Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya kaddamar da ayarin likitoci su tara domin kula da lafiyar maniyata aikin hajjin na wannan shekaran.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan bayan ganawar farko da ayarin da kuma shugabannin hukumar.

Ayarin likitocin ƙarƙashin jagorancin Dr.

Bello Jamoh, za su gudanar da cikakken binciken lafiyar maniyata kafin tafiyar su zuwa kasa mai tsarki da zai gudana a sansanin alhazai da ke Mando, Kaduna.

Sannan kuma za su bayar da taimakon gaggawa a kasar Saudiyya tare da haɗin gwiwar Ayarin likitocin daga Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON).

Shugaban hukumar ya ce mambobin ayarin za su kasance cikin tsari na duba lafiyar mahajjata a tsawon lokacin aikin hajjin.

“Lafiya maniyata aikin hajjin tana da matuƙar muhimmanci, mun zaɓi ayarin ne bisa ƙwarewarsu, kuma muna da tabbacin za su bayar da ingantaccen kulawa ta lafiya a lokacin aikin hajjin,” In ji shi.

Shugaban ya ƙara da cewa za a gudanar da cikakken gwajin lafiya ga dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajj, musamman don gano mata masu juna biyu.

Babu sassauci ko kaɗan wajen barin mata masu juna biyu su tafi Hajj.” in ji Malam Salihu, yana mai jaddada cewa gudunmuwar da ayarin likitocin za su bada wajen tabbatar da wannan doka, na da muhimmanci don bin ƙa’idodin aikin Hajjin.

Ya ja hankalin ayarin likitocin su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa da sadaukarwa, domin tabbatar da cewa mahajjata sun samu aikin hajji mai sauƙi cikin koshin lafiya.

 

Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: ayarin likitocin

এছাড়াও পড়ুন:

Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15

Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na Naira tiriliyan 12.8 daga watan Agustan 2024 zuwa Oktoba 2025, bisa ga bayanan da Hukumar Kula da Rarraba Man Fetur ta Najeriya (NMDPRA) ta fitar.

Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da kasar ke ƙoƙarin ƙara samar da man fetur a cikin gida, duk kuma da aikin da matatar Dangote ke yi.

An kashe matashi yayin rikici a wajen raɗin suna a Bauchi Amurka za ta hana ’yan Najeriyar da ake zargi da yi wa Kiristoci kisan kiyashi biza

Bisa amfani da matsakaicin farashin lita ɗaya na ₦829.77, an ƙididdige jimillar lita 15,435,000,000 da aka shigo da su a wannan lokaci.

Bincike ya nuna cewa mafi yawan shigo da man fetur ya kasance ne a watan Satumban 2024 lokacin da ba a samar da man ba a cikin gida, inda aka shigo da lita biliyan 1.52, sai Agusta 2024 da lita biliyan 1.38, sannan Disamba 2024 da lita biliyan 1.31.

A Oktoba 2025, an shigo da lita biliyan 1.17, sai Nuwamba da lita biliyan 1.12. Amma a Janairu 2025, adadin ya ragu sosai zuwa lita miliyan 765.7, kafin ya ɗan ƙaru zuwa lita miliyan 770 a Fabrairu, sannan miliyan 889.7 a Maris.

A Afrilu, an samu lita miliyan 861, sai kuma Mayu da ya haura zuwa 1.19 biliyan, kafin ya ragu zuwa 978 miliyan a Yuni, sannan ya ƙaru zuwa 1.11 biliyan a Yuli, kafin ya sauka zuwa 818.4 miliyan a Agusta, 663 miliyan a Satumba, da 855.6 miliyan a Oktoba.

Samarwa da mai a cikin gida

A ɓangaren samarwa a cikin gida, jimillar lita biliyan 7.2 aka samar a wannan lokaci, dukkansu daga matatar man Dangote.

Bayanan sun nuna cewa ba a samu gudunmawar samarwa daga cikin gida ba a watan Agusta 2024, amma a Satumba 2024, Dangote ya samar da lita miliyan 102, wanda ya ƙaru zuwa miliyan 300.7 a Oktoba 2024, sannan miliyan 558 a Nuwamba 2024.

Bayanan sun nuna cewa har yanzu ƙasar na dogaro sosai da shigo da man fetur duk da ƙoƙarin kawo ƙarshen shigo da shi domin tallafa wa samarwa a cikin gida.

Dangote ya sha bayyana cewa matatar man shi karfin tace ganga 650,000 a kullum na iya wadatar da Najeriya.

Sai dai masana a fannin sun ce haramta shigo da man fetur zai iya haifar da babakere a fannin, wanda suka ce bai dace da kasuwar man fetur ba a kasar.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • DSS ta kama likitan da ke duba ’yan bindiga a dazukan Kwara
  • Najeriya ta shigo da tataccen man fetur na tiriliyan 12.8 cikin watanni 15
  • Gwamnatin Jigawa Za Ta Samar da Wutar Lantarki a Yankunan Kananan Hukumomin Jihar
  • Mutum 6 sun rasu, 13 sun jikkata a hatsarin mota a Kogi
  • Ƙudirin dokar hukuncin kisa ga masu satar mutane ya tsallake karatu na biyu
  • MDD Ta Amince Da Kudurori Biyu Masu Yin Tir Da HKI
  • Rikicin Kungiyoyin Asiri Ya Yi Sanadiyyar Mutuwar Wani Matashi A Jihar Kwara
  • CBN ya kara yawan kudin da mutum zai iya cirewa a mako zuwa N500,000
  • An tsare tsohuwar shugabar kula da manufofin ketare ta EU Mogherini bisa badakalar cin hanci
  • Gwamnatin Nasarawa Za Ta Gurfanar da Iyayen Yaran da Ba Sa Zuwa Makaranta