Hakimin Kafin Hausa Ya Jinjinawa Gwamna Namadi Bisa Ayyuka Cigaban Al’umma
Published: 27th, April 2025 GMT
Hakimin Kafin Hausa, Dan Amar na Hadejia, Alhaji Aliyu Usman Ginsau, ya yaba wa Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, bisa aiwatar da jerin manyan ayyuka a fadin jihar cikin shekaru biyu da suka gabata.
Hakimin ya yi yabon ne yayin bikin kaddamar da wani littafi a garin Kafin Hausa.
A jawabinsa yayin taron, Gwamna Umar Namadi ya yi jinjina ga marubucin littafin bisa rubuta cikakken tarihi da zai amfani al’umma, musamman matasa masu tasowa.
Malam Umar Namadi ya kuma yi alkawarin umurtar ma’aikatar ilimi ta jihar da ta sayi kwafin littafin domin amfanin ɗalibai a makarantun gwamnati.
Gwamna Umar Namadi ya kuma sayi kwafi bakwai na littafin a madadin iyalinsa kan kudi naira miliyan daya, yayin da Ma’aikatar Kananan Hukumomi ta Jihar ta sayi kwafi kan kudi naira miliyan biyu, sannan Sanata mai wakiltar Jigawa Arewa Gabas ya sayi littafin kan kudi naira miliyan daya.
Sauran sun hada da Kananan Hukumomin da ke karkashin Masarautar Hadejia, inda kowanne ya bayar da gudummawar naira dubu dari biyu, Shugaban Karamar Hukumar Kafin Hausa ya bayar da naira dubu dari biyar, tare da wasu hukumomin gwamnati, da kungiyoyi masu zaman kansu da kuma mutane daban-daban.
An tara sama da naira miliyan bakwai a yayin kaddamar da littafin tarihin Hakimin Kafin Hausa, Dan Amar na Hadejia, Alhaji Aliyu Usman Ginsau, a garin Kafin Hausa.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: Jigawa naira miliyan Umar Namadi
এছাড়াও পড়ুন:
Matan sojojin da suka mutu na neman agaji
Ƙungiyar Tsofaffin Sojoji ta Najeriya ta bukaci gwamnati da ta ɗauki matakai na gaggawa wajen inganta rayuwar mata zawarawan sojojin da suka mutu a bakin aiki tare da ba su goyon bayan da ya dace.
Sabon shugaban ƙungiyar a Jihar Bayelsa, Mista Baratuaipre Allison-Alamini, ne ya yi wannan kira jim kaɗan bayan rantsar da shi.
Ya yi alƙawarin ci gaba da ƙoƙari ganin cewa muryar zawarawan sojojin da suka rasu ta isa inda ya kamata, ta yadda za a inganta rayuwarsu da kuma tabbatar da samun tallafin da suka cancanta.
Allison-Alamini ya kuma sha alwashin ba da muhimmanci ga walwalar tsoffin sojoji a jihar, tare da gode wa mambobin ƙungiyar bisa yadda suka ba shi amanar shugabanci.
Wani mutum ya rasu a gidan karuwai bayan ziyartar ’yan mata ’Yan bindiga sun sace mata 5 a KanoZaben ya gudana ne ƙarƙashin kulawar Ma’aikatar Tsaro ta Tarayya, ƙarƙashin jagorancin Laftanar Kanar Bello Kaya, tare da wakili daga ofishin sakataren gwamnatin jihar.
A yayin zaben, Odon Alfred ya sake lashe mukamin mataimakin shugaban kungiyar ba tare da hamayya ba, yayin da Mista Amiekumo Angozi ya zama ma’ajin kungiyar.
Shugaban kwamitin zaɓe, Mista Aghomo Samson, ya bayyana zaɓen a matsayin mai cike da kwanciyar hankali, gaskiya da amana. Ya yaba wa mambobin ƙungiyar bisa halin natsuwa da suka nuna kafin, yayin, da bayan gudanar da zaben.
Ya ya buƙaci sabbin shugabannin da su jagoranci ƙungiyar cikin adalci ba tare da rikici ba, tare da hada kan dukkan matakan kungiyar a cikin dukkan al’amuransu.
Wakilin sakataren gwamnatin Jihar Bayelsa, Ogori Raymond, ya buƙaci sabbin shugabannin su gudanar da mulki mai inganci, gaskiya da gaskatawa, wanda zai ƙarfafa zumunci, hadin kai, adalci da daidaito a tsakanin mambobin kungiyar.
A nasa bangaren, wakilin shugaban kasa na majalisar ƙungiyar tsoffin sojoji ta Najeriya, Mista Toye Dele, ya sake tabbatar da ƙudirin Gwamnatin Tarayya na ci gaba da kula da walwalar tsoffin sojoji da kuma kiyaye gado da tarihi na rundunar sojojin Najeriya.