Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo
Published: 29th, April 2025 GMT
Michael, wanda ke zaune a Phase 4, ya yi ƙoƙarin ceton abokinsa, amma shi ma makiyayin ya sare shi da adda.
An garzaya da Michael zuwa Asibitin Mararaba domin ceto rayuwarsa, amma likita ya tabbatar da mutuwarsa bayan isar su.
‘Yansanda sun bayyana cewa an adana gawar Michael a asibitin domin gudanar da bincike.
Kwamishinan ‘yansandan jihar, ya umurci a tura jami’an tsaro domin kare rayuka da dukiya a yankin, tare da umartar Mataimakin Kwamishinan Sashen Binciken Laifuka da ya fara bincike da kuma kamo wanda ake zargi domin gurfanar da shi a kotu.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppএছাড়াও পড়ুন:
Zaɓen 2027 ya hana ni korar wasu ma’aikata – Bago
Gwamnan Jihar Neja, Mohammed Umaru Bago, ya jaddada goyon bayansa ga wa’adin mulki ɗaya kacal ga gwamnonin, yana mai cewa hakan zai inganta aiki da kuma inganta harkokin mulki.
Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake rantsar da sababbin zaɓaɓɓun shugabannin Ƙananan hukumomi, mataimakan shugabannin, Kwamishinoni da shugabannin hukumar a ɗakin taro na Hauwa Isah Wali da ke gidan gwamnati, Minna babban birnin jihar.
Sojoji sun kashe ’yan ta’adda 2, sun ƙwato makamai a Borno Osimhen ya lashe kyautar gwarzon ɗan wasan bana na TurkiyyaBago ya bayyana cewa, saboda zaɓen 2027 ne ya hana shi ya ɗauki tsauraran matakai kan wasu jami’an idan ba don zaben da ke tafe ba, yana mai cewa tsarin wa’adi ɗaya ne zai bai wa shugabanni damar yin taka-tsantsan ba tare da matsin lamba na siyasa ba.
“Ni mai goyon bayan wa’adi ɗaya ne ga gwamnoni domin abin takaicin mun dawo kan batutuwan siyasa, komai na Najeriya cike yake da siyasa, abin takaici ne!
“Akwai abubuwan da zan iya yi a yau, amma zan yi magana ne a kai bayan zaɓe. Dole ne in sallami wasu ma’aikata da ba su da amfani, amma ba zan iya ba saboda zaɓe, sun faɗi jarabawarsu da yawa, ba za a iya yi musu ƙarin girma ba, amma nauyi ne a kan tsarin. Idan da zango ɗaya ne ake yi, da na fi yanke hukunci fiye da wanda nake a yau,” in ji shi.