Hakimin Kafin Hausa, Dan Amar na Hadejia, Alhaji Aliyu Usman Ginsau, ya yaba wa Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, bisa aiwatar da jerin manyan ayyuka a fadin jihar cikin shekaru biyu da suka gabata.

Hakimin ya yi yabon ne yayin bikin kaddamar da wani littafi a garin Kafin Hausa.

A jawabinsa yayin taron, Gwamna Umar Namadi ya yi jinjina ga marubucin littafin bisa rubuta cikakken tarihi da zai amfani al’umma, musamman matasa masu tasowa.

Malam Umar Namadi ya kuma yi alkawarin umurtar ma’aikatar ilimi ta jihar da ta sayi kwafin littafin domin amfanin ɗalibai a makarantun gwamnati.

Gwamna Umar Namadi ya kuma sayi kwafi bakwai na littafin a madadin iyalinsa kan kudi naira miliyan daya, yayin da Ma’aikatar Kananan Hukumomi ta Jihar ta sayi kwafi kan kudi naira miliyan biyu, sannan Sanata mai wakiltar Jigawa Arewa Gabas ya sayi littafin kan kudi naira miliyan daya.

Sauran sun hada da Kananan Hukumomin da ke karkashin Masarautar Hadejia, inda kowanne ya bayar da gudummawar naira dubu dari biyu, Shugaban Karamar Hukumar Kafin Hausa ya bayar da naira dubu dari biyar, tare da wasu hukumomin gwamnati, da kungiyoyi masu zaman kansu da kuma mutane daban-daban.

An tara sama da naira miliyan bakwai a yayin kaddamar da littafin tarihin Hakimin Kafin Hausa, Dan Amar na Hadejia, Alhaji Aliyu Usman Ginsau, a garin Kafin Hausa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa naira miliyan Umar Namadi

এছাড়াও পড়ুন:

MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar

Shugaban Ƙungiyar Iyaye na Jami’ar MAAUN, Alhaji Mustapha Balarabe, ya ƙaryata rahotannin da ke cewa jami’ar ta yanke wasu kuɗi masu yawa domin yaye ɗalibai.

A wata sanarwa da ya fitar tare da sakataren ƙungiyar, Hajiya Habiba Sarki, ya ce koken da aka kai wa PCACC da kuma rahotannin da aka wallafa ba su da tushe.

Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a ’Yan sanda sun gano zinaren N23m bayan shekara 13 da ɓacewarsu a Borno

Ya bayyana zargin a matsayin yunƙurin ɓata wa jami’ar suna.

Ya ce MAAUN na daga cikin jami’o’in masu zaman kansu mafi sauƙin farashi a Kano, kuma tana ba da ingantaccen ilimi.

“MAAUN na ɗaya daga cikin jami’o’i masu zaman kansu masu sauƙin farashi a Kano, tana ba da ingantaccen ilimi tare da ƙayatattun gine-gine.

“Wasu jami’o’in a jihar suna cajin kuɗin makaranta ninki uku a kan na MAAUN, amma ba a jin kukan kowa game da su. Me ya sa sai MAAUN?

“Idan ɗalibi ya biya kuɗin makaranta na tsawon shekaru huɗu, me ya sa za a ga laifi idan aka nemi ya biya kuɗin yayewa a jami’a mai zaman kanta?

“Wannan ba wani sabon abu ba ne. Wannan batu gaba ɗaya na nuna wata maƙarƙashiya ce da ke nufin ɓata suna da barazana daga wanda ba a san ko waye ba da yake iƙirarin cewa yana kare muradun ɗalibai da iyaye,” in ji shi.

Ya kuma yi tambaya: “Me ya haɗa MAAUN da hukumar PCACC a kan wannan batu?”

A ƙarshe, ya shawarci wanda ya kafa jami’ar da ya ci gaba da jajircewa wajen samar da ilimi mai inganci.

A gefe guda kuma, ya yaba masa saboda ƙin ƙara kuɗin makaranta duk da halin matsin tattalin arziƙi da ya sa wasu jami’o’i ƙara ƙudinsu.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Sharhi:’HKI tana fama da karancin sojojin a dukkan rassan sojojin kasar’.
  •  Palasdinu: Sojojin “Isra’ila” 3 Su Ka Jikkata Sanadiyyar  Taka Su Da Mota
  • Gwamnatin Jihar Kaduna Ta Gabatar Da Kasafin Kudin 2026 Na Kimanin Triliyan Daya
  • MAAUN: Ƙungiyar iyaye ta musanta zargin ƙara ƙudin yaye ɗalibai a jami’ar
  • Sarkin Musulmi ya buƙaci gwamnonin Arewa suke saurarar ƙorafin jama’a
  • Hamas : Isra’ila na jinkirta aiwatar da mataki na biyu na yarjejeniyar tsagaita wuta
  • Zanga zanga Ta Barke A Isra’ila Yayin Da Natanyaho Ke Neman Afuwa Kan Batun Cin Hanci Da Rashawa
  • NAJERIYA A YAU: Halayen Da Ambasadoji Ya Kamata Su Mallaka Kafin Tura Su Wasu Kasashe
  • Jihar Jigawa Ta Mayar da Rarar Kudi Sama da Naira Miliyan 50 Ga Maniyyatan Aikin Hajjin 2026
  •  Sau 590 “Isra’ila” Ta Keta Tsagaiwa Wutar Yaki