Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya kaddamar da ayarin likitoci su tara domin kula da lafiyar maniyata aikin hajjin na wannan shekaran.

Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan bayan ganawar farko da ayarin da kuma shugabannin hukumar.

Ayarin likitocin ƙarƙashin jagorancin Dr.

Bello Jamoh, za su gudanar da cikakken binciken lafiyar maniyata kafin tafiyar su zuwa kasa mai tsarki da zai gudana a sansanin alhazai da ke Mando, Kaduna.

Sannan kuma za su bayar da taimakon gaggawa a kasar Saudiyya tare da haɗin gwiwar Ayarin likitocin daga Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON).

Shugaban hukumar ya ce mambobin ayarin za su kasance cikin tsari na duba lafiyar mahajjata a tsawon lokacin aikin hajjin.

“Lafiya maniyata aikin hajjin tana da matuƙar muhimmanci, mun zaɓi ayarin ne bisa ƙwarewarsu, kuma muna da tabbacin za su bayar da ingantaccen kulawa ta lafiya a lokacin aikin hajjin,” In ji shi.

Shugaban ya ƙara da cewa za a gudanar da cikakken gwajin lafiya ga dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajj, musamman don gano mata masu juna biyu.

Babu sassauci ko kaɗan wajen barin mata masu juna biyu su tafi Hajj.” in ji Malam Salihu, yana mai jaddada cewa gudunmuwar da ayarin likitocin za su bada wajen tabbatar da wannan doka, na da muhimmanci don bin ƙa’idodin aikin Hajjin.

Ya ja hankalin ayarin likitocin su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa da sadaukarwa, domin tabbatar da cewa mahajjata sun samu aikin hajji mai sauƙi cikin koshin lafiya.

 

Adamu Yusuf

উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa

কীওয়ার্ড: ayarin likitocin

এছাড়াও পড়ুন:

Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa

Wani dalibin shekarar ƙarshe a Jami’ar Ambrose Alli da ke jihar Edo, ya mutu a wani hatsarin mota bayan shi da wasu dalibai sun yi jerin gwanon motoci domin murnar kammala jarabawar ƙarshe.

Aminiya ta samu labari a ranar Talata daga wani mai amfani da Facebook mai suna Inside Edo, cewa hatsarin ya faru ne a ranar Litinin jim kaɗan bayan daliban sun gama jarabawar ƙarshe. Sai dai ba a bayyana sunan dalibin ba.

DAGA LARABA: Ko Ziyarar Tawagar Amurka Za Ta Kawo Karshen Matsalar Tsaro A Najeriya? Iya sojojin da ke tsaron Seyi Tinubu sun isa su samar da tsaro a Benin – Soyinka

Majiyar ta ce motar ta yi ƙoƙarin wuce wata mota kafin ta kwace ta kuma daki wata babbar mota.

A cewar majiyar: “Wani mummunan hatsari ya faru a Ujoelen, kusa da makarantar firamare, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar wani dalibi da ya kammala karatu a jami’ar Ambrose Alli, Ekpoma.

“A cewar masu gani da ido, hatsarin ya faru ne yayin da aka yi yunƙurin wucewa da ɗaya daga cikin motocin da abin ya shafa.

“Wannan haɗarin ya jawo rasa iko, wanda ya haifar da mutuwar. Mazauna yankin da ke kusa sun ruga wurin, amma ba a iya ceto wanda ya jikkata ba.”

Haka kuma, Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa daliban sun kasance suna tukin mota cikin ganganci kafin su yi taho-mu-gama da wata babbar mota da ta tsaya a hanya.

An ce wanda ya rasu yana cikin jerin gwanon motocin da daliban da suka kammala karatu suka yi.

NAN ta ruwaito: “An ce yana cikin jerin gwanon sabbin daliban da suka shiga kan hanya a ranar Litinin jim kaɗan bayan bikin kammala makaranta.

“Lamarin ya faru ne lokacin da wanda ya rasu ya yi yunƙurin wuce wata babbar mota mai tafiya, amma ya buge da wata mota da ta tsaya a gefen hanya.”

Ƙoƙarin samun martani daga kwamandan sashe na jihar Edo a Hukumar Kiyaye Hadura ta Ƙasa (FRSC), Cyril Mathew, ya ci tura, domin lambar ba ta shiga har zuwa lokacin hada wannan rahoton.

Sai dai NAN ya rawaito daga baya Mathew ya tabbatar da lamarin, yana mai cewa mutum ɗaya ya mutu yayin da wasu biyar suka jikkata a hatsarin.

Ya ce: “Daliban, bayan sun gama rubuta takardar jarabawa ta ƙarshe, sun shiga hanya cikin jerin gwanon motoci.

“A cikin wannan yanayi, ɗaya daga cikinsu ya yi yunƙurin wuce wata mota, ya kuma buge da wata babbar mota da ta tsaya a gefen hanya,” kamar yadda NAN ya rawaito daga Mathew.

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Dalibin jami’a ya rasu a hatsarin motar murnar kammala jarabawa
  • Uwargidan Gwamnan Jihar Zamfara Ta Taya Oluremi Tinubu Murnar Nadin Sarauta a Ile-Ife
  • Saurayi ya kashe budurwarsa sannan ya soya qwaqwalwarta 
  • Gwamnan Jihar Ribas ya sauya sheka zuwa APC
  • Yara masara zuwa makaranta barazana ne ga kasa — Shettima
  • An Fito Da Gawawwakin Shahidai 98 Da Aka Binne Cikin Gaggawa A Asibitin “Ash-Shifa”
  • Gwamnonin Arewa Za Su Zuba Biliyoyin Naira Don Yaki da Matsalar Tsaro
  • Zaben 2027: NNPP Ta Sha Alwashin Maye Gurbin Tinubu da Radda
  • ASUU-SSU Ta Zargi VC Da KaryDokokin Jami’ar Jihar Sakkwato
  • Juyin mulki: An kama sojojin da suka yi yunƙurin kwace mulki a Benin