Aminiya:
2025-11-02@21:11:36 GMT

Ƙungiyoyin da suka yi shuhura a Firimiyar Ingila

Published: 27th, April 2025 GMT

Wannan wata mahawara ce da aka daɗe ana yi kan wace kungiya ce ta fi gawurta a Birtaniya? Shin wace kungiya ce ta fi lashe kofuna?

Wacce ce ta fi tara kudin shiga ko kuma ta fi yawan mabiya a shafukan sada zumunta?

Wace kungiya ce ta fi filin wasa mai girma? Wacce ce ta fi daraja a gasar Firimiya?

’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno Abubuwan da suka faru yayin jana’izar Fafaroma Francis

Sai dai wannan muhawara da wuya a kawo ƙarshenta, saboda dole za a ci gaba da samun ra’ayoyi mabambanta, kuma ba dole ba ne a samu gamsasshiyar amsa.

 An tafka muhawara kan abubuwa da dama, amma a ƙarshe sai muka yi nazari tare da daddale guda 10 da za mu zayyano.

a) Wannan kiyasi ne, kuma akwai ra’ayoyi mabambanta

b) Ba muna nufin cewa wannan hukunci kamar yankan wuka ba ne.

Manyan kungiyoyi 10 a Birtaniya

Manchester United Liverpool Arsenal Manchester City Celtic Chelsea Tottenham Hotspur Rangers Aston Villa Newcastle United

Domin samar da gamsasshshen bayani, mun yi nazarin kungiyoyin da suke kan gaba.

Kungiyar da ta fi lashe manyan kofi

Game da kungiyar da ta fi lashe manyan kofuna, a bisa al’ada ana kallon kungiyar da ta lashe kofuna a matsayin gawurtacciya.

Idan ana maganar lashe manyan kofuna, babu kungiyar da ta kai Celtic da Rangers.

Liverpool ce gaba a Ingila wajen lashe kofuna, sai Manchester United ke biye mata – kuma akwai alama Liverpool za ta kamo Manchester United wajen lashe gasar Premier guda 20.

Haka kuma ta fi kowace kungiya lashe gasannin Turai, sannan Arsenal ce ta fi lashe gasar FA.

Yadda Manchester City ke jan zarenta a ’yan shekarun nan, ciki har da lashe gasar premier shida a cikin shekara bakwai da lashe kofuna uku a kaka daya, wato kakar 2022-23.

Kungiyar da ta fi da yawan mabiya a kafofin sadarwa

Wasu masu tunanin mazan jiya ba za su damu da batun mabiya a kafofin sadarwa ba.

Amma suna da rawar da za su taka wajen gane kungiyar da ta fi girma ba a Ingila ba kadai, har da duniya baki daya.

Manchester United ce ta fi yawan masu mabiya a kafofin sadarwa a jimilla.

Sai dai akwai wasu kungiyoyi da suka fi mabiya a daidaikun kafofin sadarwa.

Manchester City ce ta fi karancin mabiya a kafofin sadarwa idan aka kwatanta da kungiyoyin da take makwabtaka da su, amma ta yi fintikau TikTok.

Amma kuma Tottenham ce shida a jimilla, amma kuma ta fi kowacce a TikTok.

Kungiyoyin da ake kira “manya shida” ne suka fi yawan mabiya, amma lashe gasar premier da Leicester City ta yi a kakar 2015-15 ta kara mata mabiya a kafofin sadarwa, inda ta zo ta bakwai.

Kungiyar da ta fi samun kudaden shiga

Shin batu ne ake yi na kudi? Idan kudin ake tunani, to lallai Machester City ce za ta fara zuwa a rai.

A wasu alkaluma da binciken Deloitte Money League ta fitar, ya bayyana cewa, Manchester City ce ta fi samun kudin shiga a kakar 2023-24 a Ingila da fam miliyan 708, kuma ta biyu a duniya, inda take biye da Real Madrid.

Kungiyoyin gasar premier guda tara ne suke cikin kungiyoyi 20, sannan da wasu karin biyar a cikin guda 30, saboda Brighton ta kara matsowa bayan ta fafata gasar kofin Europa a karon farko.

Kungiyar da filin wasanta ya fi girma

Idan kuma babbar kungiya na nufin mafi girman filin wasa, to lallai Manchester United ce a gaba.

Wembley ne fili mafi girma mai daukar mutum 90,000, amma Old Trafford ya fi girma a cikin filayen wasannin kungiyoyi, sannan kuma kungiyar ta sanar da shirinta na fadada filin ya zarce Wembley – inda za ta kashe fam biliyan biyu domin samar da fili mai cin mutum 100,000.

Kungiyar da ta fi karewa a matakai masu daraja a

A harkar tamaula, dadewa ana yi yana da muhimmanci. Wannan ne abin da Machester City ta ce a shekara 10 da suka gabata.

Ta ce gasar premier guda shida – har da lashe guda hudu a jere. Yanzu tana da kiyasin 1.7.

A tsakanin Liverpool da Manchester United da Arsenal da Tottenham da Chelsea babu takamaiman bambanci a matsakaici matsayi.

Da West Ham da Everton da Crystal Palace sun fi kwaarewa a tsakankanin tsakiyar teburi a shekara 10 da suka gabata.

Ba a saka Celtic da Rangers ba saboda ba sa buga Gasar Premier, amma Celtic ta kare a ta daya sau tara a shekara goma da suka gabata, sannan ta kare a ta biyu a 2020-21, ga Rangers, wadda ita kuma ta kasance ta biyu sau biyar.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Firimiyar Ingila mabiya a kafofin sadarwa Kungiyar da ta fi kungiyar da ta fi gasar premier lashe gasar

এছাড়াও পড়ুন:

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

“Haka kuma an kama wata mata mai shekaru 34 da ake zargi da hannu a lamarin, tare da wasu masu gidan marayu guda biyu da ke Abuja da Jihar Nasarawa, inda aka gano wasu yaran da ake kyautata zaton an yi safarar su. Wasu daga cikin gidajen marayun da aka gano ana amfani da su ne a matsayin cibiyoyin ajiye yara, inda ake jiran ‘kwace’ ko sayar da su da sunan daukar nauyin marayu.”

Ya ce, “An gano gidajen marayu guda hudu da ke Kaigini, Kubwa Edpressway Abuja; Masaka Area 1, Mararaba kusa da Abaca Road; da kuma Mararaba bayan Kasuwar Duniya suna da alaka da wannan kungiya, kuma ana ci gaba da bincike a kansu.”

Ya kara da cewa, daya daga cikin masu korafin ya bayyana cewa ya biya Naira miliyan 2.8 a matsayin kudin daukar yaro, sannan ya biya Naira 100,000 a matsayin kudin shawara ga daya daga cikin ‘yan kungiyar.

Sanarwar ta kara da cewa, “Wani mai korafi ya ce shi ma ya biya Naira miliyan 2.8 kudin daukar yaro da Naira 100,000 kudin shawara ga wani dan kungiyar.

“An canza sunayen yawancin yaran da aka ceto, lamarin da ya kara wahalar da bincike da gano asalinsu,” in ji sanarwar.

Darakta Janar ta NAPTIP, Binta Adamu Bello, ta bayyana damuwarta kan wannan lamari, inda ta ce safarar yara ta zama babbar matsala a kasa.

Ta hanyar Adekoye, DG din ta nuna damuwa game da yadda wasu gidajen marayu ke amfani da raunin jama’a wajen aiwatar da safarar yara.

Ta ce, “Abin takaici ne yadda wasu masu mugunta da ke da sunayen kwararru da matsayi a cikin al’umma, suke amfani da matsayin su wajen yaudarar mutanen da ke cikin mawuyacin hali, su yi safarar ‘ya’yansu, da dama daga cikinsu ma sun tsira ne daga halaka a lokacin rikice-rikicen al’umma ko na manoma da makiyaya, sannan a sayar da su ga iyaye masu neman haihuwa a matsayin daukar yaro ba tare da sahihin izinin iyayensu ba.

“Wannan abin ba za a yarda da shi ba, kuma wadanda aka kama kan wannan mugun aiki za su fuskanci hukuncin doka yadda ya kamata.

“’Ya’yanmu ba kayayyaki ba ne da za a ajiye su a gidajen marayu a sayar ga mai biyan mafi tsada. Wannan dole ya tsaya,” in ji ta.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Manyan Labarai Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa November 1, 2025 Manyan Labarai Jerin Gwarazan Taurarinmu November 1, 2025 Manyan Labarai Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari October 31, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • 2027: Yadda Gwamnoni Suka Yi Fatali Da Mataimakansu Wajen Zaɓo Waɗanda Za Su Gaje Su
  • Wadi Al-Salam: Maƙabartar Musulmai Mafi Girma A Duniya
  • Larijani: Iran Ba Ta Tsoron Gudanar Da Tattaunawa, Amma Ta Zama Mai Amfani
  • Isra’ila Ta Kashe Mutane 4 Tare Da Jikkata Wasu Guda 3 A Kudancin Labanon
  • Waye Zai Lashe Ƙyautar Gwarzon Ɗan Wasan Afrika Na 2025?
  • Samia Suluhu Hassan ta lashe zaben shugaban kasa a Tanzaniya
  • Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar
  • Zaɓen Tanzania: Shugaba Samia Suluhu Hassan ta yi tazarce
  • An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3
  • Real Madrid zata nemi diyyar Dala bilyan 4 daga UEFA