Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Wajabcin Kawo Karshen Ayyukan Ta’addanci A Kasashen Yanki
Published: 27th, April 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Dole ne a kawar da ta’addanci ta hanyar hadin kan kasashen yanki
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan harin ta’addancin da aka kai a birnin Pahalgam na kasar Indiya, tare da nuna alhini da juyayinsa ga gwamnati da al’ummar kasar Indiya, yana mai jaddada bukatar hadin gwiwa tsakanin kasashen yankin domin yakar ta’addanci da kuma tsayawa tsayin daka kan wannan barazana ta bai daya.
Pezeshkian ya zanta ta wayar tarho a yammacin jiya Asabar da fira ministan kasar Indiya Narendra Modi, inda suka tattauna kan sabbin al’amuran da suke faruwa a yankin na Indiya, da kuma alakar da ke tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kasar Indiya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Indiya
এছাড়াও পড়ুন:
Shugabannin kasashen (ECOWAS) na taro a Abuja
Shugabannin kasashe mambobin kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka (ECOWAS) na taro a wannan Lahadi a Abuja, fadar mulkin Najeriya.
Taron, zai ba da damar yin bitar batutuwan da ke ci gaba dake zaman karfa kafa wa kungiyar a hanlin yanzu.
Juyin mulkin Guinea Bissau da yunkurin juyin mulkin soja a Benin, na daga cikin ajandar taron.
Shugaban kungiyar na wannan karo kana kuma shugaban kasar Saliyo Julius Maada Bio ya yi tir da juyin mulkin na baya bayan nan.
Batun janye sojoji kusan 200 na rundunar tsaro ta ECOWAS da aka tura Benin tun bayan yunkurin juyin mulkin a ranar 7 ga Disamba shi ma za’a tattauna a kansa.
Taron zai kuma duba halin da ake ciki a Guinea Bissau, zai kuma duba yiyuwar kakabawa kasar takunkumi bayan hambarar da Shugaba Umaro Sissoco Embalo a ranar 26 ga Nuwamba.
Kungiyoyin fararen hula da wasu kungiyoyi 17 na Yammacin Afirka suna kira ga kungiyar da ta fitar da sakamakon zaben shugaban kasa da na ‘yan majalisa na ranar 23 ga Nuwamba ba tare da bata lokaci ba.
Share
0 0 votes Article Rating Subscribe Login Notify of new follow-up comments new replies to my comments Label {} [+] Name* Email* Website Label {} [+] Name* Email* Website 0 Comments Oldest Newest Most Voted Inline Feedbacks View all comments Masu Alaka Mutum biyu sun mutu a harbin bindiga a Jami’ar Brown ta Amurka December 14, 2025 Kasashen AES zasu kafa bankin dogaro da kai December 14, 2025 Sheikh Na’im Kassim: Idan Duniya Baki Daya Za Ta Taru, Ba Wanda Zai Iya Kwace Makaman Hizbullah December 13, 2025 DRC: Kungiyar M23 Ta Kwace Iko Da Wani Gari Mai Muhimmanci December 13, 2025 Syria: Sojojin “Isra’ila” Sun Kutsa Cikin Yankin Qunaidhara December 13, 2025 Kalibaf: Iran Da Habasha Suna Bunkasa Alakokin Siyasa Da Tattalin Arziki December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 171 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 170 December 13, 2025 Kissoshin Rayuwa: Sirar Imam Al-Hassan(a) 169 December 13, 2025 Isra’ila Ta Kai Hari A Kudancin Labanon A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Tsagaita Bude Wuta December 13, 2025 Categories Afirka Dogayen fina-finai Duniya Gallery IRAN IRAN POLITICS IRAQ Mata MIDDLE EAST Musulunci