Mahukunta Gandun Daji Na Hadejia Sun Kai Ziyarar Aiki Hukumar NOA
Published: 26th, January 2025 GMT
Hukumar kula da gandun daji na Hadejia ta ce wuraren shakatawa na kasa suna taka rawar gani ta fuskar kiyaye halittu, da magance matsalolin sauyin yanayi, da inganta bincike, da ci gaba, gami da samar da ayyukan yi a Najeriya.
Mukaddashin jami’in kula da gandun dajin, Mista Jonah Moses ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar neman shawarwari ofishin wayar da kan jama’a na kasa da ke Dutse, babban birnin jihar Jigawa.
Ya nanata cewa al’umma za su kara fahimtar fa’idojin irin wadannan wurare ne kadai idan Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Kasa NOA, ta taimaka wajen fadakarwa ko ilmantar da jama’a.
Jonah Moses ya bayyana cewa, sun kawo ziyarar ce domin ganawa da masu ruwa da tsaki irin su hukumar ta NOA, wadanda za su iya taimakawa wajen fahimtar da jama’a game da gandun daji na Hadejia.
Da yake mayar da martani, Daraktan Hukumar Wayar da Kan Jma’a ta kasa NOA na jihar Jigawa, Malam Ahmad Tijjani Ibrahim ya yabawa mai kula da gandun dajin na Hadejia da tawagarsa bisa da kwazon da suke nuna wajen tafiyar da ayyukansu.
Ya kara da cewa hukumar ta ba da fifiko kan batun sauyin yanayi, inda ta samar da sashen kula da muhalli, da yanayi, da makamashi.
Shugaban hukumar ta NOA ya tabbatar wa tawagar cewa a shirye hukumar ta ke na zaburar da al’ummar kasa game da ayyukan gandun dajin.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
‘Haduwata da masu garkuwa da ɗan uwana a dajin Zamfara’
Wani mazaunin Kano, Namadi Bawa, ya bayyana yadda ya shiga cikin daji a Jihar Zamfara domin kai kudin fansa ga ’yan bindiga da suka sace ɗan uwansa, inda ya tarar da su cikin mawuyacin hali na rashin lafiya, kafin daga bisani ya samu ya kubutar da shi. A tattaunawar mutumin da Aminiya, y ace an sace ɗan uwan nasa ne a Gusau babban birnin jihar Zamfara, a kan hanyarsa ta dawowa daga Sakkwato.A cewar Namadi, ɗan uwansa ya ci karo da shingen da ya yi kama da na jami’an tsaro a hanya, sai dai daga baya aka gano ’yan bindiga ne suka yi masa kwantan bauna tare da wasu fasinjoji.“Sun kira ni suka tambaya ko na san ɗan uwana, na ce eh. Suka ce sun sace shi kuma yana hannunsu. A lokacin kwana ɗaya kenan da sace shi,” in ji Namadi.
Cinikin kuɗin fansa da tafiya daji domin kai musuYa ce masu garkuwar sun fara neman kuɗin fansa har Naira miliyan 16, amma bayan tattaunawa aka rage zuwa miliyan bakwai.
Namadi ya ce masu garkuwar sun yi gargaɗin cewa ba za su lamunci rage wani abu daga adadin kudin da aka yi cinikin ba, suna gargaɗin cewa muddin suka ƙirga kuɗin suka ga ba su cika ba, za a ga ba daidai ba.
“Sun ja hankali cewa kada a rage ko ƙwandala a ciki, idan aka rage za a ga ba daidai ba,” in ji shi.
Namadi ya bayyana yadda ya je da kansa ya kai kudin cikin daji.
A cewarsa, an umurce shi ya tsaya a wani ƙauye kafin daga bisani a nuna masa hanyar shiga. Daga bisani aka ba shi wata riga ya saka kafin ya isa wurin da aka karɓi kudin.
“Na zaci za su ƙirga kudin, amma sai suka tattaka su da ƙafa, suka ce sun cika. Bayan haka suka ce na gangaro daga kan dutsen da suka kai ni. Na yi ta kallo ko zan ga ɗan uwana, amma daga baya ne suka nuna min shi tare da wasu da aka sace, duk suna kwance cikin yanayin rashin lafiya,” in ji shi.
Yanayin dajin da masu garkuwarNamadi ya ce yanayin da ya tarar da su ya nuna suna fama da cutar kwalara, inda aka ajiye su a bukka a tsakiyar dajin da ba motar da za ta iya shiga sai babur.
“Na san idan a wannan yanayin ne, ba za su yi dogon zango ba. Ta su za ta kare,” in ji shi.
Ya ƙara da cewa ɗan uwansa da sauran da aka sace sun shiga mawuyacin hali, inda dole ne aka kai ɗan uwansa asibiti bayan an karɓo shi saboda yanayin da aka same shi.
Namadi ya kuma ce duk da fargaba da tashin hankalin da ya shiga, addu’a ce ta taimaka masa ya dawo gida lafiya.
“Mu ci gaba da addu’a saboda tana da tasiri a kan mutanen nan. Insha Allahu Allah zai kawo ƙarshen su,” in ji shi.
Cin karo da wasu masu garkuwar a hanyar dawowaBayan ya karɓo ɗan uwansa, Namadi ya ce a hanyarsa ta fita daga dajin ya sake cin karo da ’yan bindigar sun kamo wasu mutanen, suna kaɗa su zuwa cikin daji.
“Sun ba ni shawara kada na bi ta inda na zo, saboda akwai ƙungiyoyin masu garkuwa da dama a yankin waɗanda ba sa ga maciji da juna da za su iya sake kama mu,” in ji shi.
Daga nan sai ya ce duk da muggan makaman da ’yan bindigar ke da su, ba su fi ƙarfin gwamnati ba.
Ya yi kira ga gwamnati da ta ƙara ƙoƙari wajen kawar da ’yan bindiga a yankin, tare da fatan addu’ar jama’a za ta taimaka wajen kawo ƙarshen matsalar.