Leadership News Hausa:
2025-06-15@06:39:33 GMT

Ƴan Fashi Sun Sace Fasinjoji 7, Ƴansanda Sun Ceto 2 A Kwara

Published: 27th, April 2025 GMT

Ƴan Fashi Sun Sace Fasinjoji 7, Ƴansanda Sun Ceto 2 A Kwara

Ƴan fashi sun sace fasinjoji guda bakwai a cikin motocin haya biyu a ƙauyen Eleyin da ke cikin ƙaramar hukumar Isin a Jihar Kwara.

A cewar rahoton LEADERSHIP, lamarin ya faru ne da misalin ƙarfe 5:45 na yamma a ranar Juma’ar da ta gabata, lokacin da wasu ƴan fashi su biyar suka toshe hanya, suka tsayar da motoci biyu, sannan suka tilasta ɗaukar dukkanin fasinjojin zuwa wani wuri da ba a sani ba.

Uwargidan Shugaban Kasar Sin Ta Tattauna Da Takwararta Ta Kasar Kenya Ra’ayin Matasa Kan Kungiyar ‘Yan Ta’adda Mai Suna  Lakurawa Da Ta Fito A Kebbi

Wasu majiyoyi sun bayyana cewa, daga cikin fasinjojin motar ɗaya, akwai shugaban sashin shari’a na ƙaramar hukumar Oke Ero, Barr. Elizabeth Arinde, da daraktan gudanar da ma’aikata na wannan ƙaramar hukumar, Alh. Musbau Amuda.

Kakakin Ƴansanda na Jihar Kwara, Toun Ejire-Adeyemi, ta tabbatar da faruwar lamarin, inda ta bayyana cewa an sami ceto fasinjoji biyu, Ganiyu Ajayi da Kolawole Adeyemi. Ta kuma ƙara da cewa, har yanzu ana ƙoƙarin ceto sauran fasinjojin guda biyar da kuma kama ƴan fashin.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Kwara

এছাড়াও পড়ুন:

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya

Zuzzurfar tattaunawa da ta wakana tsakanin tsagin Sin da na Amurka a birnin Landan, ta sa masu bayyana ra’ayoyin jin karfin gwiwa game da makomar shawarwarin tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka.

Kuri’un jin ra’ayin jama’a na kafar CGTN ta kasar Sin, sun nuna yadda masu bayyana ra’ayoyi suka amince cewa, shawarwari sun nuna kyakkyawan fata game da aiwatar da matsayar da shugabannin kasashen biyu suka cimma yayin tattaunawar da suka yi ta wayar tarho, tare da sassauta sabani a batutuwan tattalin arziki da cinikayya tsakanin sassan biyu.

Yayin kuri’un jin ra’ayoyin, masu bayyana mahanga sun goyi bayan matsayar Sin, inda kaso 87.1 bisa dari suka amince cewa ba wani batu na wa ya yi nasara, ko wanda ya yi hasara a batun tattalin arziki da cinikayya tsakanin sassan biyu.

Kaso 85.2 bisa dari na ganin karfafa hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, ba kawai zai kyautata ci gabansu ba ne, har ma zai samar da wani muhimmin tabbaci ga daidaito, da bunkasar tsarin gudanar da ayyukan masana’antu na duniya. Yayin da kaso 87.1 bisa dari ke ganin managarcin tsari, da daidaiton ci gaban alakar tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Amurka, ba kadai zai amfani al’ummunsu ba ne, har ma zai samar da muhimmiyar gudummawa ga bunkasar tattalin arzikin duniya. (Mai fassara: Saminu Alhassan)

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
  • Taron Koli Na Sin Da Kasashen Yankin Tsakiyar Asiya Karo Na Biyu Zai Ingiza Manufar Kara Dunkulewar Sassan Yankin
  • Abin da muke da shi a Najeriya ba cikakkiyar dimokuraɗiyya ba ce — Fayemi
  • Ƴansanda Sun Kama Shahararren Ɗan Damfarar Yanar Gizo A Bauchi
  • Ƴansanda Sun Cafke Masu Garkuwa Da Mutane 2, Sun Ceto Mutane 11 A Delta Da Katsina
  • Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN: An Yi Kira Ga Amurka Da Ta Cimma Daidaito Da Sin Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya
  • Babu wanda ya tsira daga hatsarin Jirgin Air India mai dauke da fasinjoji 242
  •  Iran Za Ta Kara Yawan Sanadarin Urani’um Da Take Tacewa A Wuri Na Sirri
  • EFCC Ta Kama Mutane 11 Kan Zargi Aikata Damfara A Intanet A Kaduna
  • Basaraken Da Aka Sace A Kogi Ya Kuɓuta Bayan Shafe Kwanaki 27 A Hannun ‘Yan Bindiga