Mahukunta Gandun Daji Na Hadejia Sun Kai Ziyarar Aiki Hukumar NOA
Published: 26th, January 2025 GMT
Hukumar kula da gandun daji na Hadejia ta ce wuraren shakatawa na kasa suna taka rawar gani ta fuskar kiyaye halittu, da magance matsalolin sauyin yanayi, da inganta bincike, da ci gaba, gami da samar da ayyukan yi a Najeriya.
Mukaddashin jami’in kula da gandun dajin, Mista Jonah Moses ya bayyana haka a lokacin da ya kai ziyarar neman shawarwari ofishin wayar da kan jama’a na kasa da ke Dutse, babban birnin jihar Jigawa.
Ya nanata cewa al’umma za su kara fahimtar fa’idojin irin wadannan wurare ne kadai idan Hukumar Wayar da Kan Jama’a ta Kasa NOA, ta taimaka wajen fadakarwa ko ilmantar da jama’a.
Jonah Moses ya bayyana cewa, sun kawo ziyarar ce domin ganawa da masu ruwa da tsaki irin su hukumar ta NOA, wadanda za su iya taimakawa wajen fahimtar da jama’a game da gandun daji na Hadejia.
Da yake mayar da martani, Daraktan Hukumar Wayar da Kan Jma’a ta kasa NOA na jihar Jigawa, Malam Ahmad Tijjani Ibrahim ya yabawa mai kula da gandun dajin na Hadejia da tawagarsa bisa da kwazon da suke nuna wajen tafiyar da ayyukansu.
Ya kara da cewa hukumar ta ba da fifiko kan batun sauyin yanayi, inda ta samar da sashen kula da muhalli, da yanayi, da makamashi.
Shugaban hukumar ta NOA ya tabbatar wa tawagar cewa a shirye hukumar ta ke na zaburar da al’ummar kasa game da ayyukan gandun dajin.
Usman Muhammad Zaria
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
এছাড়াও পড়ুন:
Rawar Da Dakta Bello Matawalle Ke Takawa Wajen Inganta Harkokin Tsaro A Nijeriya
Daya daga cikin manyan nasarorin da Dakta Bello Matawalle ya samu shi ne kaimi da aka yi wurin yaki da ta’addanci, ta hanyar kyautata hadin gwiwa da Sojojin kasa, da Sojojin sama da sauran hukumomin tsaro. An yi rugu-rugu da matattaran ‘yan ta’adda a Arewa Maso Gabas, wanda hakan ya yi sanadiyar raguwar hare-hare. A Arewa Maso Yamma kuwa, gagarumar gudummawa da ma’aikatar tsaro a karkashinsa ta amfani da karfin soja ya yi mummunar illa ga matattarar ‘yan ta’adda wanda hakan ya kyautata fata da al’umma ke da shi cewa an kusan share musu hawaye.
2. Kula da walwalar sojoji da karfafa musu gwiwa
Ganin cewa karfin Sojan Nijeriya ya dogara ne a rundunarta, Dakta Bello Matawalle ya inganta hanyoyin walwalar sojojin ta hanyar biyan su kudin alawus a kan lokaci, kyautata matsuguninsu, da kuma samun ingantaccen kiwon lafiya. Wannan ya kara azama wa sojojin da suke gwabza yaki a fagagen fama.
3. Zamanantar da Dakarun Sojoji
Ganin bukatar gaggawa da ke akwai na zamanantar da sojojin Nigeriya, Matawalle ya samar da waraka ta hanyar samar da sabbin makamai na zamani, da jirage marasa matuki don tattara bayanai da kuma kayan ayyuka da sojoji ke bukata lokacin yaki.
Wadannan kayayyaki sun inganta dabarun da sojoji ke amfani da su ta hanyar raguwar yawan sojojin da ke rasa rayukansu da kuma karuwar nasarori a duk lokacin da aka fita ba-ta-kashi.
4. Raguwar sace-sacen mai da zagon kasa wa tattalin arziki.
Tattalin arzikin Nijeriya ya jima na fama da illar da ake masa sakamakon satan danyen mai a yankin Niger Delta. A karkashin jagorancin Matawalle, an samu karuwar aikace-aikacen da suka hada da hadin gwiwar sojojin ruwa wadanda suka hada da lalata cibiyoyin sace danyen mai wanda hakan ya haifar da aruwar danyen mai da ake fitar da kuma karin kudaden shiga ga kasa.
5. Karfafa mu’amala da hadin gwiwa a yankin Afrika da kasa-da-kasa.
Yawancin matsalolin tsaro ya kan wuce iyakar kasa, saboda haka ne Dakta Matawalle bai yi kasa a gwiwa ba wurin daukar matakan kulla kawance da makwabtan asashe irin su Chadi, da Nijar da Kamaru, da sauran kawayen kasashe irin su Amurka, Birtaniya da Tarayyar Turai wanda ya inganta yanda ake tattara bayanai da kuma musayar bayanan sirri. Hakan ya sa ‘yan ta’adda da masu aikata muggan laifuka ke samun wahalar samun maboya.
6. Karfafa kere-keren kayan yaki a gida
Bisa umurnin da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya bayar na tunanin dogaro da kai a fannin tsaro, Dakta Bello Matawalle ya yi kokarin agaza wa Hukumar Samar da Kayan Yaki ta Nijeriya (DICON) domin kara samar da makaman yaki a gida Nijeriya. Wannan mataki ya rage dogaro da kasashen waje da kuma karfafa tattalin arzikin tsaron Nijeriya.
Baya ga bangaren yaki, Bello Matawalle yana cigaba da jaddada muhimmancin aiki da al’umma domin dawo da tsaro. Wannan kiranye da yake yi wurin neman tattaunawa, da sasanci da kuma ayyukan cigaba a yankunan da ake rikici sun taimaka matuka gaya wajen dinke rashin yarda tsakanin jami’an tsaro da kuma fararen hula, wanda hakan zai haifar da zaman lafiya mai dorewa.
Jagorancin Bello Matawalle ya nuna aiki ba kama kafar yaro, sabbin dabaru, da kuma kishin kasa. Nasarorinsa ya nuna irin fahimtarsa a matsalolin tsaron Nijeriya da kuma irin niyyar da gwamnati ke da shi wurin magance su.
Bashir Aliyu dan jarida ne mai nazarin al’amuran da suka shafi siyasa da tsaro.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp