‘Yan Bindiga Na Kakaba Harajin Miliyoyin Naira Ga Mutanen Zamfara
Published: 26th, April 2025 GMT
A watan Janairu kawai, marigayi shugaban ‘yan fashin daji, Isuhu Yellow, ya sanya harajin naira miliyan 172.7 a kauyuka 25, ciki har da bukatar amfanin gona.
A misali, an kakaba wa kauyen Gijinzama harajin naira miliyan 8.5, Dakolo naira miliyan 5 da buhunan wake 20, da Kibari, Kunchin Kalgo naira miliyan 20, Sungawa naira miliyan 15, da Yalwa naira miliyan 2.
Ba da jimawa ba, wani shugaban ‘yan fashin dajin nan, Dogo Gide, ya bukaci a biya naira miliyan 100 daga wasu al’ummomi 23 da ke karamar hukumar Tsafe, lamarin da ya sa jama’a suka kauracewa gidajensu.
Al’ummomin da abin ya shafa sun hada da Kunchin-Kalgo da aka nemi naira miliyan 20 daga wajensu, Sungawa naira miliyan 15, Rakyabu naira miliyan 15, da Kwaren Mai-Saje naira miliyan 10.
A ranar Lahadi, 20 ga Afrilu, ‘yan bindiga sun sake neman naira miliyan 60 daga mazauna kauyen Dankurmi a karamar hukumar Maru.
Wani mazaunin kauyen Kwalfada a karamar hukumar Tsafe wanda ya nemi a sakaye sunansa, ya tabbatar da cewa ‘yan garkuwa da mutanen sun kakaba wa rayuka da dama haraji a yankin.
Ya ce, miliyoyin naira ne masu garkuwan suka nema a hannun jama’a ko kuma su kawo musu farmaki.
Wani mazaunin kauyen Dan Jibga, Mai suna Muhammad Dogo, ya ce ‘yan fashin daji sun sanya harajin naira miliyan 10 ga al’ummar Gama Lafiya bayan kashe wasu mutum biyu a ranar Lahadi da Litinin.
Dogo ya ci gaba da cewa, sauran kauyukan da harajin ya shafa sun hada da Unguwar Tofa naira miliyan 26.6, Makera naira miliyan 15, Sungawa naira miliyan 20, Rakyabu naira miliyan 7, Yalwa naira miliyan 8, Kwarin Mai Saje naira miliyan 11, Langa-Langa, inda harajin ya kai tsakanin naira miliyan 20 zuwa naira miliyan 30.
Ya kara da cewa ‘yan fashin dajin sun kwace kauyukan Gidan Dawa, Rijiyar Tsakar Dawa, Dan Jibga, da Bilbis.
Wani mazaunin garin Mara da ke karamar hukumar Maru, Malam Ibrahim Maru, ya koka da yadda matsalar ‘yan fashin dajin ke ta kara ta’azzara a yankin Maru a ‘yan kwanakin nan.
Ya ce, “Hanyar Talata Mafara zuwa garin Maru ta zama tarkon mutuwa ga matafiya da direbobin wanda sun daina amfani da hanyar bayan karfe 4 na yamma.
“Da zarar karfe 4 na yamma ya yi zai yi wuya a samu direban da ke son daukar fasinjoji daga Maru zuwa Talata Mafara, kwanan nan na yi tattaki daga Talata Mafara zuwa Maru domin ziyarar jaje, amma da isa Maru, sai aka ba mu shawarar mu koma.
“Wannan hanyar ba ta da tsaro, ‘yan bindiga sun ci gaba da ayyukansu, suna gudanar da ayyukansu ba dare ba rana, sun yi garkuwa da mutane da dama, ciki har da mata da yara, a kauyuka daban-daban, kuma suna sanya haraji a kan al’ummomi da dama.”
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsAppকীওয়ার্ড: naira miliyan 15 naira miliyan 20 karamar hukumar
এছাড়াও পড়ুন:
Gwamnatin Sakkwato Ta Sayo Manyan Tan-tan 250 Na Sama Da Naira Biliyan 22
An shawarci gwamnatocin jihohin Sakkwato, Kebbi da Zamfara da su kirkiro hanyoyi na wayar da kan al’umma dangane da shirye-shiryen tallafi da ayyukan ci gaba da gwamnatin tarayya ke aiwatarwa domin bunkasa tattalin arziki da tabbatar da tsaro a yankunansu.
Shugaban sashen kimiyyar zamantakewa na Jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke Sakkwato, Farfesa Chika Umar Aliyu, ne ya bayar da wannan shawara yayin gabatar da takarda a wajen taron shekara-shekara na kungiyar Nigerian Institute of Management reshen jihar Sokoto na shekarar 2025, wanda aka hada da gabatar da lambar yabo ga wadanda suka cancanta.
Farfesa Chika ya bayyana cewa, gwamnati tarayya na da shirye-shiryen tallafi da dama da suka hada da na noma, kasuwanci da kuma koyar da sana’o’in hannu domin kara habaka tattalin arzikin ‘yan Najeriya da rage zaman kashe wando, da tayar da hankali musamman matasa a yankin.
Ya jaddada cewa dole ne gwamnatocin jihohi su tallafa wa kokarin gwamnatin tarayya ta hanyar amfani da hukumominsu na jin dadin al’umma domin cimma burin shirye-shiryen.
A jawabinsa wajen taron, kwamishinan noma na jihar Sakkwato, Muhammad Tukur Alkali, ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta sayo manyan Tan-tan na noma guda 250 da kayan aikin gona da darajarsu ta kai naira biliyan ashirin da biyu da miliyan dari daya (₦22.1bn), domin tabbatar da wadatar abinci.
A cewar Tukur Alkali, gwamnatin jihar ta hanyar shirye-shiryen inganta rayuwar al’umma, ta samar da sama da ayyukan yi 2,700 a bangaren noma, abin da ke da tasiri mai girma wajen bunkasa noma mai dorewa da ci gaban ababen more rayuwa a karkara.
Daga Nasir Malali