisan...
    Fira ministan HKI wanda kotun duniya ta manyan laifuka take nem ruwa a jallo ya bayyana cewa; Babu yadda za su tsayar da yakin Gaza, matukar kungiyar Hamas ba ta mika wuya baki day aba. Benjemine Netanyahu ya kuma ce; A lokacin da Hamas za ta mika makamanta ne, shi ne za mu yi tunanin ko za mu bude mata hanyar ficewa daga Gaza, da kuma dakatar da yaki. A gefe daya tashar talabijin din CNN ta ambato wata majiya ta gwamnatin Amurka tana cewa; Amurka ta gargadi kungiyar Hamas akan cewa, hakurinta ya kusa karewa akan batun tsagaita wuta, tare da neman kungiyar ta gwagwarmaya ta bayar da jawabi a cikin gaggawa kafin makwanni biyu masu zuwa. Tashar talabijin...
    Asusun kula da ƙananan yana na Majalisar Ɗinkin Duniya UNICEF, ya ce ya wani sabon bincike da ya gudanar ya banƙado yadda cin zarafin ƙananan yara da kuma kulle su ba bisa ƙa’ida ba ke ci gaba da bazuwa a Nijeriya. A cikin rahoton da ya fitar ranar Litinin, UNICEF ya ce har yanzu akwai dubban ƙananan yara da gwamnati ta rufe su ba kuma tare da cikakken bayani ga iyalansu ba, wasu ma a yanzu babu cikakken bayani kan inda suke ko kuma halin da suke ciki. Zazzaɓin Lassa ya kashe mutum 151 a Nijeriya bana — NCDC Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa Asusun ya ce a Nijeriya rufe ƙananan yara tare da...
    Yuro biliyan 4 Yen biliyan 15 (na Japan) Tallafin dala miliyan 65 Kuma aron cikin gida ta hanyar sayar da hannun jarin gwamnati (bond) na kusan Naira biliyan 757. Har ila yau, akwai shirin tara kuɗi har dala biliyan 2 ta hanyar takardun lamuni da za a fitar cikin ƙasa amma a kuɗin ƙetare. Shugaban kwamitin kasafi, Sanata Olamilekan Solomon, ya ce wannan amincewa tsarin doka ce kawai, domin an riga an haɗa bashin cikin tsare-tsaren kasafin kuɗi da MTEF tun da farko. Sanata Sani Musa (Niger Ta Gabas) ya bayyana cewa wannan shiri ba na shekara ɗaya ba ne, amma zai shafi rabon kuɗi na tsawon shekara shida, yana mai jaddada cewa Nijeriya ba ta taɓa gazawa wajen biyan...
    Hukumar Hisbah ta ce ta kama tare da lalata barasa da ta kai kimanin naira miliyan 5.8 a karamar hukumar Kazaure ta Jihar Jigawa. Kwamandan Hisbah a jihar Malam Ibrahim Dahiru ne ya bayyana haka a wata hira da manema labarai a Dutse, babban birnin jihar. Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati  Ya ce an gudanar da aikin ne karkashin jagorancin shugaban hukumar da ke Kazaure, Mansur Dabuwa, inda aka lalata katan 400 na barasa da darajar kudinsu ya kai naira miliyan 5.8. Ya bayyana cewa an kama barasa da aka kona a lokacin samamen da aka kai a sassa daban-daban a...
    Hukumar yaƙi da cututtuka masu yaɗuwa a Nijeriya (NCDC) ta ce adadin mutanen da zazzaɓin lassa ya kashe bana sun kai 151 a fadin kasar. Cikin wata sanarwa da NCDC ta wallafa a shafinta na X ranar Litinin, ta ce yawan kisan da cutar zazzaɓin lassa ke yi ya ƙaru daga kashi 17.3 cikin 100 da aka samu a bara. Jami’an tsaro sun dakile yunkurin Sanata Natasha na shiga harabar Majalisa Kamfanonin lantarki za su katse wuta kan bashin N5.2trn da suke bin gwamnati  Sanarwar ta ce an yi bitar alkaluman mamatan a bana ne bisa  la’akari adadin waɗanda suka kamu kuma ta yi ajalinsu a shekarar 2024. Hukumumar ta ce alkaluman mamatan ya kai kashi 18.9 cikin 100 na...
    Kamfanonin wutar lantarki sun yi barazanar katse wutar a fadin Najeriya saboda tarin bashin da ya haura Naira tiriliyan 5.2 da suke bin gwamnati. Taurin bashin, wanda ke barazana ga ci gaba da ayyukan kamfanoni, ya hada da Naira tiriliyan 1.2 na wutar da aka samar a watanni shidan farkon shekarar 2025, da Naira tiriliyan 2 daga 2024, da kuma bashin da aka gada tun daga 2015 wanda ya kai Naira tiriliyan 1.9. Shugabar ƙungiyar kamfanonin samar da wutar lantarki, Dakta Joy Ogaji, ta bayyana cewa kamfanonin sun daɗe suna nuna kishin ƙasa ta hanyar ci gaba da samar da wuta duk da rashin biyan su kuɗaɗensu, amma yanzu sun gaji. Ta bayyana cewa kudin da ake kashewa wajen samar...
    Kamfanonin wutar lantarki sun yi barazanar katse wutar a fadin Najeriya saboda tarin bashin da ya haura Naira tiriliyan 5.2 da suke bin gwamnati. Taurin bashin, wanda ke barazana ga ci gaba da ayyukan kamfanoni, ya hada da Naira tiriliyan 1.2 na wutar da aka samar a watanni shidan farkon shekarar 2025, da Naira tiriliyan 2 daga 2024, da kuma bashin da aka gada tun daga 2015 wanda ya kai Naira tiriliyan 1.9. Shugabar ƙungiyar kamfanonin samar da wutar lantarki, Dakta Joy Ogaji, ta bayyana cewa kamfanonin sun daɗe suna nuna kishin ƙasa ta hanyar ci gaba da samar da wuta duk da rashin biyan su kuɗaɗensu, amma yanzu sun gaji. Ta bayyana cewa kudin da ake kashewa wajen samar...
    Gwamnatin ƙasar Guinea ta rufe wasu sassan kamfanoni guda 1,724 sakamakon kama su da laifin ƙin bin dokokin hukuma, yayin da aka janye kayayyakin da suke sarrafawa daga kasuwa. Sanarwar na zuwa ne ƙarƙashin ma’aikatar kasuwanci a ƙasar, tana mai cewa an ɗauki matakin ne don kare lafiyar masu sayen kayayyakin da kuma tabbatar da kare muhalli, da kuma tilasta musu biyayya ga dokokin tafiyar da kamfanoni. Ma’aikatar kasuwanci ta ƙasar ta ce ba shakka wannan mataki zai zama tamkar hannunka mai sanda ga sauran kamfanoni da ke tafiyar da ayyukansu ba dai-dai ba. Da yake magana shugaban ƙungiyar masu sayen kayayyaki na ƙasar, Ousmane Keita, ya ce tun shekaru sama da uku suke ta wannan kiraye-kiraye, amma ba a...
    Asibitin Koyarwa na Jami’ar Abubakar Tafawa Ɓarkewa (ATBUTH) da ke Bauchi zai fara gwajin rigakafin cutar zazzabin Lassa. Wannan shiri na da nufin tabbatar da ingancin rigakafin, kuma wani ɓangare ne na babban shiri mai kasashe da yawa mai suna “Background Rates of Adverse Events for Vaccine Evaluation in Africa (BRAVE).” ATBUTH na daga cikin cibiyoyin kiwon lafiya huɗu a Najeriya da aka zaɓa don wannan aikin na tsawon shekaru uku (tare da yiwuwar ƙarin shekaru biyu don sa ido). Sauran su ne Cibiyar Kiwon Lafiya ta Tarayya (Owo) da Babban Asibitin Irrua da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Benin. Wannan shiri, wanda Gidauniyar Ƙasa da Ƙasa kan Cututtukan Masu Saurin Yaɗuwa a Najeriya (IFAIN) ke gudanarwa tare da haɗin gwiwar...
    Kungiyar Agaji ta Red Cross (ICRC) ta bayyana cewa yunwa na ƙara tsananta a Arewa maso Gabashin Nijeriya, musamman a jihohin Borno, Adamawa da Yobe. A cewar rahoton, rikicin da ya dauki shekaru 16 ya durƙusar da kasuwanci da hanyoyin samun aiki, wanda hakan ya tilastawa mutane dogaro da ƙananan gonaki don rayuwa. Mutum 16 sun mutu a haɗarin jirgin sama a Bangladesh Jihohin da za a samu ruwan sama da iska mai ƙarfi a sassan Nijeriya — NiMet ICRC ta bayyana cewa fiye da mutum miliyan 3.7, wadanda galibi manoma ne na fuskantar barazanar matsanancin rashin abinci a yankin da aka shafe shekaru ana rikici. Churi Ibrahim, wani tsohon manomi dan shekara 70 da ke ciyar da iyalinsa goma,...
    Hukumar kula da yanayi ta Nijeriya (NiMet) ta sanar da cewa a ’yan kwanakin nan za a samu ruwan sama da iska mai ƙarfi a wasu jihohi da ke sassa daban-daban na ƙasar. Hakan na kunshe cikin hasashen yanayi na kwana uku, daga Litinin 21 zuwa Laraba 23 ga Yulin 2025 da hukumar ta fitar. Ƙalubalen da ke tattare da sauya sunan jami’a An nada ’yar Najeriya a Kwamitin Nukiliya na Majalisar Dinkin Duniya NiMet ta shawarci al’umma da su yi taka-tsantsan kan yiwuwar samun ambaliya da kuma ɓarna da iska mai ƙarfi ke iya haddasawa. A cewar sanarwar da hukumar ta wallafa a shafin sada zumunta na X, jihohin Arewa da na Kudu da kuma yankin tsakiya, duk za...
    Ya ce PDP ce kaɗai ke da ƙarfin gina ƙasa. “Wannan gwamnati ce da ke cewa mutane su yi azumi alhali su suna cin abinci sannan suna jin daɗi. Babu ɗan Nijeriya mai kishin ƙasa ko wata jam’iyya mai jin zafin halin da mutane ke ciki da za ta goyi bayan Tinubu a 2027. Gwamnatinsa kasuwanci ne mara riba,” in ji Ologunagba. Kakakin PDP ya kuma nuna damuwa kan halin rashin tsaro, inda ya ambaci kisan gillar da aka yi wa mutane a Jihar Filato da kuma hari kan ɗan takarar PDP daga Anambra a Abuja, a matsayin alamu cewa rashin tsaro ya zama ruwan dare. Ya ce ƙarfin PDP yana hannun talakawa, ba sai da manyan ’yan siyasa ba....
      Manoma a Jihar Kaduna sun bayyana gamsuwarsu da yadda iri na TELA Hybrid Maize daga kamfanin EcoBasic Seeds ke samar da amfanin gona ba tare da amfani da maganin kwari ba.   Sun bayyana hakan ne a Jaji, Jihar Kaduna, lokacin da ‘yan jarida suka kai ziyara gonakin gwaji da kamfanin EcoBasic Seeds ya kafa.   Wani daga cikin manoman, Mallam Sabitu Abdullahi, ya bayyana Irin Masara na TELA Hybrid a matsayin masara mai ban mamaki, yana cewa tana bada amfanin gona mai yawa da kuma girbi cikin kwanaki 70 kacal.   “Idan duka manoman Najeriya suka rungumi wannan iri, zai taimaka wajen tabbatar da wadatar abinci a kasa,” inji shi.   Ya ce ya shafe shekaru uku yana...
    Gwamnatin Libya ta tasa keya daruruwan baƙin haure ‘yan ƙasar Sudan 700 zuwa ƙasarsu da yaƙi ya ɗaiɗaita, A cewar mahukuntan, waɗannan mutanen sun yi hijira zuwa Libya ne domin gujewa yaƙi da talauci, inda suke neman hanyar tsallakawa zuwa Turai. A cewar huƙumar kula da baƙin haure, an kori mutane 700 daga Libya da aka kama a tsakiya da kudu maso gabashin ƙasar, inda aka tura su zuwa Sudan a ranar Juma’ar da ta gabata ta ƙasa. Bayanin ya nuna cewa wasu daga cikin waɗanda aka korar na ɗauke da cututtuka masu yaɗuwa kamar su hepatitis da cuta mai karya garkuwar jiki, wasu kuma an tura su ne saboda laifuffuka ko kuma dalilan tsaro. Korar ta zo ne a...
    Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniya, Hajiya Amina Mohammed, ta yaba wa Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, bisa kokarinsa wajen inganta ci gaban zamantakewar al’umma da kuma tallafawa aiwatar da Muradun Cigaba mai Dorewa (SDGs). Hajiya Amina Mohammed ta kai ziyara Jihar Kano ne domin yin ta’aziyya ga gwamnati da al’ummar jihar bisa rasuwar fitattun dattawan nan  biyu, wato Alhaji Aminu Alhassan Dantata da tsohon Shugaban Kasa Muhammadu Buhari. A yayin ziyarar tata, Mataimakiyar Shugaban Majalisar Dinkin Duniyar ta nuna gamsuwa da wasu daga cikin shirye-shiryen Gwamna Yusuf na cigaban al’umma, musamman wadanda suka yi daidai da muradun ci gaban duniya. Daga cikin wadannan shirye-shirye akwai sanya fitilu masu amfani da hasken rana a titunan Kano, kafa cibiyar kula...
    Jami’in harkar shari’ar kasa da kasa ya bayyana cewa: Harin da aka kai wa Iran babban laifi ne kuma jarrabawa ce ta tarihi ga kwamitin sulhu Mataimakin ministan harkokin wajen kasar Iran kan harkokin shari’a da kasa da kasa, Kazem Gharibabadi, ya ce: Harin da aka kai wa Iran babban laifi ne, kuma jarrabawa ce ta tarihi ga kwamitin sulhun Majalisar Dinkin Duniya. A yayin wani taron manema labarai da ya yi da wakilan kasashe mambobin Majalisar Dinkin Duniya fiye da 110 a birnin New York na kasar Amurka a jiya Litinin, Gharibabadi ya bayyana ma’auni na wuce gona da iri da gwamnatin yahudawan sahayoniyya da Amurka suka dauka kan yankin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kuma sakamakonsa ga zaman...
    Kwamandan rundunar hadin gwiwar hedikwatar tsaron saman Iran ya jaddada cewa: Duk wani sabon kuskure da ‘yan sahayoniyya suka aikata zai haifar da mummunan sakamako Kwamandan rundunar hadin gwiwar hedikwatar tsaron saman Iran kuma  kwamandan bataliyar Khatam al-Anbiya (s.a.w) Birgediya Janar Alireza Sabahi Fard, ya jaddada cewa: Duk wani sabon kuskure da yahudawan sahayoniyya za su sake yi, zai haifar da mummunan sakamako. Birgediya Janar Seyyed Majid Mousavi, kwamandan rundunar sararin samaniyar Iran na dakarun kare juyin juya halin Musulunci ta Iran ya ziyarci hedikwatar hadakar tsaron sojojin saman na Khatam al-Anbiya, inda ya tattauna da Birgediya Janar Sabahi Fard, kan sakamakon arangamar da sojoji suka yi a baya-bayan nan da kuma hanyoyin inganta hadin kan tsaro. A zaman taron,...
    Jami’in kungiyar Hamas ya bayyana cewa: Kamen da hukumar Falasdinawa ta yi wa ‘yan gwagwarmaya a yankin Gabar Yammacin Kogin Jordan yana nuna goyon baya ne ga ‘yan mamayar Isrta’ila Jami’in kungiyar Hamas Abdel Rahman Shadid ya bayyana cewa: Kamen da jami’an tsaron Hukumar Falasdinawa suka yi na wani gungun ‘yan gwagwarmaya a Nablus da Jenin, da kwace makamansu, da kuma ci gaba da fatattakar ‘yan gwagwarmaya a duk fadin yankin gabar yammacin kogin Jordan, yana nuni da ci gaba da goyon bayan gwamnatin mamayar Isra’ila ce da murkushe al’ummar Falastinu. A cewar cibiyar yada labaran Falasdinu, Shadid ya jaddada a cikin wata sanarwa da ya fitar cewa: Kamen da jami’an tsaron hukumar cin gashin kan Falasdinawa suka yi kan...
    Mataimakin shugaban kasar Iran na farko ya jaddada cewa; Ra’ayin gwamnati shi ne tattaunawa akan fagen yadda al’amura zasu karfafa Mataimakin shugaban kasar na farko na kasar Iran Mohammed Reza Aref ya bayyana cewa: Babu wani bambanci tsakanin diflomasiyya da fannin, inda ya ce har yanzu ra’ayin gwamnati shi ne tattaunawa kan hanyoyi kyautata gudanar da madafun iko. A yayin ganawarsa da malaman jami’ar Shariff ta fasahar kere-kere, Aref ya yaba da irin rawar da al’ummar Iran suka taka a yakin kwanaki 12 da yahudawan sahayoniyya da Amurka suka dorawa Iran, inda ya ce: Matsayin al’ummar Iran da kasancewarsu a fagen kare kasar ya kasance mai karfi wajen yakar makiya, saboda dabarun makiya shi ne cewa bayan harin da aka...
    Mamba a kwamitin tsaron kasar Iran ya bayyana cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran zata zama daya daga cikin manyan kasashen duniya Ala’uddin Boroujerdi mamba a kwamitin tsaron kasa da manufofin kasashen waje na majalisar shawarar Musulunci ya bayyana cewa: Kisan gillar da aka yi wa fitattun malamai irin su Shaheed Tehranji ba zai kawo cikas ga ci gaban ilimi na Iran ba, illa dai zai kare daliban da suka yi karatu karkashin tallafin wadannan malamai don ci gaba da tafarkinsu tare da rubanya hidimarsu. Boroujerdi ya yi ishara da ma’auni na Shaheed Tehranji, inda ya bayyana shi a matsayin fitaccen malami da ya yi karatu a makarantar Imam al-Khameini, kuma jagoran juyin juya halin Musulunci. Ya tabbatar da cewa al-Shahed...
    Ministan yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila yana alfahari da rusa Gaza da tarwatsa mazauna yankin! Isra’ila Katz, ministan yakin gwamnatin mamayar Isra’ila, ya wallafa wani hoto da ya nuna yadda aka lalata garin Beit Hanoun a arewacin zirin Gaza, yana mai alfahari da yadda aka rusa gine-ginen garin”. Kuma ta hanyar dandalin “X”, Kats yayi sharhi game da hoton, yana cewa: “Bayan Rafah da Beit Hanoun.. babu mafaka ga ‘yan ta’adda. Hoton da aka dauka ta sama yana nuni da dimbin baraguzan gine-gine da kango da kuma irin barnar da aka yi wa daukacin garin da ke daura da layin da aka shimfida da tarwatsewar kango da ragowar gine-ginen da suka ruguje a hoton inda ke nuni irin girman bala’in...
    Sanata Yemi Adaramodu, mai magana da yawun Majalisar Dattawa, ya ce matsalar tsaro a Najeriya na raguwa, kuma tattalin arziƙi ya fara farfaɗowa. Ya yaba da ƙoƙarin da sojoji ke yi wajen yaƙi da ’yan bindiga da ’yan ta’adda. Haɗakar ’yan hamayya alheri ce ga siyasar Nijeriya — Gbajabiamila WFP ya dakatar da tallafin abinci a Yammaci da Tsakiyar Afirka “Sojoji suna ƙoƙari saboda muna ba su isasshen kuɗi don siyan makamai da kula da jin daɗinsu. Yanzu matsalar ’yan bindiga ta ragu a wasu jihohi, kuma ana magance ta.” Ya ƙara da cewa satar mutane ta ragu: “A da, mutane ba sa iya bacci saboda tsoro. Amma yanzu abubuwa sun ɗan gyaru. Sai dai waɗanda za su sa siyasa...
     Shugaban kasar Korea ta Arewa ya bayyana goyon bayan sag a kasar Rasha a yakin da take fafatawa da kasar Ukraine. Kafafen yada labarai na Korea ta Arewa sun bayyana cewa Kim Jong Un ya fadawa ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Layrov, a cikin xiyarar kwanaki 3 da ya kai ziyara kasar. Kasar korea ta Areawa dai ta sha taimakawa kasar Rasha da sojoji da kuma makamai ma yakin da take fafatawa da kasar Ukraine fiye da shekaru uku da suka gabata. Kim ya hadu Lavrov ne a kan iyakokin kasashen biyu na ruwa da ke Wonsan . Kasashen bi yu sun tattauna karin taimakawa juna a bangaren tsaro.  KCNA ya bayyanan cewa shuwagabannin biyu sun tattauna al-amura da...
    Benyamin Natanyahu firai ministan HKI ya amince da cewa gwamnatinsa ta kashe masana fasahar Nukliya na kasar Iran da dama, don haka kasar ci gaba a wannan bangaren. Tashar talabijin ta Presstv a nan Tehran ta nakalto Natanyahu yana fadar haka a lokacinda yake hira da tashar talabijin ta Amurka mai sun a FOX NEWS. Wannan ikrarin dai ya fidda shakka da ake da shi ne cewa gwamnatin HKI ce take kashe masana fasahar Nikliyar kasar kuma wannan furucin ya zama shaida a kansa a duk lokacinda al-amarin ya zaman a shari’a. Har’ila yau furucin ya tabbatar da cewa HKI tana zagon kasa wa JMI wacce shirin makamashin nukliyar ta, ta zaman lafiya ce karkashin kula na hukumar IAEA. Banda...
    A wani bidiyo da ya karaɗe kafafen sada zumunta, Usman Dako ya bayyana yadda aka kori iyalinsa, aka rusa gidansu, aka kuma tsorata matarsa da ‘ya’yansa. Ya ce gida ne da aka ware wa mahaifinsa tun zamanin marigayi Sarki Ado Bayero, amma yanzu an rusa shi ba tare da haƙƙi ba. Dako ya dage da cewa zai ci gaba da nuna biyayya ga Aminu Ado Bayero, duk kuwa da korar da aka yi masa. Har yanzu dai Sarki Sanusi bai ce uffan ba game da lamarin, kuma ba a samu wani bayani daga majalisar Sarakunan ba. Ana sa ran za a ci gaba da sauraron shari’ar nan ba da jimawa ba. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun...
    Kakakin ma’aikatar sharia a nan Iran ya bayyana cewa shi bai da wata masaniya dangeneda cewa HKI ta kai hare-hare kan gidan yarin Evin na Tehran ne don kashe ma’aikatanta da aka kama aka kuma tsare a gidan yarin. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto kakakin na ma’aikatar sharia yana fadar haka a nan Tehran ya kuma kara da cewa, a cikin yakin kwanaki 12 da ya gabata jami’an tsaron kasar Iran sun kama ma’aikatan leken asirin na HKI da dama a lokacin, suna aikawa Haramtacciyar kasar Rahotanni a cikin yakin. A lokacinda aka tambayeshi kan cewa kun gano cewa hare-haren ranar 22 ga watan Yunin da ya gabata a cikin yakin kwanaki 12, HKI ta kai...
    Mai Alfarma Sarkin Musulmi Muhammad Sa’ad Abubakar ya bayyana hukumar kula da shige da fice ta Najeriya a matsayin matakin farko na tsaro wajen kare rayuka da dukiyoyi a kasar.   Mai Alfarma Sarkin Musulmi ya bayyana hakan ne a lokacin da ya karbi bakuncin daliban jami’ar Immigration da ma’aikatan kwalejin Sokoto a ziyarar ban girma a fadarsa.   Ya yi kira da a samar da jami’an shige-da-fice don duba bakin haure da ke barazana ga zamantakewa da ci gaban tattalin arzikin kasar.   Ya kara da cewa galibin ‘yan kungiyoyin ta’addanci irin su Lakurawas da Boko Haram ba ’yan Najeriya ba ne.   Jagoran ya bayyana cewa, hukumar shige da fice na taka muhimmiyar rawa wajen tabbatar da tsaron...
     Shugaban kasar Korea ta Arewa ya bayyana goyon bayan sag a kasar Rasha a yakin da take fafatawa da kasar Ukraine. Kafafen yada labarai na Korea ta Arewa sun bayyana cewa Kim Jong Un ya fadawa ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Layrov, a cikin xiyarar kwanaki 3 da ya kai ziyara kasar. Kasar korea ta Areawa dai ta sha taimakawa kasar Rasha da sojoji da kuma makamai ma yakin da take fafatawa da kasar Ukraine fiye da shekaru uku da suka gabata. Kim ya hadu Lavrov ne a kan iyakokin kasashen biyu na ruwa da ke Wonsan . Kasashen bi yu sun tattauna karin taimakawa juna a bangaren tsaro.  KCNA ya bayyanan cewa shuwagabannin biyu sun tattauna al-amura da...
    A cikin wannan mako dai an yi ta murna da farin ciki a fadin jihar Kano inda dubban ‘yan fansho suka fara karbar kudaden fansho da garatuti da aka dade ba su yi ba.     Kudaden da aka fitar na ‘yan fansho na jihar Kano, sun kasance wani babban ci gaba a kokarin da gwamnan ke ci gaba da yi na biyan bashin zunzurutun kudi har naira biliyan 48 na kudaden alawus-alawus da kuma na mutuwa da ya gada daga gwamnatocin baya.   ‘Yan fansho da suka karbi kudadensu sun nuna matukar godiya ga Gwamna Yusuf kan abin da mutane da yawa ke kira a matsayin hanyar rayuwa bayan shekaru da aka yi watsi da su.   Daga cikin...
    Shirin Samar da Abinci na Majalisar Ɗinkin Duniya (WFP) ya sanar da dakatar da bayar da tallafin abinci a ƙasashen Yammaci da Tsakiyar Afirka da ke fama da rikici. Hakan dai na zuwa ne a sakamakon rage tallafin da Amurka ke bayarwa na kuɗi ƙarƙashin Hukumar USAID, wanda hakan ke kawo cikas ga ayyukan wannan ƙungiyar. Za a sa zare tsakanin Amurka da Turai kan harajin kasuwanci An sanya dokar hana fita a Adamawa Duk da cewa lokaci ya bambanta daga ƙasa zuwa ƙasa, ana hasashen kayan abinci za su isa zuwa kusan watan Satumba a mafi yawan ƙasashen da abin ya shafa, wanda hakan zai bar miliyoyin mutane masu rauni cikin halin rashin tallafin gaggawa, a cewar WFP. “Muna...
    ‘Rundunar ‘yan sandan jihar Kwara ta ce ta kama wasu da ake zargi da aikata laifuka, ta kwato bindigogi, da kuma kama sama da Naira miliyan 11 da ake zargin kudin fansa ne a cikin wannan lokaci.   Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Adekimi Ojo ne ya bayyana haka yayin da yake zantawa da manema labarai a Ilorin.   A cewarsa jami’an ‘yan sanda tare da hadin gwiwar kungiyoyin tsaro na cikin gida sun cafke wani kasurgumin mai garkuwa da mutane mai suna Idirisu Sariki a Okuta, karamar hukumar Baruten.   Ojo ya ce ana kyautata zaton Sariki na da alaka da sace-sacen mutane da dama a yankunan kan iyaka a jihar   Ya bayyana cewa, a yayin samamen jami’an tsaro...
    Dan majalisa mai wakiltar mazabar Katagun ta tarayya a jihar Bauchi Alh. Awwalu Abdu Gwalabe, ya bayar da hujjar cewa tattalin arzikin Najeriya na da karfin da zai iya dorewar karin jihohi 12.   Ya bayyana haka ne ga manema labarai a wajen taron jin ra’ayin jama’a kan sake duba kundin tsarin mulkin 1999 a Arewa maso Gabas a Gombe   Alh. Awwalu Gwalabe, ya ci gaba da cewa, idan har Gwamnatin Tarayya za ta iya kashe Naira tiriliyan 17 wajen gina titin lagos-calabar kadai, hakan na nuni da cewa tattalin arzikin zai iya dorewar samar da karin jihohi.   Ya ce sama da shekaru arba’in ne al’ummar shiyyar katagun a jihar Bauchi suke ta tada jijiyoyin wuya na ganin...
    Shugaba Trump da abokansa sun ce sun gano cewa ana tafka almundahana da zamba a hukumar. Rahoton na zuwa ne yayin da gomman shugabannin duniya ke taro a Birnin Sabeilla na kasar Sifaniya cikin makon nan domin tattauna batun katse tallafin, wanda ya fi kowane bayar da agaji a duniya. Bayan nazarin bayanan alkaluman tallafin hukumar a kasashe 133 a duniya, binciken ya kiyasta cewa tallafin USAID ya rage mutuwar mutum miliyan 91 a kasashe masu tasowa tsakanin 2001 zuwa 2021. Sun kuma yi amfani da wani kiyasi wajen hasashen yadda rage tallafin da kashi 83% adadin da gwamnatin Amurka ta sanar a farkon wannan shekara na iya shafar adadin masu mutuwa. Rahoton ya ce katse tallafin zai haifar da...
    3. Girman Lambar Yabo da Za a Baiwa Zakaran Gasar Kungiyar da ta lashe kofin za ta samu fam miliyan 97 daga hukumar FIFA. Hakanan, za ta sanya tambarin kofin na tsawon shekaru 4, sabanin shekara 1 da ake yi a baya. 4. Muhimmancin Wasan ga Duka Kungiyoyin Ga PSG, wannan kofi na iya zama jaddawalin nasarar su bayan barin Kylian Mbappé. Ga Chelsea kuma, nasarar na iya maido da su sahun gaba a turai da duniya gaba daya. 5. Kallon Duniya na Kan Wasan Wasan zai jawo hankalin masu sha’awar kwallon kafa a duniya, musamman ganin yadda kowanne bangare ke dauke da fitattun ‘yan wasa da kocin da ke kokarin kafa tarihi. Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna...
    An haifi Peter Rufa’i a ranar 24 ga watan Agusta, 1963, a Oshodi, Legas, a wani gidan sarautar gargajiya, Mahaifinsa shi ne sarkin kabilar Idimu a Jihar Legas, duk da hasashen da ake yi na cewa zai yi gadon sarautar gidansu, Rufa’i ya yi watsi da sarautar don ci gaba da fuskantar abin da yake sha’awa wato kwallon kafa. 2. Ya yi Wasa A Manyan Kungiyoyin Kwallon Kafa A Kasashen Turai Rufa’i ya fara sana’ar kwallon kafa a kungiyoyin gida Nijeriya kamar Storeery Stores da Femo Scorpions kafin ya tsallaka zuwa kasar waje, ya taka leda a kungiyoyi a kasar Benin (Dragons de l’Ouémé), Belgium (Lokeren, Beberen), Netherlands (Go Ahead Eagles), Portugal (Farense, Gil Bicente), da Spain (Hércules, Deportibo La...
    Dakarun rundunar “Shahid Izzuddin al-kassam’ da kuma ” Sarayal Kuds” sun sanar da kai jerin hare-hare akan sansanonin ‘yan sahayoniya a yankuna mabanbanta na Gaza. A bayanin da dakarun ” Kassam” su ka fitar sun bayyana hare-hare masu yawa da su ka kai wa ‘yan mamaya, da su ka hada da tarwatsa motocin buldoza biyu samfurin D9 a unguwar Zaituna a cikin birnin Gaza. Haka nan kuma sun kai wani harin a ranar 6 ga watan Yuli wanda su ka rusa tankar yaki ta “Mirkava” ta hanyar amfani da wata nakiya mai tsananin fashewa. Bugu da kari , Kassam ta ce a ranar 9 ga watan Yuli din ta kai wani harin akan sansanin da kwamandoji masu bayar da umarnin...
    Gwamnatin Adamawa ta ayyana dokar ta baci ta hana zirga-zirgar mutane na tsawon sa’o’i 24 a Karamar Hukumar Lamurde da ke Kudancin jihar. Bayanai sun ce wannan lamarin na zuwa ne bayan samun rahotannin mutuwar kimanin mutane hudu a wani sabon rikici na kabilanci da ya auku a yankin. Tinubu ya dawo Najeriya bayan ziyarar aiki a Saint Lucia da Brazil Sanatan Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC DW ta ruwaito kakakin rundunar ’yan sandan jihar, SP Suleiman Nguroje yana ba da shaidar matakan da suke dauka domin dakile rikicin. Kazalika Kwamishin ’yan sandan jihar, Dankombo Morris ya kaddamar da kwamitin bincike kan musabbabin afkuwar lamarin. Kana Kwamishinan ya ba da umarnin jibge ’yan sandan kwantar da tarzoma a yankin...
    Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya dawo gida Najeriya bayan kwashe makonni biyu, inda ya ziyarci ƙasashen Saint Lucia da Brazil. Mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga, ne ya sanar da hakan a shafinsa na X. Sanatan Abuja ta sauya sheƙa zuwa ADC Abin da ya faru tsakani na da DSS bayan kama ni — Ɗan Bello Shugaba Tinubu ya bar Najeriya ne a ranar 28 ga watan Yuni, 2025 don ziyarar aiki a waɗannan ƙasashe biyu. Da farko ya je Saint Lucia domin ƙarfafa dangantaka tsakanin Najeriya da ƙasashen yankin Caribbean, da kuma ƙara haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen kudancin duniya. A ranar 4 ga watan Yuli, Tinubu ya tashi daga Saint Lucia zuwa Brazil, inda ya halarci taron BRICS...
      Ko za ka iya fada wa masu karatu dan takaitaccen tarihinka? An haife ni a Unguwar Adakawa cikin birnin Kano, na yi makarantar firamare a Adakawa, daga nan kuma na tafi zuwa makarantar sakandire (Gwammaja One), bayan na sauke Alkur’ani, daga baya na tafi sai na wuce zuwa ‘School of Health Technology’ ta Kano. Bayan nan, sai kuma na tsunduma harkokin kasuwanci da siyasa, kazalika ina da mata biyu da kuma ‘ya’ya goma a halin yanzu.   Kamar wane irin kasuwanci kake yi? Ina harkar takalma ‘yan Kofar Wambai, wadda ita ce sana’ar dana fara koya, sannan kuma ita ce sana’ar da dangina suke yi.   Me ya ja hankalinka har ka tsunduma cikin masana’antar Kannywood? Tun ina yaro...
    Har ila yau a wannan rana, Wang Yi ya gana da ministan harkokin wajen Sri Lanka Vijitha Herath a birnin na Kuala Lumpur. Bugu da kari, kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Sin ya mai da martani a yau Asabar game da furucin da Philippines ta yi kan sanarwa game da bikin cika shekaru 9 da fitar da hukuncin takkadamar “Philippines v. China”, inda ya bayyana cewa, “hukuncin” ya saba wa ka’idojin dokokin kasa da kasa da kuma yarjejeniyar MDD kan batun teku, kuma ya sabawa ainihin gaskiyar dake tattare da batun tekun kudancin kasar Sin, haka kuma ba shi da wata daraja ko amfani.(Safiyah Ma) Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin...