Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi rangadi a rundunar arewaci ta rundunar sojin ’yantar da al’ummar Sinawa wato PLA, gabanin Bikin Bazara.

Xi Jinping wanda shi ne sakatare janar na kwamitin kolin JKS kuma shugaban hukumar koli mai kula da ayyukan soji (CMC), a madadin kwamitin kolin da hukumar CMC, ya mika gaisuwar sabuwar shekara ga dukkan jami’an rundunar soji ta PLA, da sojoji ’yan sanda, da fararen hula dake aiki a rundunar soja, da mambobin kungiyoyin sa kai da ma jam’an tsaro da aka kebe domin bukatar gaggawa.

A bana, Bikin Bazara na sabuwar shekarar al’ummar Sinawa ya fado ne a ranar 29 ga watan nan na Janairu. (Fa’iza Mustapha)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

EFCC ta ƙwato fiye da naira biliyan 500 a shekara biyu — Shetima

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya bayyana cewa, Hukumar EFCC mai yaƙi da masu yi wa tattalin arziki ta’annati ta samu nasarar tara dukiyar da ta haura naira biliyan 500 a tsawon shekaru biyu na gwamnatinsu.

Shettima, wanda ya wakilci Shugaba Bola Tinubu, ya bayyana haka ne a yayin wani taron bita da ƙara wa juna sani na alƙalai da Hukumar EFCC tare da haɗin gwiwar Hukumar Shari’a ta Najeriya (NJC) suka shirya a birnin Abuja.

Red Cross ta kafa cibiyoyin rage haɗurran bala’o’i a makarantun Gombe NLC ta sa zare da gwamnati kan yajin aikin ASUU

Shettima ya buƙaci alƙalai da sauran ma’aikatan ɓangaren shari’a da su ƙara ƙaimi tare da yin aiki bisa gaskiya da adalci, yana mai gargaɗin cewa ana fara samun matsala ne a ƙasa da zarar masu riƙe da amanar hukunci suka fara tauye haƙƙin mai haƙƙi.

Mataimakin shugaban ƙasar ya ce gwamnatinsu ba ta tsoma baki a harkokin shari’a, yana mai cewa “mun ba ɓangaren shari’a da hukumomin yaƙi da cin hanci damar gudanar da ayyukansu ba tare da katsalandan ba,” in ji shi.

Da yake bayyana irin nasarorin da aka samu a fannin yaƙi da cin hanci da rashawa, Shettima ya ce EFCC ta samu nasarar ƙwato fiye da naira biliyan 500 a cikin shekara biyu da suka gabata.

“A cikin shekara biyu na wannan gwamnatin, EFCC ta samu nasarar gurfanar da sama da mutum 7,000 a gaban kotu, sannan ta ƙwato dukiyar da ta haura naira biliyan 500,” in ji Shettima.

Ya ƙara da cewa, kuɗaɗen da aka ƙwato ana amfani da su ne a shirye-shiryen tabbatar da walwalar al’umma, ciki har da shirin bayar da bashi ga ɗalibai da sauran manufofin tallafa wa jama’a.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Jami’an tsaro sun kama Sowore saboda shirya zanga-zanga
  • Yawan Hada-hadar Kudaden Kasashen Waje Na Kasar Sin A Farkon Rabu’i Na Uku Na Bana Ya Zarce Dala Triliyan 11
  • Rundunar ‘Yan Sanda A Jihar Zamfara Ta Gargadi Direbobi Game Da Rufe Lambar Mota
  • Iran Ta Godewa Rasha Game Da Goyon Bayan Da Ta Bata A Kwamitin Sulhu Na M D D
  • Gwamnatin Borno rufe makarantun jihar saboda rigakafin ƙyanda da Polio
  • Jami’an Kasashen Afrika Na Koyon Dabarar Yaki Da Talauci Ta Sin A Jihar Ningxia
  • EFCC ta ƙwato fiye da naira biliyan 500 a shekara biyu — Shetima
  • Gina Kasar Sin Ta Dijital Na Kara Gaba Zuwa Sabon Matakin Amfani Da Basira
  • Sakataren Majalisar Kolin Tsaron Kasar Iran Ya Karbi Bakwancin Takwaransa Na Iraki
  • Morocco Ta Lashe Kofin Duniya Na Ƴan Ƙasa Da Shekara 20 Karo Na Farko A Tarihinta