Shugaban Putin Na Rasha Ya Bada Sanarwan Tsagaita Wuta Da Ukraine Na Bangaren Guda kuma na sa’o’ii 72 ko kwanaki 3, daga 8-10 na watan Mayu mai zuwa.

Jaridar Daily Trust ta Najeriya nakalto jakadan kasar Rasha a Abuja yana fadar haka a wani taro baje kolin hotinan yaki Rasah da Nazi a dai dai lokacinda kasar take cikar shekaru 80 da samun nasara a kan sojojin Nazi a karshen yakin duniya na II a Abuja.

Andrey Podelyshev yace idan kasar Ukraine ta zami da tsagaita wuta a cikin wadannan kwanaki ba laifi, amma kuma idan sojojinta sun kai wani hari a kan rasha ta zata rama da hare-hare masu tsanani.

Shugaban Volodimir Zelesky dai tuni ya yi watsi da tsagaita wutar ya kura kara da cewa Rasha tana son ta ja hankalin duniya ne da wannan tsagaita wuta, don amfanin kanta a yakin da suke fafatawa. A halin yanzu dai an dai kwanaki kimani 1,159 aka fafatawa tsakanin kasashen biyu.

উৎস: HausaTv

এছাড়াও পড়ুন:

2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — Okonkwo

Tsohon jigo a Jam’iyyar LP, Kenneth Okonkwo, ya ce dole ADC ta tsayar da ɗan Arewa takara idan tana son ta kayar da Shugaba Bola Tinubu a zaɓen 2027.

A cikin wata hira da aka yi da shi a gidan talabijin na Channels, Okonkwo, ya ce idan ADC ta tsayar da ɗan Kudu takara, Tinubu zai sake lashe zaɓe ba tare da wata tangarɗa ba.

Biza: UAE ta ƙaƙaba wa ’yan Najeriya sabbin takunkumai Yara miliyan 5.4 na fama da karancin abinci a jihohin arewa 9 – Red Cross

Ya ce dole ne ’yan adawa su yi aiki da hikima da dabaru idan suna son yin nasara.

“Shirina a wannan karon shi ne zan goyi bayan ɗan Arewa a 2027,” in ji shi.

Ya ce wannan ɗan takarar dole ne ya kasance mutum mai farin jini a Arewa.

Ya ambaci sunan Atiku Abubakar da Aminu Tambuwal a matsayin misali na mutanen da ke da farin jini a yankin.

“Mutumin dole ne ya cancanta. Idan ya taɓa riƙe muƙamin shugaban ƙasa ko kusa da hakan, to hakan zai ƙara wa tafiyar armashi.

“Idan ya haɗu da ɗan Kudu a matsayin mataimaki, to hakan zai taimaka sosai,” in ji Okonkwo.

Ya bayyana shugabancin Tinubu a matsayin “mara amfani,” inda ya ce ƙarfin ɗan Arewa ne kawai zai iya kawowa takarar Tinubu cikas.

Ya yi gargaɗin cewa tsayar da ɗan Kudu takara a jam’iyyar zai sa Tinubu ya lashe zaben cikin sauƙi.

“Idan ka tsayar da ɗan Kudu domin yin takara da Tinubu, wanda shi ma ɗan Kudu ne, to zai lashe zaɓe cikin sauƙi.”

“Idan aka kawo ɗan Kudu Maso Gabas, ko da ya yi nasara, za su murɗe zaɓen a hannunsa ,” in ji shi.

Ya bayyana cewa a siyasar Najeriya, sai ka samu goyon bayan “tsari” kafin ka iya kare nasararka.

Ya ce yankin Kudu Maso Yamma bai taɓa fafatawa da shugaban ƙasa mai ci ba saboda sun san dabarar siyasa.

Ya sake jaddada cewa Peter Obi ne ya lashe zaɓen 2023, amma an ƙwace masa.

Ya ce hakan na iya sake faruwa idan ba a shirya da kyau ba.

“Amma idan ɗan Arewa ne ya ci, babu wanda zai murɗe masa ko a ce ya sauka domin ba su fito daga yankin ɗaya da Tinubu ba,” in ji shi.

Okonkwo, ya fice daga jam’iyyar LP a watan Yulin 2024 saboda rikice-rikicen cikin gida da jam’iyyar ke fama da shi.

Yanzu da ’yan adawa suka haɗu ƙarƙashin jam’iyyar ADC, yana fatan za su iya ƙirƙiro tafiya mai ƙarfi domin tukarar zaɓen 2027.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Qalibof: Asarorin HKI A Yakin Kwanaki 12 Yafi Abinda Ta Bayyana
  • Shugaban Kasar Iran Yace Huldar kasar Iran Da IAEA Zai Ci Gaba Ne Idan Ta Daina Fuska Biyu
  • Ministan Tsaron Iran Ya Bayyana cewa: Martanin Da Iran Ta Mayar Ne Ya Sanya Isra’ila Ta Amince Da Tsagaita Wuta
  • Shugaban Majalisar Shawarar Musulunci  ya Bayyana Yadda Iran Da Mayar Da Martani Mai Gauni Kan Isra’ila
  • Manazaecin Kasar Amurka Ya Ce; Isra’ila Ta Sha Kashi A  Yakinta Da Jamhuriyar Musulunci Ta Iran
  • Rizai: Mun Harbo Jirage Kanana Da Manya 80 Na ‘Yan Sahayoniya
  • 2027: Idan ADC na son lashe zaɓe dole ta bai wa ɗan Arewa takara — Okonkwo
  • Gwamnatin Mamayar Isra’ila Ta Amince Iran ta Kai Hare-Hare Kan cibiyoyin Sojojinta Guda Biyar
  • Amurka Tana Fatan HKI da Hamas Su Tsaida Budewa Juna Wuta Na Kwanaki 60 A Karshen Wannan makon
  • TCN Ta Wayar Da Kan Al’ummomin Kaduna Kan Illar Lalata Kayan Wuta Da Gini Karkashen Babbar Wayar Wuta