Ƙungiyoyin da suka yi shuhura a Firimiyar Ingila
Published: 27th, April 2025 GMT
Wannan wata mahawara ce da aka daɗe ana yi kan wace kungiya ce ta fi gawurta a Birtaniya? Shin wace kungiya ce ta fi lashe kofuna?
Wacce ce ta fi tara kudin shiga ko kuma ta fi yawan mabiya a shafukan sada zumunta?
Wace kungiya ce ta fi filin wasa mai girma? Wacce ce ta fi daraja a gasar Firimiya?
’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno Abubuwan da suka faru yayin jana’izar Fafaroma FrancisSai dai wannan muhawara da wuya a kawo ƙarshenta, saboda dole za a ci gaba da samun ra’ayoyi mabambanta, kuma ba dole ba ne a samu gamsasshiyar amsa.
An tafka muhawara kan abubuwa da dama, amma a ƙarshe sai muka yi nazari tare da daddale guda 10 da za mu zayyano.
a) Wannan kiyasi ne, kuma akwai ra’ayoyi mabambanta
b) Ba muna nufin cewa wannan hukunci kamar yankan wuka ba ne.
Manyan kungiyoyi 10 a Birtaniya
Manchester United Liverpool Arsenal Manchester City Celtic Chelsea Tottenham Hotspur Rangers Aston Villa Newcastle UnitedDomin samar da gamsasshshen bayani, mun yi nazarin kungiyoyin da suke kan gaba.
Kungiyar da ta fi lashe manyan kofi
Game da kungiyar da ta fi lashe manyan kofuna, a bisa al’ada ana kallon kungiyar da ta lashe kofuna a matsayin gawurtacciya.
Idan ana maganar lashe manyan kofuna, babu kungiyar da ta kai Celtic da Rangers.
Liverpool ce gaba a Ingila wajen lashe kofuna, sai Manchester United ke biye mata – kuma akwai alama Liverpool za ta kamo Manchester United wajen lashe gasar Premier guda 20.
Haka kuma ta fi kowace kungiya lashe gasannin Turai, sannan Arsenal ce ta fi lashe gasar FA.
Yadda Manchester City ke jan zarenta a ’yan shekarun nan, ciki har da lashe gasar premier shida a cikin shekara bakwai da lashe kofuna uku a kaka daya, wato kakar 2022-23.
Kungiyar da ta fi da yawan mabiya a kafofin sadarwa
Wasu masu tunanin mazan jiya ba za su damu da batun mabiya a kafofin sadarwa ba.
Amma suna da rawar da za su taka wajen gane kungiyar da ta fi girma ba a Ingila ba kadai, har da duniya baki daya.
Manchester United ce ta fi yawan masu mabiya a kafofin sadarwa a jimilla.
Sai dai akwai wasu kungiyoyi da suka fi mabiya a daidaikun kafofin sadarwa.
Manchester City ce ta fi karancin mabiya a kafofin sadarwa idan aka kwatanta da kungiyoyin da take makwabtaka da su, amma ta yi fintikau TikTok.
Amma kuma Tottenham ce shida a jimilla, amma kuma ta fi kowacce a TikTok.
Kungiyoyin da ake kira “manya shida” ne suka fi yawan mabiya, amma lashe gasar premier da Leicester City ta yi a kakar 2015-15 ta kara mata mabiya a kafofin sadarwa, inda ta zo ta bakwai.
Kungiyar da ta fi samun kudaden shiga
Shin batu ne ake yi na kudi? Idan kudin ake tunani, to lallai Machester City ce za ta fara zuwa a rai.
A wasu alkaluma da binciken Deloitte Money League ta fitar, ya bayyana cewa, Manchester City ce ta fi samun kudin shiga a kakar 2023-24 a Ingila da fam miliyan 708, kuma ta biyu a duniya, inda take biye da Real Madrid.
Kungiyoyin gasar premier guda tara ne suke cikin kungiyoyi 20, sannan da wasu karin biyar a cikin guda 30, saboda Brighton ta kara matsowa bayan ta fafata gasar kofin Europa a karon farko.
Kungiyar da filin wasanta ya fi girma
Idan kuma babbar kungiya na nufin mafi girman filin wasa, to lallai Manchester United ce a gaba.
Wembley ne fili mafi girma mai daukar mutum 90,000, amma Old Trafford ya fi girma a cikin filayen wasannin kungiyoyi, sannan kuma kungiyar ta sanar da shirinta na fadada filin ya zarce Wembley – inda za ta kashe fam biliyan biyu domin samar da fili mai cin mutum 100,000.
Kungiyar da ta fi karewa a matakai masu daraja a
A harkar tamaula, dadewa ana yi yana da muhimmanci. Wannan ne abin da Machester City ta ce a shekara 10 da suka gabata.
Ta ce gasar premier guda shida – har da lashe guda hudu a jere. Yanzu tana da kiyasin 1.7.
A tsakanin Liverpool da Manchester United da Arsenal da Tottenham da Chelsea babu takamaiman bambanci a matsakaici matsayi.
Da West Ham da Everton da Crystal Palace sun fi kwaarewa a tsakankanin tsakiyar teburi a shekara 10 da suka gabata.
Ba a saka Celtic da Rangers ba saboda ba sa buga Gasar Premier, amma Celtic ta kare a ta daya sau tara a shekara goma da suka gabata, sannan ta kare a ta biyu a 2020-21, ga Rangers, wadda ita kuma ta kasance ta biyu sau biyar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Firimiyar Ingila mabiya a kafofin sadarwa Kungiyar da ta fi kungiyar da ta fi gasar premier lashe gasar
এছাড়াও পড়ুন:
Ansarullah Ta Yi Allah Wadai Da Sabunta Takunkumin MDD Kan Yemen
Kungiyar Ansarullah a Yemen ta yi Allah wadai da sabunta takunkumin Majalisar Dinkin Duniya Kan kasar tare da dake tabbatar da goyon bayanta ga Falasdinu.
Kungiyar ta yi tir da matakin da Kwamitin Tsaron Majalisar Dinkin Duniya Ya Dauka Na sabunta takunkumin Kan Yemen na wata Shekara, ta kuma yi Allah Wadai da son zuciyar kasashen Yamma.
A cikin wani sako a shafin X, Mohammed al-Farah, wani babban jami’i a ofishin siyasa na Ansarullah, ya jaddada kudurin Sana’a na mayar da martani ga duk wanda ya yi yunkurin kai hari ga muradun al’ummar Yemen.
Ya kara da cewa ‘yan Yemen ba za su yi wata-wata ba don kare hakkokinsu, addininsu, da mutuncin kasa, ta kowace hanya da ta dace.
Al-Farah ya kuma kira shawarar da Majalisar Dinkin Duniya ta yanke da “mafi muni a karo na biyu,” yana mai kokawa da cewa hukumar ta yi biris da kisan kiyashin Falasdinawa a Gaza yayin da take goyon bayan gwamnatin Isra’ila a laifukan da take aikatawa da kuma yin watsi da da cin zarafin da take yi wa Yemen.
Babban jami’in ya bayyana Majalisar a matsayin wani dandali da ke biyan muradun Yamma da kuma kare muradun Amurka.
A wani bangare na jawabinsa, ya yaba wa Rasha da China saboda kin sabunta takunkumi kan Yemen, da kuma fahimtar hadarin manufofin Amurka wadda ke amfani da takunkumi ga kasashe masu iko.
Al-Farah ya kuma soki kasashen yamma da Amurka saboda goyon bayansu na soja, kudi, da siyasa ga Isra’ila, yana mai jayayya cewa takunkumin da aka sabunta wa Yemen don biyan bukatun ‘yan Sahayona ne da kuma hukunta al’ummar Yemen saboda juriyarsu, da kuma goyan bayan Gaza.”
Ya kuma sake jaddada goyon bayan Yemen ga Gaza da al’ummomin da ake zalunta a duk fadin yankin, tare da shan alwashin ci gaba da kalubalantar zalincin kasashen Yammacin duniya da Amurka a kan kasashe da al’ummomin yankin.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Afirka ta Kudu na Binciken shigar wasu ‘yan gudun hijirar Falasdinu 153 cikin kasar November 17, 2025 Najeriya ba za ta buga kofin duniya ba karo na biyu a jere November 17, 2025 DRC: An Kulla Yarjejeniyar Zaman Lafiya A Tsakanin Gwamnati Da Kungiyar M23 November 16, 2025 An Yi Kira A Bai Wa ‘Yan Hijira Saboda Sauyin Muhalli Kariya November 16, 2025 An Amince Da Sauye-sauye A Tsarin Mulkin Kasar Benin November 16, 2025 Isra’ila Ta Kai Wa Sojojin MDD Hari A Kasar Lebanon November 16, 2025 Makiya Sun Kulla Makirci kan Kasar Labanon Irin Wanda Suka Kulla Kan Siriya November 16, 2025 Kasar Afghanistan Na Kokarin Karkata Akalar Kasuwancinta Zuwa Iran November 16, 2025 Kanada Ta Tsare Tsohon Wakilin Majalisar Dinkin Duniya Mai Bincike Kan Laifukan Yakin Israila. November 16, 2025 Zarfi: HKI Ce Kawai Take Ayyana Nukiliya Ba Bisa Kaida Ba A Yammacin Asiya. November 16, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci