Aminiya:
2025-07-31@19:31:38 GMT

An kama mutum 2 ɗauke da ƙwayar tramadol ta N150m a Kano

Published: 25th, April 2025 GMT

Rundunar ’yan sandan Jihar Kano ta kama aƙalla mutane biyu da ake zargi da safarar miyagun ƙwayoyi, wanda suka hada da: Muntari Shu’aibu da Imrana Rabi’u.

A wata sanarwa da Kwamishinan ’yan sandan jihar, Ibrahim Bakori ya fitar a ranar Alhamis, ya bayyana cewa an samu waɗanda ake zargin ɗauke da ƙunshi guda shida na miyagun ƙwayoyin  Tramadol da aka ƙiyasta kuɗinsu ya haura Dala 92,000 (kimanin Naira miliyan 150m).

Mahaifi ya kashe ɗansa mai shekara 6 don yin tsafi a Gombe Gwamnan Kano ya kafa sabbin hukumomi 4

Bakori ya ce, “Rundunar ’yan sandan ta gudanar da wani samame ta hanyar fasaha da bayanan sirri, ta kama waɗanda ake zargin da wannan miyagun ƙwayoyin, biyo bayan wani rahoto da aka samu.”

Ya ƙara da cewa, kama wani ɓangare ne na ƙoƙarin da ake yi na magance musabbabin munanan laifuka a jihar.

Ya ci gaba da cewa, “aikin ya biyo bayan ƙoƙarin da hukumar ta yi na daƙile ayyukan ta’addanci, waɗanda a cewarsa, galibin safarar muggan ƙwayoyi ne na sha da fataucin miyagun ƙwayoyi a jihar.”

Kwamishinan ya kuma tabbatar da cewa an miƙa waɗanda ake zargin ga hukumar yaƙi da sha da fataucin miyagun ƙwayoyi ta ƙasa reshen Jihar Kano domin ci gaba da bincike da gurfanar da su gaban ƙuliya.

“Wannan ya yi daidai da tsarin Sufeto-Janar na ‘yan sanda na aikin ‘yan sanda da kuma ƙarfafa haɗin gwiwa tsakanin hukumomin tsaro a tsakanin ƙungiyoyin tsaro,” in ji shi.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Yan Sanda Tramadol miyagun ƙwayoyi

এছাড়াও পড়ুন:

 Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai

Dan majalisa mai suna muhammad Mirzai ya ce; Kasashen turai sun zaku, akan su sami bayanai akan girman asarar da aka yi wa cibiyoyin Nukiliyar Iran don haka ya zama wajibi Iran din ta yi amfani da siyasar barinsu a cikin duhu.

A yayin zaman da majalisar shawarar musulunci ta Iran ta yi a yau Talata, dan majalisar ya kuma yi bayani akan kallafaffen yakin kwanaki 12, ya yi ishara akan yadda HKI ta yi amfani da kirkirarriyar fasaha da kuma wasu hanyoyi na leken asiri,amma duk da haka ta ci kasa, saboda jagoranci mai cike da fasaha na jagora, da kuma yadda al’ummar kasar ta yi tsayin daka da goyon bayan tsarin musulunci.

Haka nan kuma ya ce; Daga cikin manufofin da HKI ta Shata cewa za ta cimmawa a yayin yakin, shi ne samar da sauyi a cikin wannan yankin, shi ya sa da dama daga cikin hukumomin kasashen larabawa su ka fahimci cewa raunana Iran yana nufin raunana kasashensu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Zargin Da Wasu ’Yan Siyasar Amurka Ke Yi Wa Sin Na Fitar Da Hajoji Fiye Da Kima Ya Sabawa Hujjoji Na Hakika
  • Mutum 9 sun rasu a hatsarin kwale-kwale a Jigawa
  • ‘Yan Sandan Niger Sun Hada ‘Yan’uwa Mutanen 35 Da Aka Ceto Da Iyalansu 
  • Za a kammala shimfiɗa layin dogo daga Kaduna zuwa Kano a 2026 — Gwamnatin Tarayya
  • Remi Tinubu ta bai wa waɗanda harin Benuwe ya shafa tallafin Naira biliyan ɗaya
  • Remi Tinubu ta ba da tallafin Naira biliyan ɗaya ga waɗanda harin Benuwe ya shafa
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai
  • ‘Yan Sanda A Kano Sun Kama Kasurgumin Dan Fashin Nan Barga Da Wasu Mutum 14
  • Wani mutum ya mutu yayin raba faɗar ma’aurata 
  • Ambaliyar Ruwa: Adadin Mutanen Da Suka Rasu Ya Ƙaru Zuwa 23 A Jihar Adamawa