Shugaban kasar Sin Xi Jinping, ya yi rangadi a rundunar arewaci ta rundunar sojin ’yantar da al’ummar Sinawa wato PLA, gabanin Bikin Bazara.

Xi Jinping wanda shi ne sakatare janar na kwamitin kolin JKS kuma shugaban hukumar koli mai kula da ayyukan soji (CMC), a madadin kwamitin kolin da hukumar CMC, ya mika gaisuwar sabuwar shekara ga dukkan jami’an rundunar soji ta PLA, da sojoji ’yan sanda, da fararen hula dake aiki a rundunar soja, da mambobin kungiyoyin sa kai da ma jam’an tsaro da aka kebe domin bukatar gaggawa.

A bana, Bikin Bazara na sabuwar shekarar al’ummar Sinawa ya fado ne a ranar 29 ga watan nan na Janairu. (Fa’iza Mustapha)

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9

Gwamnatin Tarayya ta amince a kafa karin sababbin jami’o’i masu zaman kansu guda guda tara a fadin Najeriya.

Ministan Ilimi, Dr Tunji Alausa ne ya sanar da hakan ranar Laraba lokacin da yake jawabi ga ’yan jaridar Fadar Shugaban Kasa jim kadan da kammala taron Majalisar Zartarwa ta Kasa.

Bello Turji bai miƙa wuya ba har yanzu — DHQ Amurka za ta sayar wa Najeriya makaman N530bn don yaƙi da ta’addanci

Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ne ya jagoranci taron wanda aka gudanar a Abuja.

A cewar ministan, sababbin jami’o’in da aka ba lasisin sun hada da Jami’ar Tazkiyah da ke Kaduna, Jami’ar Leadership da ke Abuja, Jami’ar Jimoh Babalola da ke Kwara da Jami’ar Bridget da ke Mbaise a jihar Imo.

Sauran jami’o’in sun hada da jami’ar Greenland da ke Jigawa da jami’ar JEFAP da ke Neja da jami’ar Azione Verde da ke Imo, sai jami’ar karatu daga gida ta Unique da ke jihar Legas da kuma takwararta mai suna American Open University da ke jihar Ogun.

Alausa ya kuma ce Tinubu ya gaji bukatu guda 551 na kafa makarantun gaba da sakandire masu zaman kansu, wadanda ya ce dole sai an cika tsauraran sharuda kafin a ba su lasisin.

Sai dai ya ce rashin cika wadannan sharuda ne ya rage adadin zuwa guda 79 kacal, inda daga ciki aka amince da guda tara a ranar ta Laraba.

Ya ce da yawa daga cikin jami’o’in da aka ba lasisin sun dade suna jira, wasu ma sun shafe sama da shekaru shida suna kan layi.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama mai babur ɗauke da ƙoƙunan kan mutane a Ogun
  • Gwamnati ta amince a kafa sabbin jami’o’i masu zaman kansu guda 9
  • Gwamna Sule Ya Ziyarci Gidan Yarin Keffi Bayan Tserewar Fursunoni 16
  • Majalisar Dokokin Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukumar Rano Na Tsawon Watanni Uku
  • Majalisar Kano ta dakatar da ciyaman kan zargin karkatar da taki
  • Tinubu Ya Nada Hukumar Gudanarwa Ta NCC Da Sauran su
  • Kasar Iraki Ta Ce: Yarjejeniyar Da Ta Kulla Da Iran Zai Amfani Dukkan Kasashen Yankin
  • An kama basarake kan zargin yi wa ’yar shekara 12 fyaɗe a Gombe
  • Majalisar Kano Ta Karbi Kudirin Karamin Kasafin Kudi Na Shekarar 2025
  • Tinubu Ya Sake Nada Dankaka A Matsayin Shugaban Hukumar Kula Da Da’ar Ma’aikata Ta Kasa