Leadership News Hausa:
2025-11-25@06:26:10 GMT

Shin Manchester United Za Ta Iya Lashe Kofin Europa League?

Published: 26th, April 2025 GMT

Shin Manchester United Za Ta Iya Lashe Kofin Europa League?

Manchester United ta kai zagayen kusa da karshe ne bayan doke Olympic Lyon ta Faransa da 5-4, bayan an yi canjaras da 2-2 a wasan farko da aka buga a Faransa. Kenan United ta yi nasara da 7-6 jimilla. Yanzu United za ta fafata wasan gab da na karshe ne da kungiyar Athletic Bilbao a ranar 21 ga watan Mayu.

 

Kungiyar ta Bilbao ta kai wasan karshe a gasar Europa sau biyu, na karshen a shekarar 2012, lokacin da Atletico Madrid ta doke ta da ci uku da nema a Bucharest.

 

Shekara 13 ke nan rabon United ta hadu da Athletic Bilbao, inda kungiyar ta Sifanya ta doke United da 2-1 a gasar ta Europa a shekarar 2012. Ita kuma United wannan ne karo na biyu da za ta buga wasan gab da na karshe a gasar Europa a shekara hudu.

 

A wancan karon, Manchester United ta doke Roma da ci 8:5 jimilla sai dai kungiyar Billareal ta doke ta a wasan karshe a bugun fanareti bayan an tashi wasan kunnen-doki.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

এছাড়াও পড়ুন:

’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba

Daga Aminu Dalhatu

Rundunar ’Yan Sanda a Jihar Zamfara ta ce ta samu nasarar ceto mutune 25 da aka yi  yunkurin sacewa, bayan  wani hari da ’yan bindiga suka kai wa kauyen Kuraje da ke yankin Damba a Karamar Hukumar Gusau.

Wata sanarwa da Jami’in Hulda da Jama’a na Rundunar, DSP Yazid Abubakar, ya fitar ta bayyana cewa lamarin ya faru ne a daren Juma’a 21 ga watan Nuwamban 2025, da misalin karfe 10 saura kwara, lokacin da gungun ‘yan bindiga dauke da makamai suka mamaye yankin, suna harbe-harbe tare da tasa keyar  mata 10 da yara 15 domin tafiyada su.

Sanarwar ta ce bayan samun kiran gaggawa, tawagar sintiri ta ’yan sanda daga sashen Damba da Sashen Ayyuka na Gusau tare da hadin guiwar jami’an tsaro na sa kai wato Community Protection Guards (CPG) sun hanzarta isa yankin.

Jami’an sun bi diddigin ’yan bindigar da suka tsere sannan suka shiga wani salon aiki na dabaru wanda ya kai ga kubutar da dukkan mutanen da aka sace.

DSP Abubakar ya ce an garzaya da wadanda aka ceto zuwa Sabongari Damba domin tabbatar da tsaronsu, duba lafiyar su da tantance su kafin a mika su ga iyalansu.

Kwamishinan ’Yan Sandan Jihar Zamfara, CP Ibrahim Balarabe Maikaba, ya jinjinawa jarumta da kwarewar jami’an da suka gudanar da aikin.

Ya kuma tabbatar da kudirin rundunar na ci gaba da kare rayuka da dukiyoyin jama’ar jihar.

 

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Slot na fuskantar matsin lamba saboda rashin kataɓus a Liverpool
  • Habasha: Bayan Shekaru 10,000 Dutsen Hayli Gubbi Ya Yi Aman Wuta
  • Najeriya: Kungiyar Yan Ta’adda Ta ISWAP Ta Sace Yan Mata 13 A Jihar Borno
  • Antonio Guterres Ya Kira Yi Kungiyar G 20 Da Su Warware Matsalar Rashin Adalci A Harkokin Kasuwanci
  • An Fitar Da Kudurin Bayan Taron Kungiyar G20 Ba Tare Da Halartar Kasar Amurka Ba
  • An Gabatar Da Jawabin Bayan Taro Na Kungiyar G20 Duk Tare Da Kauracewar Amurka
  • Gwamnatin Yobe ta ba da umarnin rufe makarantun kwana a jihar
  • ’Yan Sanda a Zamfara Sun Ceto Mutane 25 Bayan Dakile Harin ’Yan Bindiga a Damba
  • Mutane 315 ne suka ɓace bayan hari a makaranta Neja
  • Ɗalibai 215 da malamai 12 aka sace a Makaranta a Neja — CAN