Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya kaddamar da ayarin likitoci su tara domin kula da lafiyar maniyata aikin hajjin na wannan shekaran.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan bayan ganawar farko da ayarin da kuma shugabannin hukumar.

Ayarin likitocin ƙarƙashin jagorancin Dr.

Bello Jamoh, za su gudanar da cikakken binciken lafiyar maniyata kafin tafiyar su zuwa kasa mai tsarki da zai gudana a sansanin alhazai da ke Mando, Kaduna.

Sannan kuma za su bayar da taimakon gaggawa a kasar Saudiyya tare da haɗin gwiwar Ayarin likitocin daga Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON).

Shugaban hukumar ya ce mambobin ayarin za su kasance cikin tsari na duba lafiyar mahajjata a tsawon lokacin aikin hajjin.

“Lafiya maniyata aikin hajjin tana da matuƙar muhimmanci, mun zaɓi ayarin ne bisa ƙwarewarsu, kuma muna da tabbacin za su bayar da ingantaccen kulawa ta lafiya a lokacin aikin hajjin,” In ji shi.

Shugaban ya ƙara da cewa za a gudanar da cikakken gwajin lafiya ga dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajj, musamman don gano mata masu juna biyu.

Babu sassauci ko kaɗan wajen barin mata masu juna biyu su tafi Hajj.” in ji Malam Salihu, yana mai jaddada cewa gudunmuwar da ayarin likitocin za su bada wajen tabbatar da wannan doka, na da muhimmanci don bin ƙa’idodin aikin Hajjin.

Ya ja hankalin ayarin likitocin su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa da sadaukarwa, domin tabbatar da cewa mahajjata sun samu aikin hajji mai sauƙi cikin koshin lafiya.

 

Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: ayarin likitocin

এছাড়াও পড়ুন:

Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno – INEC

Hukumar Zaɓe Mai zaman kanta ta Ƙasa a Jihar Borno ta bayyana cewa, babu tabbas na gudanar da aikin rijistar masu kaɗa ƙuri’a na shekarar 2025/2026 a wasu Ƙananan hukumomin Jihar huɗu don matsalar tsaro.

Ƙananan hukumonin sun haɗa da: Ƙaramar Hukumar Abadam da Guzamala da Marte da Kala-Balge

Ambaliya: Magidanta da dama sun rasa muhallinsu a Yobe An sake ceto matafiya 10 da aka sace a Kogi

Bayanin hakan dai ya fito ne daga bakin Kwamishinan zaɓe na Jihar Borno, Abubakar Ahmad Ma’aji a jawabinsa ga manema labarai a Maiduguri, a wani ɓangare na shirye-shiryen fara gudanar da aikin rijistar masu kaɗa kuri’a a ranar Litinin da ke tafe.

Kamar yadda Kwamishinan Hukumar zaɓen ke bayyanawa, INEC ta mayar da rijistar masu kaɗa ƙuri’a na ci gaba da gudana a Ƙaramar hukumar Abadam zuwa kan hanyar Baga daura da ofishin Yerwa Peace.

Haka nan shi kuma aikin rijistar masu kaɗa ƙuri’a na Ƙaramar hukumar Guzamala an mayar da shi a sashen kashe gobara na rukunin gidaje 1,000.

Sauran Ƙananan hukumomin kamar Ƙaramar hukumar Kala-Balge an mayar da aikin ya zuwa  makarantar firamare ta Goni Kachalari da ke birnin na Maiduguri.

Shi kuma aikin rijistar masu kaɗa ƙuri’a na Ƙaramar hukumar Marte an mayar da shi ya zuwa Kachamai, waɗanda dukkansu suna cikin birnin Maiduguri ne.

Don haka Kwamishinan ya yi kira ga mutanen waɗannan ƙananan hukumomin da su yi haƙuri da wannan canji da aka samu an yi ne da kyakkyawar manufar da duk wanda abin ya shafa zai samu rijistar katinsa na kaɗa ƙuri’a cikin kwanciyar hankali.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Gwamna Sani Ya Ba Da Umarnin Gudanar Da Bincike Kan Kashe Wani Matashi A Barnawa
  • Ba mu da tabbas na ci gaba da rijistar kaɗa ƙuri’a a Borno – INEC
  • Matsalar tsaro na iya hana mu ci gaba da rijistar masu zabe a Borno – INEC
  • NPA Ta Fito Da Sabuwar Doka Kan Kayan Da Ake Ajiyewa A Tashoshinta
  • Zaɓen Cike Gurbi: Gwamnatin Kaduna Ta Yi Watsi Da Kalaman El-rufa’i Akan Zargin Maguɗin Zaɓe
  • An Bukaci Ficewar Marasa Lafiya da Likitoci daga Wani Babban Asbiti A birnin London
  • Jama’a sun koka kan rashin kammala aikin titi a Kafanchan
  • Gwamna Namadi Ya Yaba Wa Kungiyar NBA Bisa Inganta Manufofi Da Ka’idojin Aikin Lauya
  • ETFund Ta Koka Kan Gibin Da Ake Samu A Sashin Lafiyar Najeriya
  • Lafiyar Tinubu kalau – Soludo