Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi rangadi a rundunar arewaci ta rundunar sojin ’yantar da al’ummar Sinawa wato PLA, gabanin Bikin Bazara.

Xi Jinping wanda shi ne sakatare janar na kwamitin kolin JKS kuma shugaban hukumar koli mai kula da ayyukan soji (CMC), a madadin kwamitin kolin da hukumar CMC, ya mika gaisuwar sabuwar shekara ga dukkan jami’an rundunar soji ta PLA, da sojoji ’yan sanda, da fararen hula dake aiki a rundunar soja, da mambobin kungiyoyin sa kai da ma jam’an tsaro da aka kebe domin bukatar gaggawa.

A bana, Bikin Bazara na sabuwar shekarar al’ummar Sinawa ya fado ne a ranar 29 ga watan nan na Janairu. (Fa’iza Mustapha)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Dalilin da ya sa muka ziyarci Obasanjo — Turaki

Shugaban jam’iyyar PDP) na ƙasa, Taminu Turaki, ya bayyana cewa sun kai wa tsohon Shugaban Ƙasa Olusegun Obasanjo, ziyara domin neman shawarwari da goyon baya gabanin zaɓen 2027.

Turaki, wanda ya zama sabon shugaban jam’iyyar PDP kwanan nan, ya ziyarci Obasanjo a garin Abeokuta, da ke Jihar Ogun, tare da wasu manyan shugabannin jam’iyyar, ciki har da Shugaban Kwamitin Amintattu, Sanata Adolphus Wabara, da wasu tsofaffin gwamnoni.

EFCC na ƙoƙarin daƙile muradin Malami na yin takarar gwamna — ADC Sojoji sun daƙile harin ’yan ta’adda a Borno

Ya ce ziyarar wani ɓangare ne na gabatar da sabon shugabancin jam’iyyar ga tsohon shugaban ƙasar.

“Mun zo ne domin gode wa tsohon shugaban ƙasa kan gudunmawarsa ga dimokuraɗiyya, tare da neman shawarwari da jagoranci yayin da muke shirin tunkarar zaɓen 2027,” in ji Turaki.

“Daga shawarwari da ƙwarin gwiwar da muka samu a yau, muna da tabbacin cewa PDP ta shirya tsaf domin komawa kan mulki a shekarar 2027,” in ji shi.

Turaki, ya ce jam’iyyar PDP yanzu ta samu haɗin kai kuma ta shirya tsaf domin tunkarar manyan zaɓuka masu zuwa, ciki har da zaɓen gwamna a jihohin Ekiti da Osun.

Shi ma Shugaban PDP na Jihar Ogun, Abayomi Tella, ya ce ziyarar ta ƙara wa mambobin jam’iyyar ƙwarin gwiwa.

Ya ƙara da cewa ’yan Najeriya sun gaji da rashin kyakkyawan shugabanci kuma suna buƙatar sauyi a zaɓen 2027.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalilin da ya sa muka ziyarci Obasanjo — Turaki
  • Sin Ta Gudanar Da Taron Tunawa Da Kisan Kiyashin Nanjing
  • Bankin Ajiya na Jihar Jigawa Ya Karamar Shugaban Karamar Hukumar Birnin Kudu
  • Majalisar Jigawa Ta Bukaci Kananan Hukumomi Su Gabatar da Kasafin Kudinsu a Zangon Farko na Sabuwar Shekara
  • Samarwa Sojoji Manyan Makamai Ne Mafita – Shugaban Ƙaramar Hukumar Bukuyum
  • ’Yan sanda sun ba da tabbacin isasshen tsaro a zaɓen ƙananan hukumomin Borno
  • Tinubu Ya Yaba Wa Jami’an Tsaro Kan Ceto Dalibai 100 Da Aka Sace A Neja
  • Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa
  • Ƴan Bindigar Daji: Jihohin Arewa 7 Sun Kaddamar Da Rundunar Fatattakar Su
  • Ma’aikatar Mata da Walwalar Jama’a ta Jihar Jigawa ta Kare Kasafin Kudinta a Gaban Majalisa