Sojojin Yemen Sun Sanar Da Kai Wa Cibiyar Sojan Sama Ta “Nivatim” Hari Sau Biyu A Cikin Sa’o’i 24
Published: 27th, April 2025 GMT
Sojojin na kasar Yemen sun sake kai hari akan sansanin sojan saman a “Nivatim” na HKI a karo na biyu a cikin sa’o’i 24. Majiyar sojan kasar ta Yemen ta ce wannan shi ne karo na hudu da suke kai hari akan manufofin HKI a cikin sa’o’i 24.
Kakakin sojan kasar Yemen janar Yahya Sa’ri ya fada a wata sanar wa ta tashar talabijin cewa; sojojin kasar sun kai hari da makamai masu linzami da su ka fi sauti sauri wajen kai wa sansanin na “Nivatim” hari wanda yake a cikin yankin Naqab a Falasdinu dake karkashin mamaya.
Janar Sari ya kuma kara da cewa; hare-haren da suke kai wa HKI yana a karkashin ci gaba da taya Falasdinawa fada ne da suke yi,kuma sun sami sanarar saukar makamin a inda aka harba shi.
Haka nan kuma janar Sari ya ce; sojojin na Yemen za su ci gaba da karawa kansu karfi da yardar Allah ta hanyar bunkasa makaman da suke da su domin fuskantar ‘yan sahayoniya.
A jiya Asabar ne dai sojojin na Yemen su ka sanar da cewa sun kai hare-hare biyu da jiragen sama marasa matuki akan wasu muhimman manufofi na ‘yan sahayoniya a yankin Yafa dake karkashin mamaya da kuma a yankin Asqalan dake kusa da Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Dakarun Juyin Juya Halin Musulunci Na Iran Sun Kakkabo Jiragen Yakin Isra’ila Biyu Kirar F-35
Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta zama kasa ta farko a duniya da ta harbo jiragen saman yaki kirar F-35
Iran ta zama kasa ta farko a duniya da ta yi nasarar harbo jiragen yaki kirar F-35, bayan da ta yi nasarar auna wasu jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila kirar F-35 guda biyu, kuma ta barar da su kasa.
Gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila ta yi amfani da wadannan jirage masu tsananin ci gaban zamani wajen kai hare-haren wuce gona gona da iri kan Jamhuriyar Musulunci ta Iran da safiyar ranar Juma’a, wanda hare-haren suka yi sanadiyyar shahadar wasu manyan jami’an sojan Iran da masana kimiyyar nukiliya da fararen hula da suka hada da mata da kananan yara.
Ma’aikatar hulda da jama’a ta rundunar sojojin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta sanar a cikin wata sanarwa da ta fitar cewa: Dakarun tsaron saman Iran sun harbo jiragen saman yaki kirar F-35 guda biyu, baya ga wasu jiragen saman yakin yahudawan sahayoniyya marasa matuka ciki.
Sanarwar ta nuna cewa: Jami’an tsaron Iran sun kame daya daga cikin matukan jiragen wacce mace ce, kuma ana kan bincike domin sanin makomar matukin daya jirgin.
Abin lura shi ne cewa: Jiragen yakin kirar F-35 da ‘yan sahayoniyya ke amfani da su na daga cikin wadanda suka ci gaba a duniya kuma ake gwada su.