Aminiya:
2025-08-01@09:51:56 GMT

HOTUNA: Yadda aka dawo da ’yan Najeriya 203 daga Libya

Published: 29th, April 2025 GMT

Kalli yadda aka karɓi ’yan Najeriya guda 203 da aka dawo da su daga ƙasar Libya.

(Hoto: Onyekachukwu Obi).

.

উৎস: Aminiya

কীওয়ার্ড: Libya Najeriya

এছাড়াও পড়ুন:

Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni

Sai dai girma, kima da ɗaukakar da matasa ke da ita ga al’umma ta ja baya ƙasa sosai a bisa ga yadda rayuwarsu ke iyo da ninƙaya a kogin  zubar da mutunci ta hanyar aiwatar da abubuwan da ke da alamar ayar tambaya.

Matasa da dama a yau ba su ganin kowa da gashi, ba su girmama kowa, ba su ganin mutuncin kowa, ba su daraja kowa ballantana har a tsawata masu ko a ba su shawara da ɗora su kan hanyar yadda za su daidaita rayuwar su daga gurɓatacciyar hanya zuwa madaidaiciyar hanya.

Abin takaici ne da matuƙar damuwa yadda matasa suka gurɓata rayuwarsu mamakon amfani da lokaci da damar da suke da ita amma sai suka zaɓi biyewa ruɗin abokai da son zuciya wajen aikata abubuwan da ba su kamata ba.

Al’ummar Arewacin ƙasar nan da aka shaida da tarbiya, kamun- kai, mutunci da sanin ya kamata, a yau an wayi gari sun ɗauki gurɓatattun halayen da suka mayar da su marasa tarbiya. 

Rashin kulawar iyaye, malamai, shugabanni da dukkanin masu da tsaki ga sanya idanu ga yadda ƴaƴansu ke gudanar da rayuwar su babbar matsala ce mai zaman kan ta da ta taimaka wajen gurɓacewar rayuwar matasa.

Iyaye da dama na sakaci wajen kulawar musamman ga tarbiyar ƴaƴansu ta hanyar rashin saka idanu sosai ga yadda ƴaƴan ke gudanar da rayuwar su, abokan da suke hulɗa, wuraren da suke zuwa, binciken wayoyin su, suturar da suke saka wa da sauransu.

Idan da iyaye suna bayar da cikakkiyar kulawa ga kula da tarbiyar ƴaƴansu ta hanyar bin diddigin su a kai- a- kai da zai yi wahala a riƙa kuka a yau a yadda tarbiyar matasa ta sukurkurce.

Matasan Arewa a yau sun zama abin nunawa a bisa ga yadda tarbiyar su ta yi faɗuwar baƙar tasa, lamariin da al’ummar yankin ke kuka da kokawa musamman bisa ga rashin sanin makomar rayuwar matasa a shekaru masu zuwa.

A halin yanzu tarbiyar matasa maza da mata na fuskantar mummunar barazana da ke buƙatar iyaye, shugabanni, malamai da dukkanin masu ruwa da tsaki su tashi tsaye domin yi wa tufkar hanci tun kafin a makara wajen shawo kan bahaguwar matsalar.

Canjin zamani, kwaikwayon ɗabi’un rayuwar Turawa da kwaɗayi sun taka kuma suna ci-gaba da taka muhimmiyar rawa wajen gurɓacewar tarbiyar matasa a wannan zamanin.

Karuwanci, hulɗa da abokan banza, sharholiya da baɗala, shaye- shayen kayen maye, amfani da kafafen sada zumunta na zamani, kallon fina- finan banza, wayoyin hannu, ƙungiyoyin asiri, neman jinsi tsakanin mata da maza a baƙaƙen ɗabi’un namiji da namiji da mace da mace da sauran ayyukan fitsara lamba ɗaya abubuwa ne da ke tsunduma matasa a kogin da- na- sani 

Haka ma jahilci, talauci, kwaɗayi da neman abin duniya ido rufe da sauransu matsaloli ne da idan matasa ba su tashi tsaye haiƙan suka yaƙe su ba, to za su kai su su baro a lokacin da za su fahimci sun makaro sun makaro.

Bugu da ƙari kafafen sada zumunta na soshiyal midiya na kan gaba-gaba wajen bayar da gagarumar gudunmuwa wajen gurɓata tarbiyar matasa ta yadda matasa maza da mata ke aiwatar da abubuwan da tamkar ba su da mafaɗi.

Shigar banza ta hanyar tallata tsiraici, furta kalaman da ko kare ba zai ci ba, karuwancin yanar gizo, kalwanci tsakanin mata da maza abubuwa ne da matasa a yau ke cin karen su ba babbaka a dandalin soshiyal midiya.

Shafukan soshiyal midiya a yau a cike kuma a gurɓace suke da shafukan karuwai, ƴan daudu, ƴan luwaɗi da ƴan maɗigo waɗanda a fili suke tallata hajar su ga abokan harka wanda hakan babbar illa ce kuma babban ƙalubale ga tarbiyar matasa.

Haka ma yadda al’ummar Arewa ke gudanar da bukukuwan aure a wannan zamanin ya nuna a fili irin girman lalacewar da tarbiya ta yi a yankin a bisa ga yadda mata ke baje- kolin tsiraicin su a shigar banza wadda amarya ke jagoran ta.

Baƙuwar al’adar ranar ƙauyawa da aka fito da ita wadda a wajen bukukuwa a Arewa rana ce ta musamman da ƴan mata ke shigar fitsara da raye- rayen baɗala tamkar a ƙasar arna lamari ne da tuni gwamnatoci a Arewa suka fara ɗaukar mataki.

Gwamnatin Kano ta kasance ta farko wajen haramta ranar ƙauyawa a bukukuwan da al’ummar jihar ke yi a bisa ga illa, baɗala da matsalolin da ranar ke haifarwa musamman zubar da mutunci da darajar kyawawan al’adun ƙasar Hausa.

Bugu da ƙari sabuwar ɗabi’ar ‘saka hannu’ da matasa ƴan manyan makarantu ke yi a bisa ga murnar kammala karatu babbar matsala ce ga tarbiyar matasa. Matasan maza da mata kan yi rubutun saka hannu da maka a riguna da hijaban ƴan mata a ranar da suka kammala karatu tare da taɓa ƙirji da sauran sassan jikin matan.

Sabon salon na saka hannu a yanzu ya ɓulla har a makarantun sakandire wanda hakan babbar matsala ce da wasu gwamnatocin suka hango suka kuma haramta ɗabi’ar bakiɗaya a makarantu.

A bisa ga wannan matsalar da illarta, kwanan nan a wannan watan na Yuli gwamnatocin jihohin Sakkwato da Yobe suka bayar da sanarwar haramta murnar ‘saka hannu’ a dukkanin makarantun sakandire a jihohin biyu, matakin da ya samu yabo daga al’ummar ciki da wajen jihohin tare da kira ga sauran jihohi da su yi koyi.

Jama’a da dama na ganin gurɓatacciyar rayuwar da matasa suka ɗauka a matsayin wayewa a wannan zamanin muddin ba a samu nasarar shawo kan ta ba, to illar da za ta haifar ga manyan gobe da ke tasowa ba ƙarama ba ce.

Binciken LEAɗERSHIP HAUSA ya nuna ƴan siyasa na da kaso mai yawa na gurɓacewar rayuwar matasa a dalilin saka su aikata mabambantan ayyukan assha da suka zama silar rasa martabar su.

ƴan siyasa da dama a yau suna amfani da matasa wajen saka su a harkokin bangar siyasa, ba su kuɗin maye ko kayan maye, figar gashin kazar wannan da fashin ƙwan kazar wancan, tayar da hayaniya a wajen taron waccan jam’iyyar, ƙone ofishin ɗaya jam’iyyar da ma illata abokan adawa.

Abin damuwa ne yadda jam’iyyun siyasa a ƙasar nan ke ƙarfafa  harkokin bangar siyasa a dukkanin tarukan yekuwar neman zaɓen su a inda a kan ga matasa cike da motoci da babura a cikin shigar banza ɗauke da kowane iirin nau’i na miyagun makamai

A cewar Mainasara Giɗaɗo “yan siyasar da ke amfani da matasa wajen bangar siyasa gabanin zaɓe, galibi bayan samun nasara su kan watsar da matasan a kondon shara ba tare da assasa shiraruwan tallafawa rayuwarsu ba wanda ya kamata matasan su yi wa kan su karatun ta- natsu ta hanyar ƙauracewa waɗanda ba su damu da inganta rayuwar su ba.”

Ya ce “Matasa da dama a yau waɗanda ya kamata su himmatu wajen neman ilimi da aiki da shi tare da gudanar da sana’o’i nagari, sun banzantar da lokacin su ga shiga sabgogin da suke zubar da kima da mutuncin su ga al’umma.”

A yau matasan ƴan mata sun dabaibaye rayuwarsu da rashin tarbiya, sharholiya da baɗala da mayar da fitsara tamkar wani ado na musamman lamarin da ya zama babban ƙalubale gare su wajen samun mazaje nagari.

Masu fashin baƙin lamurran yau da kullum kan bayyana cewar kasuwar kamilallun ƴan mata nagari waɗanda suka nesanta kan su da ayyukan baɗala da abota da ƙawayen banza ta fi tashi a sauƙin neman aure akasin ƴan matan da suka yi wa kan su baƙin fentin fitsara da ke kasa samun mazaje cikin sauƙi.

A gidan aure rahotanni sun nuna yadda ƴan mata da dama ke kasa sauke nauyin gida da ya rataya a wuyansu domin galibin matasan wannan zamanin a bayyane suke bayyanawa mazaje su ba za su iya yi masu girki ba ballantana gudanar da wasu aikace- aikacen gida da suka wajaba wanda duka rashin tarbiya ne ya haddasa hakan.

A ra’ayin wani matashi, Ayuba Bello Okimo ya bayyana cewar rayuwar matasa ta na cikin babban ƙalubale a kan yadda suka tsunduma a harkokin zubar da mutunci.

Ya ce “Tabbas rayuwar matasa ta na cikin babban ƙalubale domin matasa sun tsunduma a harkokin banza da shaye- shaye gadan gadan wanda yayi tasiri wajen gurɓacewar tarbiyar matasa.”

“Wannan matsalar a yanzu har ta kai matasa na ganin matashin da ba ya yi bai waye ba, kazalika matasa a wannan lokacin suna son kuɗi ta kowane hali da son yin rayuwa mai kyau amma sai dai ba sa son neman na kai da aikin wahala, don haka lallai- lallai akwai ƙalubale sosai.”

Ya ce “ɗukkan al’ummar da Allah ya arzirta su da matasa a na cewa sun yi dace domin duk abin da ya tunkaro su za su nuna ƙarfi da zarra irin ta matasa domin cinma nasara. Tabbas Arewacin Nijeriya Allah ya albarkace mu da matasa, amma sai dai kash waɗannan matasan maimakon su kasance matasa wadanda za a yi alfahari da su sai suka kasance waɗanda ake kuka da su, sabo da an riga da an gurɓata tunani da hankalinsu, ta hanyar ayyukan banza da shaye- shaye.”

“Wasu daga cikin azzaluman shugabanni waɗanda ba sa kishin matasan ballantana son ci-gabansu, su ke saya musu kayan shaye shaye suna sha domin kawar da hankalinsu domin aiwatar da ayyukan da suka ɗora su a kai a lokacin da  su kuma ƴayansu suna makarantun ƙwarai a ciki da wajen ƙasa suna karatu.”

Ya ce wajibi ne matasa su yi wa kan su faɗa su yi karatun ta- natsu domin ceto goben su ta yadda za a yi alfahari da su ko bayan rai ya yi halinsa.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Taɓarɓarewar Tarbiyyar Matasa A Arewa: Ƙalubalen Da Ke Gaban Iyaye Da Shugabanni
  • NAJERIYA A YAU: Me dokar kasa ta ce kan karin wa’adin aiki da Shugaban Kasa ke yi?
  • Majalisar Kasa Na Duba yiwuwar Dawo Da Gwamnan Jihar Rivers Fabura Kafin Cikar Wa’adin Watanni Shida.
  • Kasar Iran Ta Bayyana Gushewar Hasashen Raunin Karfin Sojinta Kuma Ba Zai Dawo Ba
  • Wasu ’yan siyasa na sukar Tinubu saboda ɗan Kudu ne — Onanuga
  • NAJERIYA A YAU: Tinubu ya yi wa Arewa adalci a ayyuka da mukamai — Bayo Onanuga
  • Yadda ’yan bindiga suka tarwatsa ƙauyuka sama da 10 a Katsina
  • DAGA LARABA: Dalilan al’ummomi na rungumar gwaji kafin aure
  • Fiye Da Kamfanoni 30,000 Masu Zuba Jari Daga Waje Aka Kafa A Sin A Rabin Farkon Bana
  •  Wani Dan Majalisar Iran Ya Yi Kira Ga A Yi Siyasar Kin Gabatar Da Bayanai A Tattaunawa Da Kasashen Turai