Hakimin Kafin Hausa, Dan Amar na Hadejia, Alhaji Aliyu Usman Ginsau, ya yaba wa Gwamnan Jihar Jigawa, Umar Namadi, bisa aiwatar da jerin manyan ayyuka a fadin jihar cikin shekaru biyu da suka gabata.

Hakimin ya yi yabon ne yayin bikin kaddamar da wani littafi a garin Kafin Hausa.

A jawabinsa yayin taron, Gwamna Umar Namadi ya yi jinjina ga marubucin littafin bisa rubuta cikakken tarihi da zai amfani al’umma, musamman matasa masu tasowa.

Malam Umar Namadi ya kuma yi alkawarin umurtar ma’aikatar ilimi ta jihar da ta sayi kwafin littafin domin amfanin ɗalibai a makarantun gwamnati.

Gwamna Umar Namadi ya kuma sayi kwafi bakwai na littafin a madadin iyalinsa kan kudi naira miliyan daya, yayin da Ma’aikatar Kananan Hukumomi ta Jihar ta sayi kwafi kan kudi naira miliyan biyu, sannan Sanata mai wakiltar Jigawa Arewa Gabas ya sayi littafin kan kudi naira miliyan daya.

Sauran sun hada da Kananan Hukumomin da ke karkashin Masarautar Hadejia, inda kowanne ya bayar da gudummawar naira dubu dari biyu, Shugaban Karamar Hukumar Kafin Hausa ya bayar da naira dubu dari biyar, tare da wasu hukumomin gwamnati, da kungiyoyi masu zaman kansu da kuma mutane daban-daban.

An tara sama da naira miliyan bakwai a yayin kaddamar da littafin tarihin Hakimin Kafin Hausa, Dan Amar na Hadejia, Alhaji Aliyu Usman Ginsau, a garin Kafin Hausa.

 

Usman Muhammad Zaria 

 

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: Jigawa naira miliyan Umar Namadi

এছাড়াও পড়ুন:

Yadda aka yi bikin naɗa Rarara sarkin wakar ƙasar Hausa a Daura

Sarkin Daura, Mai Martaba Alhaji Faruk Umar Faruk, ya naɗa fitaccen mawaƙin siyasar nan na Hausa, Dauda Kahutu Rarara, a matsayin Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa.

An yi bikin naɗin sarautar ne a garin Daura a ranar Asabar 13 ga watan Disamba, 2025 domin karrama rawar da Rarara yake takawa wajen haɓaka waƙoƙin Hausa da kuma tasirin da yake da shi a fagen nishaɗi da al’adu.

Jirgin sama ya yi hatsari yayin sauka a Kano Tsaro: Abba ya kafa runduna ta musamman da za ta ke tsaron tashoshin mota a Kano

Tun da farko mawaƙin da kansa ya wallafa goron gayyatar naɗin sauratar da za a yi masa a shafinsa na Facebook, a ranar 9 ga watan Disamba, 2025.

Rarara ya ce: “Ina gayyatar kowa da kowa zuwa wajen naɗin sarautata, mai taken ‘Sarkin Waƙar Ƙasar Hausa’ sarautar da mai Alfarma Sarkin Daura ya yi min.

“Za a yi naɗin a fadar Mai Martaba Sarkin Daura a ranar Asabar, 13 ga watan Disamba, 2025, insha’Allah Allah.”

Bikin naɗin sarautar ya samu halartar manyan mutane, mawaƙa, jarumai, ciki har da Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Barau I. Jibirin, Ali Nuhu da sauransu, inda masoya da magoya bayan mawaƙin suka nuna farin cikinsu.

Masoyan mawaƙin sun bayyana cewa wannan karramawa ta dace da gudunmawar da Rarara ya bayar ga al’adun Hausawa.

Rarara, wanda ya shahara wajen yin waƙoƙin siyasa da na zamantakewa, ya daɗe ana damawa da shi kuma yana daga cikin manyan mawaƙa a Arewacin Najeriya.

Sabuwar sarautar da aka yi masa na nuni da amincewa da gudunmawarsa wajen bunƙasa waƙa a harshen Hausa da kuma tasirinsa a cikin al’umma.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Yadda aka yi bikin naɗa Rarara sarkin wakar ƙasar Hausa a Daura
  • Mutum biyu sun mutu a harbin bindiga a Jami’ar Brown ta Amurka
  • Tsohon Jakadan Singapore A MDD Ya Jinjinawa Hangen Nesan Kasar Sin
  • Gwamna Radda Ya Dora Harsashin Gina Ma’aikatar Sarrafa Rogo A Katsina
  • Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 3 a Binuwai
  • ‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’
  • Farashin Kayan Abinci Na Sauka Yayin Da Bikin Kirsimeti Da Sabuwar Shekara Ke Matsowa
  • Kamfanonin Sin Sun Kera Tare Da Sayar Da Motoci Sama Da Miliyan 31 Tsakanin Janairu Zuwa Nuwamban Bana
  • Kotu Ta Yanke Wa Wani Mutum Hukuncin Kisa Bisa Garkuwa Da Kashe Mai Gidansa A Kano