A watan Janairu kawai, marigayi shugaban ‘yan fashin daji, Isuhu Yellow, ya sanya harajin naira miliyan 172.7 a kauyuka 25, ciki har da bukatar amfanin gona.

 

A misali, an kakaba wa kauyen Gijinzama harajin naira miliyan 8.5, Dakolo naira miliyan 5 da buhunan wake 20, da Kibari, Kunchin Kalgo naira miliyan 20, Sungawa naira miliyan 15, da Yalwa naira miliyan 2.

7, da dai sauransu.

 

Ba da jimawa ba, wani shugaban ‘yan fashin dajin nan, Dogo Gide, ya bukaci a biya naira miliyan 100 daga wasu al’ummomi 23 da ke karamar hukumar Tsafe, lamarin da ya sa jama’a suka kauracewa gidajensu.

 

Al’ummomin da abin ya shafa sun hada da Kunchin-Kalgo da aka nemi naira miliyan 20 daga wajensu, Sungawa naira miliyan 15, Rakyabu naira miliyan 15, da Kwaren Mai-Saje naira miliyan 10.

 

A ranar Lahadi, 20 ga Afrilu, ‘yan bindiga sun sake neman naira miliyan 60 daga mazauna kauyen Dankurmi a karamar hukumar Maru.

 

Wani mazaunin kauyen Kwalfada a karamar hukumar Tsafe wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya tabbatar da cewa ‘yan garkuwa da mutanen sun kakaba wa rayuka da dama haraji a yankin.

 

Ya ce, miliyoyin naira ne masu garkuwan suka nema a hannun jama’a ko kuma su kawo musu farmaki.

 

Wani mazaunin kauyen Dan Jibga, Mai suna Muhammad Dogo, ya ce ‘yan fashin daji sun sanya harajin naira miliyan 10 ga al’ummar Gama Lafiya bayan kashe wasu mutum biyu a ranar Lahadi da Litinin.

 

Dogo ya ci gaba da cewa, sauran kauyukan da harajin ya shafa sun hada da Unguwar Tofa naira miliyan 26.6, Makera naira miliyan 15, Sungawa naira miliyan 20, Rakyabu naira miliyan 7, Yalwa naira miliyan 8, Kwarin Mai Saje naira miliyan 11, Langa-Langa, inda harajin ya kai tsakanin naira miliyan 20 zuwa naira miliyan 30.

 

Ya kara da cewa ‘yan fashin dajin sun kwace kauyukan Gidan Dawa, Rijiyar Tsakar Dawa, Dan Jibga, da Bilbis.

 

Wani mazaunin garin Mara da ke karamar hukumar Maru, Malam Ibrahim Maru, ya koka da yadda matsalar ‘yan fashin dajin ke ta kara ta’azzara a yankin Maru a ‘yan kwanakin nan.

 

Ya ce, “Hanyar Talata Mafara zuwa garin Maru ta zama tarkon mutuwa ga matafiya da direbobin wanda sun daina amfani da hanyar bayan karfe 4 na yamma.

 

“Da zarar karfe 4 na yamma ya yi zai yi wuya a samu direban da ke son daukar fasinjoji daga Maru zuwa Talata Mafara, kwanan nan na yi tattaki daga Talata Mafara zuwa Maru domin ziyarar jaje, amma da isa Maru, sai aka ba mu shawarar mu koma.

 

“Wannan hanyar ba ta da tsaro, ‘yan bindiga sun ci gaba da ayyukansu, suna gudanar da ayyukansu ba dare ba rana, sun yi garkuwa da mutane da dama, ciki har da mata da yara, a kauyuka daban-daban, kuma suna sanya haraji a kan al’ummomi da dama.”

Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

উৎস: Leadership News Hausa

কীওয়ার্ড: naira miliyan 15 naira miliyan 20 karamar hukumar

এছাড়াও পড়ুন:

Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho

Hukumar Fensho ta Jihar Jigawa da Kananan Hukumomin jihar ta shirya fara aikin tantance ‘yan fansho da ke cikin tsarin.

Shugaban Ma’aikatan Gwamnatin Jihar, Alhaji Muhammad K. Dagaceri ne ya bayyana haka yayin wani taron masu ruwa da tsaki da aka gudanar a Gidan Fansho, inda shugabannin kungiyar ‘Yan Fansho ta Najeriya reshen Jigawa suka halarta.

A cewarsa, an shirya fara aikin tantancewar ne daga ranar Litinin, 5 ga Mayu, 2025.

Alhaji Dagaceri ya bayyana cewa, an shirya hakan ne da nufin sabunta tsarin biyan fansho tare da tabbatar da ingancin bayanai.

Ya ce, aikin tantancewar zai gyara wasu ‘yan kura-kurai da suka kunno kai a cikin shekaru uku da suka gabata, da kuma tabbatar da ingantattun bayanai a jadawalin biyan fansho.

Ya kara da cewa, wannan yunkuri ya yi daidai da kudirin jihar gwamnati na tabbatar da gaskiya da rikon amana a harkokin mulki, tare da bai wa ‘yan fansho dama su gyara duk wani bayanin da bai cika ba a takardunsu.

Shi ma da ya ke jawabi, Akanta Janar na Jihar, Alhaji Abdullahi S.G. Shehu, ya jaddada cewa aikin tantancewar zai bai wa ‘yan fansho damar sabunta bayanansu da suka bace ko suka canza a takardunsu.

Saboda haka, ya bukaci dukkan ‘yan fansho daga ma’aikatun gwamnati, sassan hukumomi, kananan hukumomi da kuma hukumomin ilimi na kananan hukumomi da su halarci tantancewar a ranar da aka tsara kamar yadda yake cikin jadawalin aikin.

A jawabinsa, Shugaban kungiyar kananan hukumomi ALGON ta Jihar Jigawa, Farfesa Salim Abdurrahman, ya tabbatar da cikakken goyon baya daga shugabannin kananan hukumomi 27 domin cimma burin aikin.

Shugaban na ALGON wanda shugaban karamar hukumar Malam Madori,  Alhaji Salisu Sani ya wakilta,  ya bukaci ‘yan fanshon da su ba da cikakken haɗin kai don samun nasarar shirin.

Shi ma Shugaban hukumar, Dr. Bilyaminu Shitu Aminu, ya bukaci ‘yan fansho daga sassa daban-daban da su ba da hadin kai domin cimma burin da aka sanya, tare da jaddada cewa su ziyarci sakatariyar kananan hukumominsu domin a tantance su.

Shugaban Kungiyar ‘Yan Fansho ta Najeriya reshen Jihar Jigawa, Alhaji Umar Sani Babura, ya yi alkawarin cewa kungiyar za ta bada cikakken goyon baya domin nasarar wannan shiri.

Dukkan ‘yan fansho daga Ma’aikatun Gwamnati, Kananan Hukumomi, da Hukumomin Ilimi na Kananan Hukumomi da ke cikin tsarin  fanshon, ya zama wajibi su halarci wannan tantancewa a ranakun da aka tsara a jadawalin aikin.

 

Usman Muhammad Zaria

 

সম্পর্কিত নিবন্ধ

  • Kwastam Ta Kama Jirage Marasa Matuka Da Sauran Kayayyaki Da Darajarsu Ta Haura Naira Biliyan 921 A Legas
  • Binciken Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN: Cin Zali Ta Hanyar Kakaba Haraji Ya Illata Kimar Amurka
  • Tsoffin ma’aikatan NECO na neman a biya su bashin haƙƙoƙinsu
  • Sojoji Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga , Sun Ceto Fasinjoji 6 A Taraba
  • Za A Yi Allurar Rigakafi Ga Dabbobi Sama Da Miliyan Daya A Babura
  • Shugaba Tinubu Ya Taya Sabon Firaiministan Kanada Mark Carney Murna
  • Gwamnatin Jihar Jigawa Ta Shirya Fara Tantance ‘Yan Fansho
  • Kotu Ta Kori Ƙarar Neman Diyyar N1bn A Kan Buhari Da Emefiele Kan Sauya Fasalin Naira
  • Mutanen da talauci ya yi wa katutu zai ƙaru a Nijeriya — Bankin Duniya
  • Cibiyar Yaƙi da Ta’addanci Ta Yaba Wa Gwamna Lawal Kan Matakan Yaƙi Da ‘Yan Bindiga A Zamfara