Leadership News Hausa:
2025-05-18@15:50:43 GMT

Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo

Published: 29th, April 2025 GMT

Makiyayi Ya Kashe Abokai 2 A Nasarawa Kan Rikicin Kiwo

Michael, wanda ke zaune a Phase 4, ya yi ƙoƙarin ceton abokinsa, amma shi ma makiyayin ya sare shi da adda.

An garzaya da Michael zuwa Asibitin Mararaba domin ceto rayuwarsa, amma likita ya tabbatar da mutuwarsa bayan isar su.

‘Yansanda sun bayyana cewa an adana gawar Michael a asibitin domin gudanar da bincike.

Kwamishinan ‘yansandan jihar, ya umurci a tura jami’an tsaro domin kare rayuka da dukiya a yankin, tare da umartar Mataimakin Kwamishinan Sashen Binciken Laifuka da ya fara bincike da kuma kamo wanda ake zargi domin gurfanar da shi a kotu.

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: Makiyayi Nasarawa

এছাড়াও পড়ুন:

An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja

Wani mutum da ake nema ruwa a jallo bisa zargin garkuwa da mutane an kama shi a sansanin alhazai da ke Abuja.

Wata majiya daga jami’an tsaro ta tabbatar wa wakilinmu cewa an kama wanda ake zargin, mai suna Yahaya Zango, yayin da ake tantance takardun maniyyatan da ke shirin tafiya Ƙasar Saudiyya domin aikin Hajjin bana.

’Yan sanda sun ceto tsohuwa mai shekara 80 a hannun ’yan bindiga a Jigawa.Shin PDP za ta iya ɗinke ɓarakarta nan da zaɓen 2027?

Rahotanni sun bayyana cewar Zango yana zaune ne a unguwar Paikon-Kore da ke cikin Ƙaramar Hukumar Gwagwalada a Babban Birnin Tarayya, Abuja.

Jami’an tsaro sun bayyana shi a matsayin wanda ake nema ruwa a jallo saboda zarginsa da hannu wajen garkuwa da mutane.

Majiyar ta ce mutumin ya zo da fasfonsa tare da sauran maniyyatan Abuja, amma jami’an hukumar DSS suka gane shi kuma suka cafke shi nan take suka tafi da shi.

Wani babban jami’i daga hukumar jin daɗin alhazai, ya tabbatar da kama shi, amma ya buƙaci a sakaya sunansa.

Rahotanni sun nuna cewa an daɗe ana nemansa kafin daga bisani aka yi nasarar cafke shi.

Da aka tuntuɓi kakakin rundunar ’yan sandan Abuja, SP Josephine Adeh, ta ce: “Ka ce DSS ce ta kama shi, amma ni kakakin rundunar ’yan sandan Abuja ce.”

DSS dai ba ta fitar da wata sanarwa kan lamarin ba har zuwa lokacin haɗa wannan rahoto.

Kasancewar Najeriya na fama da matsalolin tsaro, hukumomi na ci gaba da ƙoƙarin magance su, duk da cewar har yanzu ana fama da barazanar hare-haren ’yan ta’adda.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • An kama ƙasurgumin ɗan bindiga yayin tantance alhazai a Abuja
  • ISWAP ta kashe manoma sama da 50 a Borno
  • Jami’ar FUDMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina
  • Jami’ar FUDAMA Ta Ƙara Fadawa Cikin Rikicin Shuagabanci A Katsina
  • Mutum 5 sun jikkata yayin da gidan mai ya ƙone ƙurmus a Ribas
  • Sojoji sun kashe ’yan bindiga da ƙwato shanun sata 1000 a Taraba 
  • Mutum ɗaya ya rasu a rikicin manoma da makiyaya a Yobe
  • Shugaban Kasar Iran Ya Jaddada Imanin Iran Da Tattaunawan Zaman Lafiya Amma Ba Za Ta Amince Da Barazana Ba
  • Mutum 10 sun rasu kan rikicin gona da dabbobi a Filato
  • Mutum 10 sun rasu sakamakon rikicin gona da dabbobi a Filato