Sojojin Yemen Sun Sanar Da Kai Wa Cibiyar Sojan Sama Ta “Nivatim” Hari Sau Biyu A Cikin Sa’o’i 24
Published: 27th, April 2025 GMT
Sojojin na kasar Yemen sun sake kai hari akan sansanin sojan saman a “Nivatim” na HKI a karo na biyu a cikin sa’o’i 24. Majiyar sojan kasar ta Yemen ta ce wannan shi ne karo na hudu da suke kai hari akan manufofin HKI a cikin sa’o’i 24.
Kakakin sojan kasar Yemen janar Yahya Sa’ri ya fada a wata sanar wa ta tashar talabijin cewa; sojojin kasar sun kai hari da makamai masu linzami da su ka fi sauti sauri wajen kai wa sansanin na “Nivatim” hari wanda yake a cikin yankin Naqab a Falasdinu dake karkashin mamaya.
Janar Sari ya kuma kara da cewa; hare-haren da suke kai wa HKI yana a karkashin ci gaba da taya Falasdinawa fada ne da suke yi,kuma sun sami sanarar saukar makamin a inda aka harba shi.
Haka nan kuma janar Sari ya ce; sojojin na Yemen za su ci gaba da karawa kansu karfi da yardar Allah ta hanyar bunkasa makaman da suke da su domin fuskantar ‘yan sahayoniya.
A jiya Asabar ne dai sojojin na Yemen su ka sanar da cewa sun kai hare-hare biyu da jiragen sama marasa matuki akan wasu muhimman manufofi na ‘yan sahayoniya a yankin Yafa dake karkashin mamaya da kuma a yankin Asqalan dake kusa da Gaza.
উৎস: HausaTv
এছাড়াও পড়ুন:
Manjo Janar Musawi: Ko Kadan Ba Mu Yarda Da Amurka Ba
Babban hafsan hafsoshin sojan Iran Manjo janar Musawi ya ce, ko kadan Iran ba ta yarda ko gaskata alkawullan Amurka,balle kuma zancen ‘yan sahayoniya.
Babban hafsan hafsoshin sojan na Iran ya kuma kara da cewa, sojojin kasar suna cikin Shirin ko-ta-kwana domin kalubalantar duk wan igigi na abokan gaba.
Manjo janar Musawi ya bayyana hakan ne dai a lokacin da ya yi tattaunawa ta wayar tarho da ministan tsaron kasar Tajikistan Manjo janar Imam Ali Sabir Zadeh.
A nashi gefen, ministan tsaron kasar ta Tajikistan, ya fara da yi wa janar Musawi murnar zabarsa sabon hafsan hafsoshin sojan kasar ta Iran, sannan kuma ya nuna bakin cikinsa akan rashin kwamandojin sojan Iran da su ka yi shahada a sanadiyyar harin ta’addancin HKI.
Manjo janar Imam Ali Sabir Zadeh ya kuma kara da cewa, al’ummar kasar Tajikinstan sun yi bakin ciki, don haka suna isar da ta’aziyyarsu ga al’ummar Iran.
Har ila yau minstan tsaron kasar ta Tajikistan ya yi ishara da tarayya akan harshe da al’ada da kasashen biyu su ka yi, haka nan kuma tarihi.
Haka nan kuma manjo janar Musawi ya yi wa Tajikistan godiya akan yadda ta kasance a tare da Iran a lokacin yakin kwanaki 12, lamarin da ya kara karfin alakar kasashen biyu.