Leadership News Hausa:
2025-12-10@17:17:52 GMT

Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo

Published: 29th, April 2025 GMT

Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo

Michael, wanda ke zaune a Phase 4, ya yi ƙoƙarin ceton abokinsa, amma shi ma makiyayin ya sare shi da adda.

An garzaya da Michael zuwa Asibitin Mararaba domin ceto rayuwarsa, amma likita ya tabbatar da mutuwarsa bayan isar su.

‘Yansanda sun bayyana cewa an adana gawar Michael a asibitin domin gudanar da bincike.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, ya umurci a tura jami’an tsaro domin kare rayuka da dukiya a yankin, tare da umartar Mataimakin Kwamishinan Sashen Binciken Laifuka da ya fara bincike da kuma kamo wanda ake zargi domin gurfanar da shi a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Makiyayi Nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato

Sojoji sun kashe wasu da ake zargin ’yan bindiga ne da suke ƙoƙarin yi garkuwa da ayarin ’yan kasuwa a kan hanyar Tarah–Karawa da ke Sabon Birni a Jihar Sakkwato.

’Yan kasuwar na kan hanyarsu daga ƙauyen Tarah zuwa kasuwar mako a Sabon Birni ne lokacin da ’yan bindiga suka kai musu hari a Kwanan Akimbo da misalin karfe 8 na safe.

Wani mazaunin yankin ya shaida wa wakilinmu cewa sojojin da ke sansani a Kurawa sun ji karar harbe-harbe, suka garzaya wajen, inda aka yi musayar wuta na kusan sa’a guda.

“Sojoji sun yi musu luguden wuta, daga baya ’yan bindigar suka ja da baya suka tsere zuwa maɓoyarsu a can bayan rafin.

Rashin Tsaro: Gwamnatin Tarayya ta gaza — Kwankwaso An kama tsohon fursuna da bindiga ƙirar AK-47

“Mun ƙirga gawarwakin ’yan bindiga tara a yankinmu, sannan aka gano wasu hudu a dajin kusa da rafin. Sojoji kuma sun kwashe makamai da babura da dama suka kai Kurawa,” in ji wani mazaunin.

Ya ƙara da cewa mutane biyu ne suka samu raunuka, suna karbar magani a asibiti, amma dukkan ’yan kasuwar sun tsira ba tare da wani rauni ba. “Babu asarar rayuka a ɓangaren sojoji,” in ji shi.

Al’ummomin Kurawa da maƙwabtansu sun yi murna da nasarar da sojojin suka samu.

Ɗan majalisar dokokin jihar da ke wakiltar Sabon Birni, Hon. Aminu Boza, ya ce an gano gawarwakin aƙalla tara daga cikin ’yan bindigar, kuma bincike na ci gaba.

“An kwato makamai da babura da dama daga hannunsu. Ina fatan sojojinmu za su ci gaba da irin wannan aiki,” in ji shi.

Wannan lamari ya faru ne kwana guda bayan da ’yan bindiga suka kai hari ƙauyukan Gatawa da Shalla da ke Sabon Birni da Isa, inda suka kashe mutane bakwai tare da yin garkuwa da mata da dama.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Rikicin Iyakar Thailand da Cambodia Ya Tilasta wa Dubban Mutane Barin Muhallansu
  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • Ministan Makamashi: Iran Tana Da Sanayya Ta Ilimi Na Samar Da Hadari Domin Yin Ruwan Sama
  • Majalisar Dattawa ta amince Tinubu ya tura sojojin Najeriya zuwa Jamhuriyar Benin
  • Trump Ya Yi Gefe Da Kasashen Turai Dangane Da Tattaunawa Kan Rikicin Ukraine
  • Najeriya: Jirgin Sojojin Kasar Yana Kan Hanyarsa Ta Zuwa Portugal, Amma Ta Sauka A Burkina Faso
  • Nigeria Ta Aike Da Jiragen Yaki Zuwa Kasar Benin Domin Dakile Yunkurin Juyin Mulki
  • Kasashen Iran Da Azarbaijan Sun Amince Da Ci Gaba Da Tuntubar Juna Domin Warware Duk Wani Rikici
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga 13, sun ceto ’yan kasuwa a Sakkwato
  • An kama tsohon fursuna ya je fashi da bindiga AK-47