Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Wajabcin Kawo Karshen Ayyukan Ta’addanci A Kasashen Yanki
Published: 27th, April 2025 GMT
Shugaban kasar Iran ya bayyana cewa: Dole ne a kawar da ta’addanci ta hanyar hadin kan kasashen yanki
Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya yi Allah wadai da kakkausar murya kan harin ta’addancin da aka kai a birnin Pahalgam na kasar Indiya, tare da nuna alhini da juyayinsa ga gwamnati da al’ummar kasar Indiya, yana mai jaddada bukatar hadin gwiwa tsakanin kasashen yankin domin yakar ta’addanci da kuma tsayawa tsayin daka kan wannan barazana ta bai daya.
Pezeshkian ya zanta ta wayar tarho a yammacin jiya Asabar da fira ministan kasar Indiya Narendra Modi, inda suka tattauna kan sabbin al’amuran da suke faruwa a yankin na Indiya, da kuma alakar da ke tsakanin Jamhuriyar Musulunci ta Iran da kasar Indiya.
উৎস: HausaTv
কীওয়ার্ড: kasar Indiya
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu A Iran Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan ‘Yan Ta’adda Da Suka Kai Hari Kan Hubbaren Shah Cheragh
An zartar da hukuncin kisa a kan wasu mutane 3 da ake zargi da kai harin ta’addanci a hubbaren Shah Cheragh
Shugaban hukumar shari’a ta lardin Fars (a kudancin Iran) ya sanar da cewa: Kotun Musulunci a birnin Shiraz ta yanke hukunci kan wasu mutane 7 da ake tuhuma da hannu a harin ta’addancin da aka kai a hubbaren Shah Cheragh (Ahmad ibn Imam Musa al-Kazim, amincin Allah ya tabbata a gare shi).
Haka nan kuma yayin da yake ishara da hukuncin da aka yanke wa mutanen bakwai da suka kai harin ta’addanci a hubbaren Shahragh, Hujjat al-Islam Sayyid Sadrullah Raja’i Nasab ya ce: A cikin hare-haren ta’addancin da aka kai a hubbaren Shahragh, baya ga manyan wadanda suka kai harin da aka hukunta bisa ayyukansu; An kuma hukunta wasu mutane saboda goyon baya da kuma tarayya da suka wajen samar da makamai da alburusai. Sannan bisa taimakon matakan leken asirin da aka sanya a cikin ajandar mai bincike na musamman da jami’an tsaro bayan faruwan wadannan al’amura, an gano wadannan mutane, an kama su, kuma sannan an dakile shirinsu na ta’addanci.
Hukunce-hukuncen sun hada da hukuncin kisa ga wasu mutane uku da aka samu da laifin “taimakawa wajen yada barna a kan doron kasa,” kuma an bayyana wadanda ake tuhumar a matsayin “masu kitsa” ayyukan ta’addanci. An kuma yanke musu hukuncin daurin shekaru 25 a kan kowane wanda ake tuhuma bisa zargin “taimakawa wajen gudanar da barna.”
An yanke wa wani dan ISIS hukuncin daurin shekaru 15 a gidan yari, wani kuma shekaru 10 da kwana daya.