Hajj 2025: Kaduna Ta Gaddamar Da Ayarin Likitoci Da Za Su Kula Da Alhazan Jihar
Published: 30th, April 2025 GMT
Gwamna Uba Sani na Jihar Kaduna ya kaddamar da ayarin likitoci su tara domin kula da lafiyar maniyata aikin hajjin na wannan shekaran.
Shugaban Hukumar Jin Daɗin Alhazan Jihar Kaduna, Malam Salihu S. Abubakar, ne ya bayyana hakan bayan ganawar farko da ayarin da kuma shugabannin hukumar.
Ayarin likitocin ƙarƙashin jagorancin Dr.
Sannan kuma za su bayar da taimakon gaggawa a kasar Saudiyya tare da haɗin gwiwar Ayarin likitocin daga Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON).
Shugaban hukumar ya ce mambobin ayarin za su kasance cikin tsari na duba lafiyar mahajjata a tsawon lokacin aikin hajjin.
“Lafiya maniyata aikin hajjin tana da matuƙar muhimmanci, mun zaɓi ayarin ne bisa ƙwarewarsu, kuma muna da tabbacin za su bayar da ingantaccen kulawa ta lafiya a lokacin aikin hajjin,” In ji shi.
Shugaban ya ƙara da cewa za a gudanar da cikakken gwajin lafiya ga dukkan masu niyyar zuwa aikin Hajj, musamman don gano mata masu juna biyu.
“Babu sassauci ko kaɗan wajen barin mata masu juna biyu su tafi Hajj.” in ji Malam Salihu, yana mai jaddada cewa gudunmuwar da ayarin likitocin za su bada wajen tabbatar da wannan doka, na da muhimmanci don bin ƙa’idodin aikin Hajjin.
Ya ja hankalin ayarin likitocin su gudanar da aikinsu cikin ƙwarewa da sadaukarwa, domin tabbatar da cewa mahajjata sun samu aikin hajji mai sauƙi cikin koshin lafiya.
Adamu Yusuf
উৎস: Radio Nigeria Kaduna Hausa
কীওয়ার্ড: ayarin likitocin
এছাড়াও পড়ুন:
Kotu ta ɗaure matashi kan wulaƙanta Naira a TikTok
Hukumar da ke yaƙi da cin hanci da rashawa EFCC reshen shiyyar Kaduna ta gurfanar da wani Muhammad Kabir a gaban kotu tare da yanke masa hukunci, wanda ya kasance mai wallafa bidiyo a shafukan TikTok da Instagram.
An gurfanar da Muhammad Kabir a gaban mai shari’a Rilwan Aikawa na babbar kotun tarayya da ke zamanta a Kaduna bisa laifin wulaƙantawa da lalata takardun Naira.
An kama wata mata kan safarar makamai zuwa Katsina Sabon Hari: An kashe makiyayi da shanu sama da 100 a FilatoAn kama Kabir ne a ranar Talata, 29 ga Afrilu, 2025 a Tudun Wada, Jihar Kaduna saboda yin wani bidiyo a shafinsa na TikTok da Instagram @youngcee0066 yayin da yake watsa takardar Naira a ƙasa, yana tattake su yana magana da harshen Hausa da kuma tursasa EFCC ta zo ta kama shi a inda yake.
Daga nan ne aka kama shi da laifin karya dokar babban bankin Najeriya (CBN) da ta haramta cin zarafi da wulaƙanta Naira.
Ɗaya daga cikin tuhume-tuhumen da ake yi masa, ya ce: “Kai Muhammad Kabir Sa’ad (da aka fi sani da youngcee0066) a wani lokaci a shekarar 2025 a Kaduna da ke ƙarƙashin ikon wannan kotun mai girma, ka wulaƙanta Naira wanda ya saɓa ƙa’ida, ta hanyar tattaka takardun kuɗin Naira yayin da kake yin hoton bidiyo na sada zumunta da yaɗawa a intanet, sannan yin hakan aikata wani laifi ne na Babban Bankin Nijeriya na 2007 mai hukunci a ƙarƙashin Sashe na 21 (1) na wannan dokar.”
Wanda ake tuhumar ya amsa laifin da ake tuhumarsa da aikatawa lokacin da aka karanta masa, wanda hakan ya sa lauyan mai shigar da ƙara, M.U Gadaka ya roƙi kotu da ta yanke masa hukuncin da ya dace.
Sai dai Mai shari’a Aikawa ya yanke wa Muhammed hukuncin ɗaurin watanni shida (6) ko kuma ya biya tarar Naira dubu ɗari uku (₦300,000.00) ga Gwamnatin Tarayyar Najeriya.