Hakimin Kafin Hausa, Dan Amar na Hadejia, Alhaji Aliyu Usman Ginsau, ya yaba wa Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, bisa aiwatar da jerin manyan ayyuka a fadin jihar cikin shekaru biyu da suka gabata.

Hakimin ya yi yabon ne yayin bikin kaddamar da wani littafi a garin Kafin Hausa.

A jawabinsa yayin taron, Gwamna Umar Namadi ya yi jinjina ga marubucin littafin bisa rubuta cikakken tarihi da zai amfani al’umma, musamman matasa masu tasowa.

Malam Umar Namadi ya kuma yi alkawarin umurtar ma’aikatar ilimi ta jihar da ta sayi kwafin littafin domin amfanin ɗalibai a makarantun gwamnati.

Gwamna Umar Namadi ya kuma sayi kwafi bakwai na littafin a madadin iyalinsa kan kudi naira miliyan daya, yayin da Ma’aikatar Kananan Hukumomi ta Jihar ta sayi kwafi kan kudi naira miliyan biyu, sannan Sanata mai wakiltar Jigawa Arewa Gabas ya sayi littafin kan kudi naira miliyan daya.

Sauran sun hada da Kananan Hukumomin da ke karkashin Masarautar Hadejia, inda kowanne ya bayar da gudummawar naira dubu dari biyu, Shugaban Karamar Hukumar Kafin Hausa ya bayar da naira dubu dari biyar, tare da wasu hukumomin gwamnati, da kungiyoyi masu zaman kansu da kuma mutane daban-daban.

An tara sama da naira miliyan bakwai a yayin kaddamar da littafin tarihin Hakimin Kafin Hausa, Dan Amar na Hadejia, Alhaji Aliyu Usman Ginsau, a garin Kafin Hausa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa naira miliyan Umar Namadi

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai a Neja

Gwamnonin Jihohin Arewa (NSGF) sun nuna damuwarsu kan sace malamai da ɗaliban makarantar St. Mary’s da ke Ƙaramar Hukumar Agwara, a Jihar Neja.

Sun ce wannan lamari babban hatsari ne ga rayuwar yara da makomar ilimi a yankin Arewa baki ɗaya.

DSS ta mayar da Nnamdi Kanu gidan yarin Sakkwato Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 

Shugaban ƙungiyar kuma Gwamnan Jihar Gombe, Muhammadu Inuwa Yahaya, ya ce wannan hari abin takaici ne wanda ba za a lamunta da shi ba.

Ya jaddada cewa makarantu wajibi ne su kasance wuraren karatu da tsaro, ba wuraren tashin hankali ba.

Gwamna Yahaya ya ce Arewa ba za ta lamunci koma baya ba wajen rage yawan yaran da ba sa zuwa makaranta.

Ya ce: “Arewa na fama da ƙalubalen ilimi kuma ba za mu bari miyagu su lalata ci gaban da ake samu ba.”

Ya bayyana damuwa kan yadda hare-hare ke ƙaruwa a makarantu yayin da gwamnatocin Arewa ke ƙoƙarin samar da ingantattun tsare-tsaren tsaro ga ɗalibai.

Ya ce ƙungiyar za ta ci gaba da aiki tare da hukumomin tsaro da al’umma don ƙarfafa tsaro a unguwanni da makarantu, da kuma tattara bayanai masu muhimmanci.

A madadin gwamnonin, Gwamna Yahaya ya miƙa ta’aziyyarsa ga iyalan waɗanda aka sace da Gwamnatin Jihar Neja.

Ƙungiyar ta buƙaci a ɗauki matakin gaggawa don ceto waɗanda aka sace cikin ƙoshin lafiya da kuma hana faruwar irin wannan lamari a nan gaba.

Haka kuma, ta yaba wa jami’an tsaro da ke aikin ceto ɗaliban da malamai, inda ya roƙe su da su ƙara himma, tare da roƙon jama’a su ba da haɗin kai don samun nasarar ceto waɗanda lamarin ya shafa.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Fiye da yara miliyan 400 na fama da talauci a duniya — UNICEF
  • Gwamna Namadi Ya Tabbatar da Yunkurin Kafa Cibiyar Tarayya Ta Uku a Jigawa
  • Gwamnonin Arewa sun yi Allah-wadai da sace ɗalibai a Neja
  • Sojoji sun bar makarantar Maga kafin ’yan bindiga su kai hari — Gwamna Kebbi 
  • ’Yan bindigar da suka sace masu ibada a cocin Kwara sun nemi a ba su N3bn kafin sakin su
  • ’Yan Bindiga Sun Nemi Miliyan 100 Kudin Fansa Kan Kowane Mutum Ɗaya da Suka Sace a Kwara
  • UNICEF Ta Jinjinawa Jihohin Kano, Katsina da Jigawa Bisa Inganta Rayuwar Kananan Yara
  • Jihar Jigawa Ta Amince da Naira Biliyan 3.5 a Matsayin Kudaden Tallafin UBEC 2025
  • Iyalan Waɗanda Aka Kashe Yayin Zanga-zangar Bangladesh Sun Yi Maraba Da hukuncin Kisan Tsohuwar Firaminstar
  • Gwamna Abba Kabir Zai Gabatar Da Kudirin Kafin 2026 Ga Majalisar Kano Ranar Laraba