Leadership News Hausa:
2025-04-30@19:33:09 GMT

Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana

Published: 29th, April 2025 GMT

Gwamnatin Yobe Na Ƙoƙarin Inganta Tsaro – Hon. Idi Gubana

A nasa ɓangaren, mai bai wa Gwamnan Shawara Kan Al’ammuran Tsaro, Janar Dahiru Abdusalam (Mai Ritaya), ya tabbatar da cewa gwamnatin jihar tana ɗaukar matakai tare da jami’an tsaro don samar da tsaro mai inganci.

Ya kuma bayyana cewa duk da matsalolin tsaro da ake fuskanta a hanyar Damaturu zuwa Gujba, jami’an tsaro na ƙoƙarin yin sintiri domin tabbatar da tsaro.

Janar Dahiru ya ce, “Koda yake muna fuskantar ƙalubale daga Boko Haram a yankunan wasu sansanin sojoji, jami’an tsaro na ci gaba da aikinsu domin kare yankin.”

Ya ƙara da cewa, “Muna taka-tsan-tsan musamman wajen daƙile karɓar haraji daga Boko Haram a wasu yankuna. Wannan al’amari yana da matuƙar wahala, amma muna fatan za mu samu nasara.”

Janar Dahiru ya tabbatar da cewa akwai tsaro a dukkanin sassan jihar tare da haɗin gwiwar sojoji, ‘yansanda, Civilian JTF da ‘yan sa-kai.

Ya kuma bayyana cewa za a fitar da sabbin dabaru cikin makonni masu zuwa domin yaƙar ‘yan ta’adda.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Mataimakin Gwamna Tsaro

এছাড়াও পড়ুন:

Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo

Michael, wanda ke zaune a Phase 4, ya yi ƙoƙarin ceton abokinsa, amma shi ma makiyayin ya sare shi da adda.

An garzaya da Michael zuwa Asibitin Mararaba domin ceto rayuwarsa, amma likita ya tabbatar da mutuwarsa bayan isar su.

‘Yansanda sun bayyana cewa an adana gawar Michael a asibitin domin gudanar da bincike.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, ya umurci a tura jami’an tsaro domin kare rayuka da dukiya a yankin, tare da umartar Mataimakin Kwamishinan Sashen Binciken Laifuka da ya fara bincike da kuma kamo wanda ake zargi domin gurfanar da shi a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Tarayyar Afirka ta dage takunkumin da ta kakabawa Gabon
  •  Bom Da Ya Tashi A Arewa Maso Gabashin Najeriya Ya Kashe Mutane 6
  • Talauci Da Rashin Ilimi Ne Ya Sa Ayyukan Boko Haram Ke Dawowa – Gwamnan Yobe
  • Nazarin CGTN: Ana Kara Bayyana Rashin Gamsuwa Da Sabuwar Gwamnatin Amurka Daga Ciki Da Wajen Kasar
  • Rashin tsaro: Gwamnan AbdulRahman Ya Gana Da Sarakuna Masu Daraja Ta Daya A Jihar Kwara 
  • Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
  • Boko Haram Sun Hallaka ‘Yan Zaman Makoki 7, Sun Jikkata Wasu A Borno
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara
  • Ƴan Ta’adda Sun Kashe Maharba 10 A Adamawa