Ƙungiyoyin da suka yi shuhura a Firimiyar Ingila
Published: 27th, April 2025 GMT
Wannan wata mahawara ce da aka daɗe ana yi kan wace kungiya ce ta fi gawurta a Birtaniya? Shin wace kungiya ce ta fi lashe kofuna?
Wacce ce ta fi tara kudin shiga ko kuma ta fi yawan mabiya a shafukan sada zumunta?
Wace kungiya ce ta fi filin wasa mai girma? Wacce ce ta fi daraja a gasar Firimiya?
’Yan Boko Haram sun kashe mutum 12 a Borno Abubuwan da suka faru yayin jana’izar Fafaroma FrancisSai dai wannan muhawara da wuya a kawo ƙarshenta, saboda dole za a ci gaba da samun ra’ayoyi mabambanta, kuma ba dole ba ne a samu gamsasshiyar amsa.
An tafka muhawara kan abubuwa da dama, amma a ƙarshe sai muka yi nazari tare da daddale guda 10 da za mu zayyano.
a) Wannan kiyasi ne, kuma akwai ra’ayoyi mabambanta
b) Ba muna nufin cewa wannan hukunci kamar yankan wuka ba ne.
Manyan kungiyoyi 10 a Birtaniya
Manchester United Liverpool Arsenal Manchester City Celtic Chelsea Tottenham Hotspur Rangers Aston Villa Newcastle UnitedDomin samar da gamsasshshen bayani, mun yi nazarin kungiyoyin da suke kan gaba.
Kungiyar da ta fi lashe manyan kofi
Game da kungiyar da ta fi lashe manyan kofuna, a bisa al’ada ana kallon kungiyar da ta lashe kofuna a matsayin gawurtacciya.
Idan ana maganar lashe manyan kofuna, babu kungiyar da ta kai Celtic da Rangers.
Liverpool ce gaba a Ingila wajen lashe kofuna, sai Manchester United ke biye mata – kuma akwai alama Liverpool za ta kamo Manchester United wajen lashe gasar Premier guda 20.
Haka kuma ta fi kowace kungiya lashe gasannin Turai, sannan Arsenal ce ta fi lashe gasar FA.
Yadda Manchester City ke jan zarenta a ’yan shekarun nan, ciki har da lashe gasar premier shida a cikin shekara bakwai da lashe kofuna uku a kaka daya, wato kakar 2022-23.
Kungiyar da ta fi da yawan mabiya a kafofin sadarwa
Wasu masu tunanin mazan jiya ba za su damu da batun mabiya a kafofin sadarwa ba.
Amma suna da rawar da za su taka wajen gane kungiyar da ta fi girma ba a Ingila ba kadai, har da duniya baki daya.
Manchester United ce ta fi yawan masu mabiya a kafofin sadarwa a jimilla.
Sai dai akwai wasu kungiyoyi da suka fi mabiya a daidaikun kafofin sadarwa.
Manchester City ce ta fi karancin mabiya a kafofin sadarwa idan aka kwatanta da kungiyoyin da take makwabtaka da su, amma ta yi fintikau TikTok.
Amma kuma Tottenham ce shida a jimilla, amma kuma ta fi kowacce a TikTok.
Kungiyoyin da ake kira “manya shida” ne suka fi yawan mabiya, amma lashe gasar premier da Leicester City ta yi a kakar 2015-15 ta kara mata mabiya a kafofin sadarwa, inda ta zo ta bakwai.
Kungiyar da ta fi samun kudaden shiga
Shin batu ne ake yi na kudi? Idan kudin ake tunani, to lallai Machester City ce za ta fara zuwa a rai.
A wasu alkaluma da binciken Deloitte Money League ta fitar, ya bayyana cewa, Manchester City ce ta fi samun kudin shiga a kakar 2023-24 a Ingila da fam miliyan 708, kuma ta biyu a duniya, inda take biye da Real Madrid.
Kungiyoyin gasar premier guda tara ne suke cikin kungiyoyi 20, sannan da wasu karin biyar a cikin guda 30, saboda Brighton ta kara matsowa bayan ta fafata gasar kofin Europa a karon farko.
Kungiyar da filin wasanta ya fi girma
Idan kuma babbar kungiya na nufin mafi girman filin wasa, to lallai Manchester United ce a gaba.
Wembley ne fili mafi girma mai daukar mutum 90,000, amma Old Trafford ya fi girma a cikin filayen wasannin kungiyoyi, sannan kuma kungiyar ta sanar da shirinta na fadada filin ya zarce Wembley – inda za ta kashe fam biliyan biyu domin samar da fili mai cin mutum 100,000.
Kungiyar da ta fi karewa a matakai masu daraja a
A harkar tamaula, dadewa ana yi yana da muhimmanci. Wannan ne abin da Machester City ta ce a shekara 10 da suka gabata.
Ta ce gasar premier guda shida – har da lashe guda hudu a jere. Yanzu tana da kiyasin 1.7.
A tsakanin Liverpool da Manchester United da Arsenal da Tottenham da Chelsea babu takamaiman bambanci a matsakaici matsayi.
Da West Ham da Everton da Crystal Palace sun fi kwaarewa a tsakankanin tsakiyar teburi a shekara 10 da suka gabata.
Ba a saka Celtic da Rangers ba saboda ba sa buga Gasar Premier, amma Celtic ta kare a ta daya sau tara a shekara goma da suka gabata, sannan ta kare a ta biyu a 2020-21, ga Rangers, wadda ita kuma ta kasance ta biyu sau biyar.
উৎস: Aminiya
কীওয়ার্ড: Firimiyar Ingila mabiya a kafofin sadarwa Kungiyar da ta fi kungiyar da ta fi gasar premier lashe gasar
এছাড়াও পড়ুন:
Riƙaƙƙun ’yan daba da dilolin ƙwaya 31 sun shiga hannu a Kano
Kwamitin Haɗin Gwiwa na Jihar Kano kan Tsaro da Gyaran Matasa, ya kama ’yan daba 31 a wani samame da ya gudana a unguwanni bakwai a jihar.
An kai samamen ne daga ranar 10 zuwa 14 ga watan Mayu, 2025 ƙarƙashin jagorancin Dokta Yusuf Ibrahim Kofar Mata.
Tsafta a gidan aure: Abubuwan da kowace mace ya kamata ta sani Jami’an tsaro sun daƙile harin Boko Haram sun kashe mayaƙa 5 a BornoUnguwannin da aka kai samamen sun haɗa da Ɗorayi, Ja’in, Sharada, Unguwar Dabai, Dukawa, Kabuga, Kofar Mata da sauransu, wuraren da suka yi ƙaurin suna wajen aikata laifuka.
Daga cikin waɗanda aka kama, mutum 25 ana zargin ’yan daba ne, yayin da shida ake zarginsu dallacin miyagun ƙwayoyi.
A cikin kayan da jami’an suka ƙwato akwai bindigogi na gargajiya guda huɗu, wuƙaƙe da adduna tara, sanduna uku, tabar wiwi da kuma ƙwayoyi irin su Exol guda 173 da wasu miyagun ƙwayoyi daban-daban.
Haka kuma, jami’an sun kama wasu riƙaƙƙun ’yan daba da suka daɗe suna addabar al’ummar Dorayi, ciki har da Dan Abba, Bola, Baka Kashi, Ramos, Abba Maciji da Abdul Baki.
“Dukkanin ’yan daban 25 da muka kama an gurfanar da su a gaban Kotun Majistare mai lamba 16 da ke kan titin Zungeru, kuma an tasa ƙeyarsu zuwa gidan gyaran hali.
“Sauran masu sayar da ƙwayoyi guda shida, ciki har da Rabi’u Hamza, an miƙa su ga hukumar NDLEA don ci gaba da bincike kafin a gurfanar da su a kotu,” in ji Dokta Kofar Mata.
Ya bayyana wannan samame a matsayin babban ci gaba wajen wanzar da zaman lafiya da tsaro a jihar.
Ya ce unguwanni kamar Dorayi sun sha fama da rikice-rikicen faɗan daba sama da shekaru 20.
Kama waɗannan ɓata-gari zai iya kawo ƙarshen wannan matsala.
Ya ƙara da cewa kwamitin ya ƙunshi jami’an tsaro da jami’an gwamnati domin haɗa kai wajen tsaftace birnin Kano da kuma taimaka wa matasan da suka ɓace su koma turbar gaskiya.
“Kwamitin Haɗin Gwiwa zai ci gaba da jajircewa domin ganin an samar da ingantaccen tsaro da kuma zaman lafiya ba tare da ta’ammali da miyagun ƙwayoyi ba a Kano,” in ji kwamitin.
Ga hotunan wasu daga cikin kayan da kwamitin ya ƙwato: