Hakimin Kafin Hausa, Dan Amar na Hadejia, Alhaji Aliyu Usman Ginsau, ya yaba wa Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, bisa aiwatar da jerin manyan ayyuka a fadin jihar cikin shekaru biyu da suka gabata.

Hakimin ya yi yabon ne yayin bikin kaddamar da wani littafi a garin Kafin Hausa.

A jawabinsa yayin taron, Gwamna Umar Namadi ya yi jinjina ga marubucin littafin bisa rubuta cikakken tarihi da zai amfani al’umma, musamman matasa masu tasowa.

Malam Umar Namadi ya kuma yi alkawarin umurtar ma’aikatar ilimi ta jihar da ta sayi kwafin littafin domin amfanin ɗalibai a makarantun gwamnati.

Gwamna Umar Namadi ya kuma sayi kwafi bakwai na littafin a madadin iyalinsa kan kudi naira miliyan daya, yayin da Ma’aikatar Kananan Hukumomi ta Jihar ta sayi kwafi kan kudi naira miliyan biyu, sannan Sanata mai wakiltar Jigawa Arewa Gabas ya sayi littafin kan kudi naira miliyan daya.

Sauran sun hada da Kananan Hukumomin da ke karkashin Masarautar Hadejia, inda kowanne ya bayar da gudummawar naira dubu dari biyu, Shugaban Karamar Hukumar Kafin Hausa ya bayar da naira dubu dari biyar, tare da wasu hukumomin gwamnati, da kungiyoyi masu zaman kansu da kuma mutane daban-daban.

An tara sama da naira miliyan bakwai a yayin kaddamar da littafin tarihin Hakimin Kafin Hausa, Dan Amar na Hadejia, Alhaji Aliyu Usman Ginsau, a garin Kafin Hausa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa naira miliyan Umar Namadi

এছাড়াও পড়ুন:

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Sanarwar ta ce, wannan horo mai taken ‘Computer Appreciation Training’ an shirya shi ne ta Hukumar Fasaha da Sadarwa ta Zamfara (ZITDA), a matsayin babban taron ƙarawa juna sani ga manyan jami’an gwamnati.

 

A jawabinsa yayin buɗe shirin, Gwamna Lawal ya bayyana cewa wannan horo wata muhimmiyar hanya ce wajen cimma burin gwamnatinsa na ingantaccen aiki ta amfani da fasaha.

 

Ya ce, “Burin mu shi ne tabbatar da cewa kowane bangare na gwamnati yana aiki cikin tsari, inganci da sauri, kamar yadda fasaha ke bai wa duniya damar gudanar da aiki cikin sauƙi.

 

“Mun shiga wani zamani ne da fasaha ke sauya yadda ake gudanar da mulki – daga tsarin tsara manufofi, yanke shawara, zuwa yadda ake sadarwa da isar da ayyuka ga jama’a. A yau, sanin amfani da kwamfuta ba zaɓi ba ne, wajibi ne ga duk wanda ke aikin gwamnati.”

 

Gwamna Lawal ya ce, hukumar ZITDA ta ƙaddamar da muhimman shirye-shirye kamar Zamfara e-Governance Platform (e-GovConnect), tsarin Digital Literacy Framework, da kuma haɗin gwiwa da manyan kamfanonin fasaha na duniya don ƙarfafa ilimin fasaha a jihar.

 

Ya kuma buƙaci mahalarta da su ɗauki shirin da muhimmanci, yana mai cewa ilimin da za su samu a wajen zai taimaka wajen ƙara inganta aiki, gaskiya da ingantaccen hidima ga jama’a.

 

“Mutanenmu sun cancanci gwamnati mai wayewa kuma mai amsawa cikin gaggawa ga buƙatunsu. Wannan canjin kuwa, ‘yan uwa, yana farawa da mu. Bayan wannan shirin, za a gudanar da jarrabawa domin tantance abin da aka koya, wanda kuma zai zama wani bangare na kimanta aikin kowane jami’i,” in ji gwamnan.

ShareTweetSendShare MASU ALAKA Labarai Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe October 28, 2025 Manyan Labarai Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260 October 28, 2025 Labarai Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi October 28, 2025

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Karamar Hukumar Gwarzo Ta Karfafa Yaƙi Da Miyagun Kwayoyi Da Shan Magani Ba Bisa Ka’ida Ba
  • Kungiyar Rapid Support Forces Ta Sanar Da Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Al’umma A El Fasher
  • Kasar Czech Ta Hana Wa Wani Sojan HKI Shiga Kasar Bisa Gargadin  Faransa
  • Gwamnatin Tarayya Ta Saki Naira Biliyan 2.3 Ga ASUU
  • An kashe mutum 2 a rikicin limancin masallacin Juma’a a Taraba
  • Bayan Kwace Birnin Al-Fasher Kungiyar Rapid Support Forces Suna Ci Zarafin Al’Umma
  • Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal
  • Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260
  • Rikicin adawa da cin zaben Shugaba Paul Biya ya bazu a Kamaru
  • Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100